RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

     A wannan time ɗin Rayyan ya shigo gidan, sanda ya iso saman yaji kamar ana dariya da koke-koken jarirai cikin ɗakin ta, sai ya tsaya yana kasa kunne, abun sai ƙara ƙaruwa yake yi hakan yasa ya taka zuwa bakin ƙofan ya buɗe ya shiga.

      Ɗakin dunɗum babu haske duk da kuwa ba dare bane, domin time ɗin ƙarfe 02:50pm ne, but abun mamaki duhu sosai, duk da kuwa ga windows har biyu haske na shigowa, saurin saka hannu yayi ya kunna fitilan ɗakin tunda akwai wuta, nan ɗakin ya gauraye da haske, ɗakin kuma ya koma yanda yake da hasken shi tarwai

Idanun sa ne suka sauka kan RAUDHA dake yashe a ƙasa ta dunƙule waje ɗaya, gashin ta duk ya barbaje ya rufe mata fuska, tsayawa yayi kawai yana kallon ta da tsantsan mamakin ganin ta a haka, sai da ya jima yana tunani a ransa kafin kuma ya taka zuwa wajen ta yana kiran sunan ta

Sai dai ko motsi bata yi ba

Ahankali ya duƙa gaban ta ya saka hannu ya yaye gashin da ya rufe mata fuska, idanuwan ta a rufe suke, sai numfashi da take sauke wa ahankali alamun barci take yi, kawai tsayawa yayi yana kallon kyakykyawar fuskar ta, zuciyar sa cike da tunanin “anya yarinyan nan ba ta da aljanu? Ko kuma shaye-shayen da take yi ya taɓa mata ƙwaƙwalwa”.

Sai a lokacin idanun sa suka sauka kan hannayen ta da duk bandage ɗin ya cire na wani wajen, duk da ciwon be wani warke ba amma yayi sauƙi kasancewar ya rigada ya bushe sabida maganin da aka saka mata

Shiru yayi na wani lokaci; kafin ya tashi ya ɗauke ta zuwa kan gadon, shimfiɗe ta yayi ya juya ya fice ya shiga ɗakin sa, wanka ya soma yi sannan ya fita zuwa ƙasa ya zauna cin abinci, har ya gama ya dawo ɗakin RAUDHA tana nan a yanda ya aijiye ta, ko juyawa ba ta yi, ba don numfashin da take fitarwa ba ba ya tsammanin tana da rai, zama kawai yayi a ɗakin ya tasa ta gaba yana ta kallo, zuciyar sa cike tab da wani irin nishaɗi, sosai ya shagaltu da kallon halittar da duk duniya babu abinda yafi masa a cikin ransa, tabbas tun a kallon farko da ya fara haɗuwa da ita, zuciyar sa ta hautsine da ƙaunar ta, sai dai kuma be taɓa tunanin zai sake ganin ta ba a rayuwan sa, a ranan da ya haɗu da ita anan gidan, ya kuma tabbatar da ƙanwar Suhaib ne, tabbas ranan ya kasa barci, sabida tsantsan farin ciki da ya cika sa, abun mamaki sai gashi ita ɗin ba yanda ya ɗauke ta ba, domin a tunanin sa ba ma ƙabilan su ɗaya ba, duk da rashin tarbiyyar ta be sa ya ji soyayyar ta ya fita a ransa ba, sai ma ƙara ƙaruwa da yake yi, be taɓa soyyayya ba sai akanta, tunda ya ɗaura idon sa a kanta be sake samun sukunin zuciya ba, be san kuma ya zai yi ya bayyana mata ƙaunar sa a gare ta ba.

Ajiyan zuciya ya sauke jin ana kiran sallah, ya miƙe ya fice.

      Rayyan be dawo gidan ba sai bayan isha’i, amma koda ya sake shigowa ɗakin RAUDHA, abun mamaki tana nan dai a yanda take ɗin sai barcin ta take yi, yanzu kuma sosai ya tsorata da wannan barcin na ta, zuwa yayi gaban gadon ya soma tashin ta, but ko motsi bata yi ba, duk yanda ya so ya tashe ta amma taƙi motsa wa, dole ya fita a ɗakin zuciyar sa na ayyana masa tabbas babu lafiya.

      Be daɗe ba suka dawo da doctor, shi ya tabbatar masa da lafiyan ta ƙalau, barci ne kawai take yi, sannan ya sake wanke mata ciwon ya saka mata magani ya rufe, sallama yayi masa ya tafi, sai shima ya fice ya koma ɗakin sa, a taƙaice dai haka Rayyan ya kwana da tunanin RAUDHA a ransa, ko kaɗan zuciyar sa ta kasa ba shi damar da zai sukuni, daƙyar ya iya samun barci gab da asuba, wanda sai da ya makara sallah ma, ƙarfe 07:30am ya tashi yayi sallan ya sake komawa barci, zuwa ƙarfe 09:00am. Ya gama shiryawa ya fito, be samu damar shiga ɗakin ta ba yabar gidan.

 

          ????????????

       Zuwa biyu ta farka daga barcin ta, ta daɗe kafin ta tashi daga kan gadon, sai faman juya kai take yi tana faman yamutsa fuska, sakamakon ciwo da kan nata ke yi, hannayen ta tabi da kallo fuska babu fara’a, sai kuma ta tashi ta shiga Toilet, haka nan ta lallaɓa yau tayi wanka tafito ta sauya kaya, riga da wando ƙanana ta saka ta ɗau wayan ta ta haye kan gado, duba wa ta soma yi, nan ta ga kiran yayan ta har ten missed calls, sannan na Ramcy, sai Zen da Rash, sai kuma texs message guda biyu na baƙuwar Numban jiya, duk ka babu wanda tabi kiran, haka ma text ɗin babu wanda ta duba ta ajiye wayan, rufe idanunta tayi; tayi shiru abun ta

      Koda Ester ta shigo ta gaishe ta, bata amsa mata ba, ko motsa wa ma bata yi ba, haka Ester tayi aikin ta tafice

A ranan haka RAUDHA ta wuni a saman gadon nan ko sauka ba ta yi, sai idan tana buƙatar zuwa Toilet, shima Kuku har ɗakin ya rinƙa biyo ta da abincin ta, yanda ya ajiye haka yake zuwa ya ɗauka, sai na dare ne ma da ya kawo yaga ta taɓa kaɗan.

     Da Rayyan ya dawo, ɗakin ta ya soma wuce wa don duba lafiyan ta, koda ya shiga da sallama

Tana kan gadon ta kwance, kallo ɗaya tayi masa ta maida idanun ta ta rufe, batare da ta amsa sallaman nasa ba, tunda bata saba yin hakan ba

Iso wa yayi gaban gadon ya tsaya, be yi magana ba illa kallon ta da yake yi, tsawon mintuna biyar kafin ya juya ya fice zuwa ɗakin sa.

       Yana fita ta buɗe idanun ta tana mayar dasu ta lumshe, zuciyarta na sake cinkushe wa sabida ƙamshin turaren sa dake shiga hancin ta, tamkar ta mutu haka take jin ta sabida tsantsan tsanar da take masa, ko kaɗan ba ta ƙaunar sake tozali dashi a rayuwan ta.

     Rayyan da ya shiga ɗakin sa, wanka ya soma yi ya saka riga da wando na shan iska, sannan ya zauna a gefen gadon sa yana tunani a ransa, ya jima ahaka kafin ya ɗauki wayan sa dake gefen sa ya soma typing akan Numban RAUDHA da yayi mata serving da PRETTY:

        *”DA AKWAI WASU LOKUTA DA NAKE ZUBAR DA HAWAYE SABODA KE, NA SAN ZAKI CE SABODA ME? DA AKWAI WANI LOKACI DA YAKE ZUWA NA JI TAMKAR NAYI FIKA-FIKAI NA TASHI SAMA, KIN KUWA SAN DUK SABIDA MENE NE? SABIDA MOTSAWAR SON KI A CIKIN ZUCIYA TA! DA TSINTAR KAINA A CIKIN MATSANANCIN SHAUƘI A DUK KAN LOKACIN DA NAJI MURYAN KI KO NA TUNA DAKE, KAMAR YANDA KO WACCE BISHIYA KANYI RASSA A SAMA, KUMA TAYI SAIWA A ƘASA, HAKA SON KI YA MAMAYE DUK KAN JIKI NA, IDAN NA KALLE KI SAI NAYI FARIN CIKI, IDAN NAJI TATTAUSAN MURYAN KI, SAI NISHAƊI DA WALWALA TARE DA ANNASHUWA GAMI DA FARIN CIKI SU MAMAYE ZUCIYA TA. I love U so much pretty”.*

     Sending yayi, sannan ya koma ya kwanta saman gadon.

            ????????????

     Shigowar message daga wayan ta ne ya sa tasake buɗe lumsassun idanuwan ta da suka soma sauya wa zuwa ja, hannu ta saka ta ɗauki wayan tana kallo, tamkar bata taɓa ganin wayan ba; ko tana neman wani abun aciki haka ta koma, sai kuma daga baya ta buɗe ta soma karanta text ɗin, sai da ta gama sannan ta buɗe sauran biyun da aka yi mata tun jiya, ɗaya na ƙunshe da:

_”Sama cike take da taurari masu hasken da ke haske duniya a cikin ko wanne dare, amma haske mafi haskaka fuska da yaye duhun zuciya, na ganshi ne a cikin idanuwan ki. Ki kula min da kanki. Ina son ki Pretty”._

   Ɗayan kuma na ƙunshe da saƙon:

_”SO gamon jini ne, haƙiƙa son ki ya zamo jinin jiki na! Domin na kan raba dare ina mai roƙon Allah don neman biyan Buƙata, ko kin san ke ce Abu na farko da nake roƙon na samu?”_

Ajiye wayan tayi kawai batare da tayi wani tunani ba, har ta ɗaura hannun ta saman goshin ta ta mayar da idanun ta ta rufe su, sai ta sake jiyo wani saƙon ya shigo, kamar ta share sai kuma taji tana sha’awar gani, ta yiwu me turo mata waɗannan kalaman ne da ba gane su take yi ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button