RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

Zai sake yin magana, sai yaji muryan Ammee daga bayan sa tana faɗin, “wai me ke faruwa ne? Menene haka Rayyan lafiyan ka ƙalau kuwa?”

Juyo wa yayi yana kallon ta da jajayen idanuwan sa, be ce komi ba kuma ya raɓa ta yabar ɗakin

Mamaki sosai ya kama Ammee da yanayin da ta gan sa, tabi shi da kallo tana aiyana abubuwa da dama a ranta, sai kuma ta juya ga RAUDHA dake zaune har yanzu ta kasa motsa wa, idanun ta na kafe a inda Ray ya bar wurin. muryan Ammee ya dawo da ita hayyacin ta, sai ta lumshe idanun ta hawaye na cika mata idanu

“Ɗiya ta wai lafiya? Menene ke faruwa? Me Rayyan ɗin ya zo yi wajen ki?”

Matse bakin ta tayi tana buɗe idanuwan ta da suka cika taf da hawaye, cikin rawan murya kamar zata yi kuka tace, “Ammee nima ban sani ba?”

“Baki sani ba kuma?” Ta sake tambayar ta da mamaki

Gyaɗa mata kai tayi don baza ta iya magana ba

Shiru Ammee tayi tana Kallon ta, sai kuma tace, “to meyasa zaki yi kuka Ɗiya ta? Wani abun ya faɗa miki ki sanar dani don Allah?”

Still sake girgiza mata kai tayi alamun babu komi

“Shikenan.. kwanta kiyi barci, zamu yi maganar dashi gobe”.

RAUDHA ba dai tace mata komi ba, ta kwanta tana rufe idanun ta

Itama Ammee juya wa tayi tabar ɗakin tana me rufo mata ƙofa.

Ammee na fita RAUDHA ta buɗe idanunta, sai ga hawaye shaaa sun soma zubo mata

“Ni yake nufin ƴar iska?” Tayi maganar a fili cike da ƙunan zuciya

Duk da ada ya faɗa mata waɗannan kalaman masu ɗaci, amma bata taɓa jin ɗaci da raɗaɗin su a zuciya ba sama dana yanzu, sabida a baya ko kaɗan bata san ciwon su ba, bata san zafin kalman iskanci ba, bata san ma meye ma’anar su ba, da ciwon da yake saka wa duk wanda aka kira sa dashi, alhanin kuma shi ba ya aikata wa

Hawayen ta kawai take share wa tana sake jin tsanan Ray a zuciyar ta, sosai tayi kwanan ƙunci a wannan ranan, don daƙyar barci ya ɗauke ta.

       *WASHE GARI*

    Zuwa la’asar sun gama shirin su, har airport su Zannurain suka rako su, inda jirgin su ya ɗaga.

    RAUDHA dai ta tafi cike da kewar ahalin gidan, sosai tayi shaƙuwa da su wanda bata taɓa yin makamancin sa ba a ƙanƙanin lokaci, tana zaune ne a gaban kujeran Ray, don wajen zaman su ma ba ɗaya bane, ta kwantar da kanta ta rufe idanu tana faman tunani a ranta.

    A airport ɗin Kaduna suka sauka, time ɗin ƙarfe 08:02pm. Ne na dare

Suna fito wa Ray yace mata, “ta biyo shi su shiga mota”.

Kasancewar an zo ɗaukar sa

Bata ce masa komi ba, taja Trolly ɗin ta tayi hanyar barin wajen

Ganin haka ya nufo ta da sauri ya sha gaban ta yana cewa, “ina zaki je kuma? Kin san dare yayi be kamata ki bi hanyar Zaria yanzu ba, tunda kin san doka ce ƙarfe 04:00pm ake rufe hanya, mu je gida na ki kwana, in yaso gobe a kai ki gida”.

Wani kallo ta sakar masa, cike da tsantsan takaici da haushin sa da ta kwana dashi tace, “Ka sani bazan taɓa neman taimako a gare ka ba, ko meye zai same Ni a hanyar nan, na gummaci na bi ta akan dai na je inda kake, Never”.

Ta juya taci gaba da tafiyar ta

Sakato yayi kawai yana bin ta da kallo har ta ɓace wa ganin sa.

[4/7, 9:37 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

      *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

              _Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

”’®Ɗaya tamkar da Dubu”’????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

*RAMADHAN MUBARAKH*????????????

                     2021.

           *TUNATARWA*

_Manzon Allah ya ce mana, “tsabta kam ita ce rabin imani kuma ita ce mabuɗin Sallah. Abu na farko da ake buƙata kafin a shiga sallah shi ne tsarki, tsabta ta zuciya da jiki, ta tufafi da kuma wurin yin sallar._

      _Sallah ibada ce ta ruhu, kuma a cikin ta ne Bawa yake ganawa da Ubangijin sa, yake tsayawa a natse a gaban sa yana yabo yana godiya, yana roƙon Allah ya shiryar da shi bisa ga tafarki madaidaici. Saboda haka bai kamata Bawa ya shiga wannan ganawa ba sai bayan ya shirya kansa da kyau, ya tsarkake jikin sa da tufar sa da wurin sallar sa. Zai yi alwala in ƙaramin tsarki ya kama shi; in kuwa babban tsarki ne sai ya yi wanka don kuwa ta haka ne zai haɗa tsarkin jiki da na zuciya a lokacin ganawar sa da Ubangiji._

    _Allah yasa mu dace._

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON FORTY EIGHT*

_______???? Tafiya miƙaƙƙa RAUDHA tayi, but bata sami abin hawa ba, duk da kuwa ga taxi nan suna ta yawo, da zaran tace musu “Zaria” sai su ce “baza su ba, an rigada an rufe hanya, ko sun je sojoji za su iya kama su, idan ma basu kama su ba, ƴan kidnapped za su iya ram da su, yanzu duniyar abun tsoro ne, an dena tafiyan dare”

Memakon ta saduda sai taci gaba da tafiyan ta a titi, batare da ko tsoro ba, duk da kuwa hanyan ba wai babu ababen hawa bane, tamkar ma rana alokacin

Tana cikin tafiyan ne, motan da aka ɗauko Ray ta faka a gaban ta, taja ta tsaya don bata shaida motan ba, tana ganin ya fito ta ɗaure fuska tana me kawar da kai, har ta soma tafiya ya dakatar da ita ta hanyar shan gaban ta

Wayan sa ya miƙa mata fuskar shi shima babu walwala yace, “gashi Daddy Yana son magana dake”.

Kallon sa tayi still fuskarta a matuƙar ɗaure, tamkar ta share sai kuma ta amsa ganin ya sake ce mata “ta amsa”

Hannu tasa ta amshi wayan ta kara a kunne, cikin raunin murya tana shirin kuka tace, “Daddy”.

“My daughter meyasaka baza ki bi shi ki kwana a wajen sa ba? In yaso gobe ki dawo gida. kin san hanya babu kyau, yanzu kidnappers sun yi yawa, kuma kin san halin su yanzu sai su ɗauke ki”.

Silalo wa hawayen ta suka yi, cikin shashsheƙan kuka tace, “Daddy bazan iya bin sa ba, zan je hotel na kwana”.

“Hotel kuma Baby? please ki bi shi kinji, nasan Baby na yanzu ba ta min gardama tana jin magana ta, just ki bi shi, ba na son ki kwana a hotel sabida ɓata gari sun yi yawa, kina da mutuncin ki baza ki kwana a hotel ba, promise Zaki bi shi?”

Gyaɗa kanta tayi tana ci gaba da hawaye, sai kuma ta buɗe baki tace, “Zan bi shi”.

“Yauwa good girl, Allah ya miki albarka uhm? Ki kula da kan ki, i love You”.

“Me too Daddy”.

Ray dake tsaye a gaban ta, kallon ta kawai yake yi yana sauraron abunda take faɗa, sai dai ba ya jin me Daddy ke cewa, tuni ya faɗa kogin tunani wanda har be san sanda ta ida wayan ba, sai jin dogon tsakin da taja yayi. Waro idanu yayi yana kallon ta cikin ido, kasancewar itama ta kafa masa nata idanun tana mishi kallon tsana, wayan da take miƙa masa yabi da kallo, dai-dai da ta sakar mishi wayan zai faɗi, yayi saurin tare wa yana me bin ta da kallo da har ta wuce zuwa motan. Numfashi yaja batare da yace komi ba yabi bayan ta

Baya ta shiga ta zauna

Shi kuma ya shiga gaba kamar yanda yayi ɗazu, Drever’n yaja motan suka yi gaba, har suka kai babu wanda yayi ƙwaƙƙwaran motsi

Cikin Barrack ɗin sojoji gidan nasa yake, yawanci ginin gidajen duk iri ɗaya ne, gidan sa shi ne number 7.

    Drever’n yana parking Ray ya fito, RAUDHA kuwa bata fito ba sai da taga yayi gaba sannan ta fito tare da Trolly ɗin ta, Drever’n ya amsa ya haɗa dana Ray yabi bayan sa, itama sai ta taka tabi bayan su

Tana shiga parlour’n ta tsaya tana me ƙare wa ko ina kallo, ba wani karikitai bane me yawa a Parlour’n, daga kujeru sai Fridge da kayan kallo, sai wasu Flowers guda biyu da akayi ado dasu a gaban t.v’n, sai kuma hoton shi guda biyu manne a bango, ɗaya da kakin sojojin sa yayi matuƙar kyau, tamkar ka ɗauke sa ka saka a aljihu, ita kanta ya burge ta matuƙa, har ta ƙi ɗauke kai a hoton sai da ta gama ƙare masa kallo, sai kuma ɗayan yana duƙe tamkar yayi ruku’u yana dariya, farar riga ce a jikin sa sai wandon soja…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button