RAUDHA Page 31 to 40

Dole Suhaib yaci gaba da cuku-cukun fitar da ita ƙasar India a duba ta.
Sai dai a time ɗin ne wani cuta me suna *Corona Virus (Covid 19)* ya shigo duniya, hakan yasa be samu damar fita da ita ba, don an ce ko wani ƙasa su rufe ƙasar su. babu me shiga bare fita, daga ciki kuwa har da ƙasan Nigeria, duk da a time ɗin jita-jita ake ji a Nigerian.
Allah da ikon sa kuma, acan ƙasan Chaina cutan tayi yawa matuƙa, dole shugaban ƙasar ya ba da umarnin duk wanda ba ɗan ƙasan bane, ayi gaggawar mayar dashi ƙasar su, sannan a rufe musu ƙasa babu me shiga bare fita, a time ɗin har an soma mutuwa, domin acikin ɗan ƙanƙanin lokaci an rasa mutane kusan dubu da ɗorawa. Dole aka saki su Daddy aka mayar dasu ƙasar su
Farin ciki wajen Daddy ba ya misaltuwa, domin a wajen sa ma zan iya cewa yaji daɗin shigowar cutan, tunda gashi a sanadiyar sa an sake su, memakon su yi shekara ɗaya, sun yi FOUR months.
Koda jirgi ya sauke su, sai ya kira Numban Suhaib.
Lokacin Suhaib na cikin asibiti, ya tasa RAUDHA dake barci agaba yana ta faman tunani, ringing wayan sa take yi, but tsaban tunani ya kasa ji
Sai da Nurse ɗin dake gyara wa RAUDHA ruwan da aka saka mata, yayi masa magana sannan ne ya dawo hayyacin sa
Fito da wayan cikin aljihun sa yayi, ganin sunan Daddy ya fito raɗo-raɗo da numban Nigeria, ai zumbur ya miƙe tsaye hannayen sa suna rawa tamkar zai yar da wayan
“Daddy”. Yafaɗa yana bin wayan da kallo batare da yayi yinƙurin ɗauka ba
Sai da ta katse aka sake kira, sannan ne ya ɗauka ya kara a kunne
Anan Daddy yake sanar dashi yana airport na Abuja, ya zo ya ɗauke sa
Ai babu ɓata lokaci ya fice, tsabar murna ma ya manta da cewa ya bar RAUDHA babu kowa a wajen ta, tunda dama Farida tana gida, sai idan zata kawo abinci take zuwa, shi kuma Rayyan aikin sa ba ya barin sa, sai idan ya sami time ne yake leƙowa.
Sai da Suhaib ya kusa isa airport ɗin ne, ya tuna da halin da ƙanwar sa take ciki, sai yanzu ma tunanin sa ya kai ga cewa Daddy fa zai ɗauko, shin ta ya ma zai tunkare sa da maganar ciwon RAUDHA?
“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un”. Abinda ya ke ta maimaita wa kenan
Gaba ɗaya idanuwan sa sun yi ja, sai tarin damuwa dake cikin ransa. Ahaka yayi ƙarfin halin ƙarisawa airport ɗin, duk jikin sa a sanyaye, gaba ɗaya ya rasa nutsuwar sa sai tarin damuwa da fargaba dake tare dashi, abu biyu ne suka haɗe masa a yau ɗin, ga farin cikin dawowar Daddyn sa, ga kuma baƙin cikin halin da ƙanwar sa take ciki, memakon yayi farin ciki sai baƙin ciki da damuwa su suka cika masa ilahirin zuciyar sa.
Yana shiga airport ɗin ya hangi Daddy, fitowa yayi a motan ya nufe sa da sauri
Shima Daddy tun kafin ya ƙariso ya hange sa, nan da nan ya nufo sa fuskar sa cike da fara’a, sai dai yayi mamakin ganin Suhaib shi kaɗai ban da RAUDHA, amma kuma sai ya kau da zancen daga zuriyar sa ya rungume ɗan nasa da ya iso gare sa
Suhaib tsaban murna har da ƙwallan sa, sai faɗi yake yi, “I miss You Daddy! I miss you”.
Ban da buga bayan sa babu abinda Daddy ke yi, murmushi kwance a kyakkyawar fuskar sa.
Sun ɗau kusan mintuna biyu ahaka kafin Suhaib ya janye jikin sa daga runguman da Daddy yayi masa, kallon mahaifin nasa kawai yake yi cike da so da ƙauna, gami da tarin tausayin sa a ransa. Tabbas idan ka kalle sa zaka ga tsantsan raman dake fuskar sa, ga kuma baƙi da yayi duk ya tara ƙasumba, har wani tsufan dole ya ƙara
Daddy dake tsaye riƙe da hannun Suhaib ɗin, murmushi kawai yake zuba wa yana kallon sa, ganin ya ƙure sa da idanu, sai da yaga be da alamun magana sannan ne yace, “My dear Son halan na sauya maka ne?”
Sai a time ɗin Suhaib ya dawo dogon tunanin da ya lula, ya kalli Daddyn yana ƙirƙirar murmushi yace, “Daddy ka matuƙar sauya wa sosai, idan ba don Ni ɗanka bane babu ta yanda za’a yi na gane ka”.
Sai Daddy ya saki dariya yana dukan kafaɗan Suhaib ɗin yace, “ka ganka ko?” .
Shima dariyan yayi yace, “Allah kuwa Daddy, don baka ganka bane, Allah dai ya saka mana duk wanda yake da hannu wajen saka wa a kama ka”.
Murmushi Daddy yayi yace, “Amin, amma ban ga Baby ba, ko bata san na dawo bane?”
Take zuciyar Suhaib ta buga da ƙarfi sabida fargaban da ta shige sa, sai dai ya daure ya ƙi nuna wani alama, illa murmushi da yayi yace, “ban sanar mata bane, sai mun koma ta ganka, nasan hakan zai fi saka ta farin ciki”.
Daddy ya murmusa yace, “ok Mu je to, but mu wuce gidana ne don bazan zauna a na ku ba, inyaso sai ka ɗauko ta ita da matar taka gaba ɗayan su”.
Gyaɗa masa kai Suhaib yayi, batare da ya sake furta komi ba, suka yi gaba suka shiga motan.
Direct gidan Daddy suka wuce, shima babban gida ne da babu kowa sai ma’aikata, su ma jefi-jefi suke zuwa gyara gidan tunda ana biyan su duk wata, Daddy ba ya zama a gidan sai idan zai zo Abuja yin wani kasuwanci, ko kuma time ɗin da yake ganiyan siyasa, idan zasu yi meeting anan yake sauka, har da abokan sa.
Suna shiga Suhaib yayi parcking suka fito, anan ma”aikatan suka taho suna ta kawo musu gaisuwa, Daddy na amsa wa cikin fara’a yana tambayan su iyalai da mutanen gidan, Allah ya ɗaura wa Daddy tausayi shiyasa yake matuƙar girmama duk wani talaka, ko kuma wanda yake aiki a ƙarƙashin sa, be yarda ya wulaƙanta su ba a matsayin sa na me kuɗi, yana ɗaukan su ne duk ɗaya suke, shiyasa su ma suke jin daɗin aiki a ƙarƙashin sa, sam-sam ba shi da wulaƙanci irin na masu kuɗi, gashi da zaran wata yayi zai biya su kuɗaɗen su, duk da kuwa cewa ba zaman gidan yake yi ba, su kuma ba aikin sosai suke yi ba, amma suna samun albashi sosai.
Shi Suhaib tuni ya shige cikin gidan tunda suka gaisa, ya bar Daddy Nan yana ta tambayan su matsalolin su, tare da musu alƙawura idan ya nitsa duk zai sallame su. Bayan ya gama sallaman su sai ya shigo gidan, first abinda ya fara yi wanka, sai da yayi wanka ya sauya kaya sannan ya ci abinci, atare suka ci da Suhaib duk da tsakura kawai yake yi, sosai Daddy ya kula da shi tun a airport be da walwala, ƙarfin hali ne kawai irin na sa, sai be tambaye sa ba shima, a zumman idan suka koma gida zai tasa shi gaba ya sanar masa.
Bayan sun gama cin abincin sun dawo Parlour, ya kalle sa cike da kula wa yace, “Son wai me ke damun ka? Na kula gaba ɗaya nutsuwar ka ba ya tattare da kai? Me ke faruwa faɗa min inji kaji my son?”
Kamar jira yake yi ya tambaye sa, sai ga ruwan hawaye sun soma zuba a saman kyakkyawar fuskar sa
Sosai hankalin Daddy yayi matuƙar tashi, nan ya soma salati yana tambayan Suhaib ɗin me yake faruwa? Hankalin sa duk a matuƙar tashe, rabon da ya ga kukan Suhaib tun yana ƙarami, amma yau gashi har da iyali yana kuka
Suhaib be iya sanar masa da komi ba, illa kukan sa da yaci gaba da yi.
Ana haka sai ga Rayyan ya shigo gidan, domin tunda suka dawo Suhaib ya kira sa ya sanar masa da dawowar Daddy, Shine ya ce masa ga shinan zuwa yanzu, amma kuma zuwan na sa sai ya tarar da Suhaib na kuka, ga Daddy na faman rarrashin sa yana tambayan sa abinda ke faruwa hankalin sa a tashe
Duk da Daddy yayi farin cikin ganin Ɗan Abokin nasa, amma kuma halin da Suhaib yake ciki be sa sun gaisa sosai ba, sama-sama suka gaisa inda Rayyan ya faɗa masa komi na halin da ake ciki