RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

“Haba dai kana nufin Lawan Jaga?”

“Shi fa”. Abokin nasa ya sake tabbatar masa

Da wannan hiran nasu Salman yace, “ai kuwa zai sake dawowa, dama gida an matsa mishi ya fito da mata, shi kuma be shirya auren zumunci ba, kawai shi Ramcy ɗin ce tayi masa a yanzu, bari ya koma ya gwada sa’ar sa”.

Tunda Salman ya soma zuwa gidan su Ramcy, sai kuma ta ɗauki maganar nasa da muhimmanci, domin itama ba wai son sa ne ba ta Yi ba, kawai dai bata saba tsaya wa da samari bane, shiyasa tayi masa kora da hali

Ahaka soyayya me ƙarfi ya shiga tsakanin su, a lokacin tana aji biyu ne a school ɗin ta, shine aka saka rana har sai da ta gama, kuma taƙi yarda ayi har sai da RAUDHA ta dawo, domin tace babu wanda ya isa yayi mata aure idan babu RAUDHA

Shi Baban ta ya san matsayin RAUDHA a wurin ta, shiyasa be damu ba, ya sanya musu ranan auren da yawa, ga shi yanzu har lokaci yayi.

      Washe gari asabar dubban jama’a suka shaida ɗaurin auren Rahma da Doc. Salman. Inda ya tara dubban jama’a sosai, har Suhaib ya zo mata tare da Farida.

    Su RAUDHA iyayen biki, sai cakare wa take yi, ta shiga wannan ta fita wannan ita da Amarya, yawancin kayan da suke saka wa ma iri ɗaya ne, tunda duk RAUDHA ta ɗinka musu

Kasancewar akwai partyn da za su yi, zuwa huɗu aka kai amarya ɗakin ta, gaskiya Ramcy tayi dacen muhalli, komi yaji, kuma ita kaɗai ce a gidan, duk da akwai fili na sauran ƴan uwan Salman ɗin, idan zasu yi auren su ma anan zasu zauna

Ɗakuna biyu ne da Parlour da kichen tare da Toilet, kuma duka an cika ko ina da kaya, musamman ma parlour’n ta da bedroom, kayan da Daddy ya siyan mata ne daga Dubai, kowa ya kalla sai yayi santin su, sosai suka yi kyau ga tsada

Tare da su RAUDHA aka taho kawo Ramcy, zuwa biyar da rabi har sun hallara inda za’a yi partyn, sosai wajen ya haɗu Masha Allah

Duk ƴan uwa sun taru, inda akayi ta yaba kyan da Amarya da ango suka sha, sun yi anko masha Allah, an fara gudanar da shagulgula cikin tsari, inda aka fara kiran Aminin Ango yazo ya bayar da tarihin Ango, riririri haka ya soma basu tarihin Ango suna ta shan dariya, dayake shi ɗin me yawan barkwanci ne, shiyasa yana ba da labarin ne yana saka wasa. Sai da yagama ya koma ya zauna

Inda aka ce Aminiyar amarya itama tazo ta ba da tarihin Amarya, aka kira RAUDHA, sai dai babu RAUDHA a wajen, ba ma ta iso wajen ba, tana can tare da Zulain shi ya tsayar da ita, tasha mamakin ganin sa a bikin, shine yake sanar mata “sun je gidan su ne, Daddyn ta yake sanar dasu suna biki, shine Sharif Ya rako shi nan ɗin tunda shi ya san kan gari” suna zuwa kuma basu sha wahala ba suka gano gidan

Tare suka taho wajen partyn a motan Sharif, tunda duk an watse tana tare dasu bata sani ba, daga tace ma Ramcy bari ta dawo

Suna zuwa a lokacin ne ake neman ta a hole ɗin, Ramcy sai leƙa kai take yi ta gano inda take amma ina bata ganta ba, sosai taji haushi jin M.C na sanarwan “idan babu ita a turo wata ta wakilce ta”

Waya ta ɗauka tana shirin kiran ta, sai gasu sun shigo su uku, RAUDHA na gefen Zulain suna taka wa a tare gunun sha’awa, kasancewar doguwar riga ce a jikin ta, har ƙasa yake jan mata, duk da ta saka Hill shoes, dole take amfani da hannun ta ɗaya wajen riƙe gefen rigan, hakan sai ya ba da wani style ɗin me ban sha’awa, ga shi rigan sosai yayi mata kyau ya ɗauki white skin ɗin ta, golden colour ne da ƙyalƙyalin kwalliya da kuma net da akayi amfani dashi, sai akayi mata light make-up a kyakykyawar fuskar ta da ya ƙara ƙawata fuskar

Masha Allah, kowa ya ɗaura idanun shi a kansu, ba ƙaramin tafiya da imanin jama’an wajen suka yi ba, daga ita har Zulain da ya sha kwalliyan sa cikin Suit farare, da baƙar rigan ciki, kasancewar suna tafiya ne a gaba Sharif na biye dasu a baya, sai kayi zaton su ɗin Ango da Amarya ne, sun yi kyau matuƙa, wasu ma daga cikin matasan har sun gane fuskar Zulain tunda ba ɓoyayye bane a TV. News, ana yawan saka shi idan har kai ma’abocin kallon labarai ne, dana American Dana Nigerian ma gaba ɗaya, to zaka iya sanin sa.

     RAUDHA jin ana kiran sunan ta, kai tsaye can ta wuce ta amshi abun maganar ????, tana murmushi ta soma ba da tarihin Ramcy da harshen turanci, duk da tana haɗa wa da larabci

Hakan sai ya sake birge mutane sosai, nan akayi ta mata tafi, sosai ta tafi da imanin duk wani saurayi me ji da kansa.

    Tana gama wa ta koma inda su Zulain suka zauna, hakan ya hana mutane da dama zuwa wajen ta, tunda sun ganta tare da saurayin ta.

     Ba’a tashi ba, su Zulain suka yi mata sallama suka tafi.

     Koda aka tashi a motan amarya da ango RAUDHA ta koma gida, duk da abokan ango suna ta mata tayin hawa motan su, amma ko kallo basu ishe ta ba, hakan yasa ma ta hau motan su Ramcy suka wuce gida.

    A can suka kwana da sauran ƙawayen, tunda dama al’adan su ne, ana kwanar wa Amarya, sai washe gari kowa ya watse, sanda RAUDHA zata tafi Ramcy tasha kuka, ta hana ta tafiya, RAUDHA me zata yi in ba dariya ba, ita abun ma dariya yake bata

Dama a lokacin akwai Salman sun zo da Abokin sa, su ma dariyan suka soma mata, sai daga baya da yaga da gaske dai kukan take yi taƙi barin RAUDHA ta tafi, shine ya zauna rarrashin ta, daƙyar ta yarda ta bar RAUDHA ta tafi

Abokin Salman ɗin shi ne ya dawo da ita gida, tunda Salman ɗin ne ya saka a dawo da ita

Tun a mota yake ta mata surutu, ita dai ko sauraren sa ba tayi, don ba ta son ma ta bashi ƙofan da zai iya ce mata yana son ta, saboda ta ga take-taken haka a wajen sa

Sabit ganin yanda ta nuna masa, shima sai ya kama kansa don yasan yarinyan ƴar zafi ce, yana kai ta suka yi sallama ta wuce gida, shi kuma yaja motan yabar gidan, duk da a ransa ba haka yaso ba.

????????????????????????????????????????

       *AFTER ONE WEEK*

     Yau Sunday ranan da RAUDHA za su haɗu da Ray, sosai yau ta tashi cikin zumuɗi, tun jiya ta saka masu aikin ta suka yi mata irin su soye-soyen nan, cake????, cin-cin da su nama, duk ta saka aka soya mata, yau kuma ta sanya su suyi mata girke-girke kala-kala, sannan su shirya mata a ƙaramin parlour’n sama

Yau dama Daddy Yana da inda zai je, shiyasa tun safe ma ba ya gidan, duk da kuwa yasan da zuwan Ray ɗin, but yarigada yace wa RAUDHA tace masa ya jira sa, saboda yana so yayi masa maganar auren su ne, idan da gaske yake yi ya turo.

        Sai da ta tabbatar sun gama shirya mata komi yanda take so sannan ta baro parlour’n taje ɗakin ta ta shiga wanka, tana fito wa ta zauna a gaban mirror ta soma tsara kwalliya a kyakykyawar fuskar ta, tana yi tana lumshe lumsassun idanuwan ta fuskar ta cike da annuri, tunanin kawai yanda za su haɗu da Ƙalby ɗin ta take yi yau, har ta ƙosa mintocin da suka rage haɗuwar su suyi ta haɗu dashi

Light make-up tayi, amma bakin nan ya sha jan jambaki tamkar zai dubo sabida maiƙon sa, kayan ta ta saka, riga da skert na atamfa, yau ce rana ta farko a rayuwar ta da zata fara saka kayan Hausa wa, tun sanda Ammee ta ɗinko mata ta dawo dasu bata taɓa saka wa ba, ko a bikin Ramcy babu kayan hausawan da ta ɗinka musu daga ita har Ramcy ɗin

Ray da kansa ya ce mata “ta saka mishi yau domin yaga yanda kayan za su yi mata” shi dai a rayuwa yana son ya ganta sak da kayan Hausa wa tushen ta, hakan yasa itama a ranta taji tana ƙaunar sakawan sosai, ko domin ta burge sa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button