RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 31 to 40

Ita kuma RAUDHA tunda taji ta a jikin sa ta kasa motsi, illa lumshe ido da tayi tana shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren sa, sai sake lafe masa take yi

Numfashi yaja yana buɗe idanun sa da suka soma sauya kala ya aza a kanta, ahankali ya saka hannu ya janye ta a jikin sa

Firgigit tayi tamkar wacce aka tasa daga barci

Hakan sai ya bashi matuƙar mamaki, yabi ta da ido cike da zallan soyayyar ta, duk idan ya kalle ta sai yaji komi na sa yana kwance wa, tamkar dai ana sauya masa komi da komi dake duniyar, yana jin kamar su kaɗai ne a cikin ta, sannan yana jin wani irin farin ciki da annashuwa na mamaye sa, duk wani ƙunci da ɓacin rai da yake ji akanta, ko kuma fushin da yake so ya ɗauka akanta sai ya ji ya nema ya rasa, sai tarin ƙaunar ta a zuciyar sa.

       Idanun ta ƙyarr a kansa tana hawaye tace, “Please ka tafi dani ina jin tsoro, zasu dawo su cinye Ni ne”.

Waro ido yayi cike da mamakin ta, sai kuma ya ɗaure fuska yace, “in tafi dake wajen aikin nawa kike nufi?”

Ta gyaɗa masa kai still tana hawaye

“Babu inda zan je dake, waɗanda zasu cinye ki ɗin su zo su cinye ki, Ni ba maƙale mata mammanne mata sunana ba, idan yayan naki ya dawo sai kiyi masa wannan sakaracin, amma ban dani, zuwa anjima yace min zai dawo”.

Daga haka ya juya yayi gaba abun sa

Sai ta biyo bayan sa tana hawaye, a waje a bakin ƙofa ta tsaya tana kallon sa har ya isa wajen motan sa, ya shiga yaja yanufi bakin Gate

Ta cikin Glasses ɗin motan yake kallon ta, sosai ta ba shi tausayi ganin yanda take ta hawaye, tabbas ba ƙaramin abu ne ya tsorata ta ba, tunda har ta kasa zama a gidan tana son bin sa, ji yake yi tamkar ya koma ya ɗauko ta su fita tare, but ba shi da inda zai ajiye ta; tunda shi dai ba babban Aljihu ne dashi ba, ahaka yana ji yana gani ya bar gidan.

RAUDHA dai bata tashi a wajen ba, sai kuka take yi, daɗin ta ɗaya tana hangen sojojin dake bakin Gate ɗin, sai ta saka hannu tana share hawayen ta tana tuno maganganun sa da yace mata Yayan ta zai dawo yau, sosai taji daɗi a ranta, ko ba komi zata samu salama.

     Tana nan tsaye Ester ta zo gidan, wannan dalilin ne ya saka ta samu ta koma ciki, amma sai dai ta hana Ester yin aikin ta, a dole Ester CE zata raka ta tayi wanka, har Toilet suka nufa tare da ita, Ester ta tsaya a bakin ƙofa har tayi wankan ta gama, tafito ta shirya cikin wando Three qwater baƙi, da jan riga me layi-layin baƙi, suka fito Parlour

A taƙaice dai duk inda Ester ta saka ƙafa, RAUDHA na biye da ita tamkar jela, har ta gama aikin ta suna tare, sai dai ta zauna kusa da ita tana kallon ta ba ta cewa uffan.

Ƙiri-ƙiri RAUDHA ta hana Ester tafiya koda ta gama aikin na ta, dole ta zauna suka koma Parlour suna kallo.

????????????????????????????????????????

     Wajen ƙarfe 04:30pm. Drever ya tafi ɗauko su Suhaib a airport, kasancewar kafin Rayyan ya fita ya sanar masa zuwa ɗauko su; tunda shi bazai dawo ba sai dare.

     Koda drever’n ya isa har jirgin su yayi landing, shi ya taimaka musu wajen saka kayan su cikin Boot bayan da suka gama gaisawa, sannan yaja motan suka taho gida.

      Sanda aka buɗe Gate ɗin gidan, RAUDHA dake kwance saman dogon kujera tana jin ƙaran buɗe wa, but bata yi motsi ba don a tunanin ta Rayyan ne ya dawo

Ester itama tana zaune tana kallo.

    A time ɗin ne suka shigo parlour’n da sallama

Jin muryan yayan ta a cikin kunnen ta, ai babu shiri ta wuntsilo daga saman kujeran ta ƙwalla ƙara, tatashi ta nufe sa a guje ta ɗare jikin sa

Bakin Suhaib gaba ɗaya yaƙi rufuwa sabida ganin gudan jinin sa, sai shilla ta yake yi yana juyata a cikin parlour’n, ita RAUDHA tsaban murna har da kukan ta, dole ya koma rarrashin ta yana tambayan ta abinda ke damun ta, dama haka take so sai ta fara masa shagwaɓa

Farida tuni ta nufi cikin parlour’n, ta zauna kan kujera suna gaisawa da Ester

A lokacin ne Suhaib suka ƙariso su ma cikin parlour’n, yana maƙale da RAUDHA suka zauna

Sannan ne Ester ta gaishe da Suhaib, ya’amsa mata cike da fara’a, sallama tayi musu ta fice abun ta

Farida tace, “Ƙanwata babu gaisuwa? Tunda kin samu Yayan ki ko missing ɗina ma ba kya yi”.

Kallon ta RAUDHA tayi tana murmushi, sai kuma ta tashi daga jikin Suhaib, ta koma kusa da Faridan, ta ɗaura kan ta a kafaɗan ta tana faɗin, “a’a Aunty nayi missing ɗin ki sosai da sosai”.

Gaba ɗaya murmushi suka yi me haɗe da farin ciki, don sosai suka ga sauyi a tattare da RAUDHA, tabbas kallo ɗaya kayi mata zaka san tayi sanyi sosai

RAUDHA dai bata sake bi ta kansu ba, sai ta koma yi wa Haneep dake cinyan Farida wasa, tana jan kumatun sa tana tale masa wai sunan wasa, shi kuma ya zuba mata fararen idanuwan sa yana mata dariya yawu na zuba

Ɗaga kai tayi ta kalli Suhaib ta ce, “Yaya har yanzu be dena zubar da silver ɗin ba, be samu sauƙi bane?”

“Ya samu mana Baby, baki ga ciwon cikin sa ya warke ba, shima a hankali halittar sa zai koma normal idan muka ci gaba da nema masa magani, tunda an samu sauƙi yanzu”.

Gyaɗa kai kawai tayi alamun ta fahimta

Tashi Farida tayi ta miƙa wa Suhaib yaron, sannan ta wuce ɗaki ta bar su nan, RAUDHA tuni ta koma kusa da Yayan ta tana ci gaba da jan kumatun Haneep tana sauraron hiran Suhaib ɗin, wanda shi kaɗai yake maganar sa, sai dai ta kaɗa masa kai, ko ta amsa masa da “Umm..” ko “a’a”.

   Kafin dare sosai suka sake ganin sauyi a tare da RAUDHA, gaba ɗaya ta maƙalƙale su, duk inda suka saka ƙafa tsakanin Farida da Suhaib, to, nan itama zata saka nata, tana manne dasu a ko ina, duk a tunanin su tayi missing ɗin su ne sosai, har Suhaib yana tsokanar ta, don shi mamaki abun ya ba shi, tunda wajen kwanaki bata yin masa magana tana fushi dashi, be yi zaton idan ya dawo zata kula sa haka ba, sai hakan ya ƙara saka sa farin ciki, musamman da yaga tayi sanyi matuƙa tana ladab tamkar ba ita ba, sai duk tunanin sa Rayyan ne ya sauya ta, tunda dama ya ba shi amanar ta ne don su samu sauyi, ya san halin abokin sa ba ya ɗaukar raini, bazai yarda da duk wani banzan halin ta da zata iya nuna masa ba, shiyasa yayi tunanin ko a sanadiyar sa zata shiryu, ya sauya mata hali tunda shi bazai iya ba. Kuma abinda ya ƙara basa mamaki ko kaɗan bata yi maganar Rayyan ba, bare kuma ta kawo ƙarar sa akan abinda yayi mata.

     Wajen sha ɗayan dare Rayyan ya dawo a ranan, time ɗin ma RAUDHA tuni tayi barci a ɗakin Farida

Sosai abokan suka yi murna da ganin juna, nan suka yi ta hira suka raba dare.

       ????????????

     Tun daga ranan koda yaushe RAUDHA a ɗakin Farida take kwana, har a time ɗin tsoron kwana ita kaɗai take yi, duk da bata sake yin mafarkin ba amma tsoron yaƙi barin ta. Yanzu ko bi ta kan Rayyan ba ta yi, ko kallo ma be ishe ta ba, dayake shima ba zama yake yi sosai agidan ba a kwanakin, don haka ba sa wani haɗuwa, idan kuwa yazo ya tarar dasu suna zaune a Parlour gaba ɗayan su, to ɗayan biyu ne, ko ta tashi ta bar wajen; ta koma ɗaki. Ko kuma dama tasan ba zama zai yi ba zai fita ne

Shi dai Rayyan mamakin hakan yake yi, abinda ke ɓata masa rai kuma, ko kaɗan ba ta kallon sa, idan har zai dawwama idanun sa akan ta ne, to har yabar wajen bazai ga ta kalli inda yake ba, shi kuma hakan na ƙona masa rai, yana so ma ko ɗan faɗan nan ne ma ya taƙale ta don ta kula sa, amma ba ta zama inda yake, Kuma a kwanakin sosai yake tura mata text message love, koda sau ɗaya ne bata taɓa dawo masa da reply ba, har kiran ta ya gwada yi amma taƙi ɗauka, ya kan rasa wacce iriyan yarinya ce wannan, shin ko dai ba ta soyyayya ne?

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button