RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

“Ok yanzu har kin hau mota ne, ko kuma Yayan naki zai kai ki?”

Gajeren tsaki taja tace, “wa yace maka yaya na ne shi? Allah ya kiyaye”.

Dariya ne ya so ƙwace masa, sai dai ya daure yayi murmushi yana cewa, “amma ai a matsayin Yayan ki yake, ko ba komi ma ya girme ki”.

“Ƙalby ka dena min maganar mutumin nan, idan ba so kake yi mu ɓata ba, raina a ɓace yake wlh”.

“I’m so sorry Pretty, Allah yasa dai ba shi ne ya ɓata miki rai ba?”

Cike da jin haushi tace, “shi ne mana, dama idan ba shi ne ba, waye ya isa ya ɓata min? wlh Ƙalby na matuƙar tsanar sa fiye da komi dake duniyar nan, da za’a bani bindiga wlh sai na harbe shi, babu wanda ya taɓa shiga rayuwa ta ya muzguna min irin sa, a kansa na soma kwana da baƙin ciki, kuma na tashi da shi, a kan shi nake zubar da hawaye a koda yaushe, bazan taɓa yafe masa ba”.

Sosai jikin Ray yayi sanyi ƙalau, muryan sa a sanyaye yace, “Why kika tsani bawan Allan nan haka? Ni naga tamkar gyara yake miki, mene ne aibun shi a ciki?”.

Lumshe ido tayi batare da tace komi ba

Sai da ya kira sunan ta sannan tace, “idan har kana so mu ci gaba da rayuwa a haka, kar ka sake min maganar sa, idan kuma ba haka ba”. Sai tayi shiru kawai batare da ta ƙarisa ba

Murmushi yayi me ciwo yace, “wato nima zaki tsane Ni Ko? Ke kenan babu wanda ya isa ya faɗa miki Gaskiya? Pretty ki bi duniyar nan a sannu, komi kika gani a..”

Ƙit tayi cancel ɗin kiran, sannan ta kashe wayan gaba ɗaya tana me ajiye wa saman cinyan ta, rufe idanuwan ta tayi. Bata sake motsi ba har sanda Drever’n ya sanar mata sun iso Zaria, sai anan ta buɗe ido ta faɗa masa inda zai kai ta.

    A bakin tanƙamemen gate ɗin gidan su ya faka, tayi masa maganar yayi horn

Horn ɗin yayi kamar yanda ta umarce shi

Me gadi ne ya leƙo, ganin taxi sai ya fito ya taho, har zai fara faɗan sa kamar yanda ya saba sai ya hangi RAUDHA dake zaune a baya, nan ya washe baki ya soma kwarara mata gaisuwa tare da maraba

Ɗaga masa kai kawai tayi, sannan tace masa, “ya buɗe musu ƙofa”

Da saurin sa kuwa ya koma ya buɗe, me Taxi yaja suka yi ciki

Dayake da tafiya sosai, shiyasa taƙi sauka tun daga wajen, har bakin ƙofan parlour’n gidan ya kai ta ya ajiye, sannan tafito ta miƙa masa 5k da ta zaro

Masu aiki biyu maza da suka hango ta, su suka ƙaraso suka yi mata sannu da zuwa, sannan ɗaya yaja mata Trolly ɗin ta suka yi ciki.

      A lokacin babu Daddy a gidan ya fita, tunda ta tambaya akace mata ba ya nan, sai ta wuce ɗakin ta , wanka ta soma yi ta hau yin breakfast da tasaka aka shirya mata, sai da taji ta ta ƙoshi sosai sannan ta zauna tana me jingina da kujeran ta lumshe idanun ta, bata sake motsa wa ba har wajen shuɗewar mintuna 20, lokacin sosai idanun ta suka rufe da barci, kan gado ta faɗa ta hau sheƙawa.

      Time ɗin da Daddy ya dawo, sannan tana barci, shiyasa be tashe ta ba har sanda ta farka don kanta, anan ne suka gaisa har yake tsokanar ta “ya ga ta sauya ne, duk tayi yaushi, ko dai tafiyan ne ya sata haka?”

Dariya tayi tace, “Daddy kenan, ai ba yau na saba tafiyan ba, kawai zaman mota ne daga Kaduna zuwa nan ya gajiyar dani”.

Shafa kanta yayi yana murmushi yace, “Daughter kin ganki ko? Akwai ragwanta wani lokacin, amma Captain ɗin ya kawo ki, ko saka wa yayi a kawo ki?”

Tana jin sunan sa ta sauya fuska tana ƙara lafe wa ajikin sa, kamar bata so tayi maganar tace, “Ya saka an kawo Ni ne”.

Domin tasan idan tace motan haya ta hau, ya dinga maganar kenan, ita kuma ta tsani duk wani magana da ta shafe sa a yanzu

Saurin ma sauya hiran tayi da maganar bikin Ramcy, haka suka ci gaba da hiran su, inda Daddy yake shawaran abinda Ya kamata yayi wa Ramcy ɗin a bikin

RAUDHA kuma ta bashi shawaran yayi mata kayan ɗaki

Yace, “ok babu damuwa, yanzu kuma zan buga waya a samo mata masu kyau koda a nan Nigeria ne, tunda naga yanzu su ma suna yin kaya masu kyau, zan kira mahaifin ta, idan za su yi mata sai su fasa su yi wani hidiman da kuɗin”.

“Yauwa Daddy, Amma Daddy a ƙoƙarta idan na waje zai samu ayi mata, ka ga yanzu ana fita Abroad sosai ba kamar watannin baya ba”.

“To my dear duk yanda kika ce ai, insha Allahu za’a samu ma kafin bikin” 

Daga haka hiran suka ci gaba da yi, inda RAUDHA take ta mishi lissafin abubuwan da zasu kashe daga ita har Ramcy ɗin na hidiman biki, yace, “zai bata kuɗin”.

[4/9, 8:37 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

*RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR:* ✍️

_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

”’®Ɗaya tamkar da Dubu”’????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

*F.W.A????/*

*RAMADHAN MUBARAKH*????????????

2021.

            *HADHISI*

_An karbo dga Aisha Allah yqara yarda agareta tace ” Manzon Allah s.a.w ya aureta tana da shekara shidda,kuma yatare da ita tana da shekara Tara,kuma Allah ya karbi ransa tana er shekara sha takwas.

Muslim ya ruwaito_

.

*NOT EDITED* ___________________________????

*SEASON FIFTY*

_______???? Washe gari RAUDHA ta haɗa Trollyn kayan ta ta wuce gidan su Ramcy, a ranan ma suka koma gidan RAUDHAN, ita da Ramcy da wasu tsirarun ƙawayen ta calss mate ɗin ta da suka zo mata biki, acan za su zauna ayi mata gyaran jiki da RAUDHA zata ɗau nauyi, da duk wasu shirye-shirye da ya kamata su yi

Duk a ranan ne dai me gyaran jikin ta iso aka soma wa Ramcy gyaran jiki, su kuma su RAUDHA da sauran ƙawayen su ne masu fita suyo abubuwan buƙata, duk a motan RAUDHA ake fita, duk da su ma ƴan matan ƴaƴan masu shi ne, wasu ma aciki da motan su suka zo, ga su suna da iyayi irin na gogaggun ƴan bokon nan ƴaƴan masu hannu da shuni, amma tunda suka ga RAUDHA sai suka raina kan su, ko wacce cikin su tana so ta shige mata

Ita kuwa ko kallo basu ishe ta ba, idan ma tana son yin abu, sai dai ta tambayi Ramcy, ita kuma Ramcy sai ta haɗa ta dasu su taimaka mata, shiyasa suke fita tare, ahaka har suka soma shige mata tana kula su, shima sai su ne suka tsulmo ta cikin zancen su

Itama RAUDHA har da ita akayi mata gyaran jikin kaɗan, ta ma ce ba ta so but Ramcy sai da tasaka akayi mata

Komi sun shirya agidan, inda suka koma gidan Aunty Nafeesa ana gobe bikin, don acan za su yi taron su na ƙawaye.

      Gidan su Ramcy ya cika maƙil da mutane, domin babu laifi suna da dangi sosai, musamman dangin Mahaifiyar ta, su ma sun zo da yawa, duk da ba Mahaifiyar a raye amma sun yi mata kara sosai, haka zalika Amaryar Baban su ma tayi gayya sosai, tunda ita a wurin ta ta riƙe su Ramcy tamkar ƴaƴan ta ne, sai kuma dangin Mahaifin ta, duk da su anan Zarian suke ma.

      Doctor Salman sunan Mijin da Ramcy zata aura, anan Zarian yake, a cikin samaru, babu laifi suna da hali sosai, don zan iya cewa ma, duk a cikin ƴan uwan sa ya fi su samun kuɗi, lokacin da Ramcy take zuwa A.B.U Zaria suka haɗu dashi, inda shi kuma ya je karantar wani course, kamar da wasa dai abun nasu, domin ita Ramcy taƙi ba shi damar yaga gidan su ma, a school kawai suke haɗuwa su gaisa, har ma sun rabu daga baya, tunda shi shekara ɗaya kacal yayi a lokacin. Sai kuma watarana kwatsam ya zo anguwan su wajen wani abokin sa, suka sake haɗuwa ita kuma ta fito gidan Aunty Nafeesa, anan yake faɗa wa abokin nasa “ita ce wacce ya so ta bashi dama taƙi” shine abokin yace “ai kuwa ga gidan su can idan kana so in Kai ka, ai Yayan ta Aboki na ne, Lawan”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button