RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

Maganar Ray ɗin ne ya dawo da ita daga tunanin da ta afka wajen ƙare wa hotunan kallo, sai ta zubo masa idanu cike da jin haushin kanta da ta tsaya tana kallon sa a hoto, don ta nuna masa ba burge ta yayi ba, sai ta taɓe baki ta furta, “ko kyau! Sai mugun hali”.

Ray ya ji ta sarai, sai yayi murmushi kawai yana yin gaba zai shige ɗaya daga cikin ƙofofin biyu da suke jere, sai da ya kusa shige wa sannan yace da ita, “ta shiga ɗaya ɗakin”

Taka wa tayi ta buɗe ƙofan ta shiga tare da Trolly ɗin ta da ta ɗauka a Parlour, babban ɗaki ne me Toilet a ciki, gado ne kawai da sip, sai lallausan carpet ɗin ƙasa, baya ga haka babu komi ciki. Kan gadon ta nufa ta zauna tana me zare veil ɗin da tayi rolling da shi a kanta, babu abinda take yi sai faman taɓe baki tana bin ko ina da kallo, tare da karkaɗa ƙafafun ta dake lilo ƙasan gadon

Kamar shuɗewar mintuna goma sai ta miƙe ta shiga Toilet, wanka ta soma yi ta ɗauro alwala, ta saka riga da wando masu taushi na barci, sannan ta ɗaura Robber White Hijab tayi Sallah, bayan ta idar ta koma kan gadon ta kwanta tana me zame hijabin daga jikin ta. Shiru tayi tana tunani a ranta, sosai take jin yunwa a wannan gaɓar, amma kuma ba shi ne damuwar ta ba, illa kewar Ƙalby ɗin ta da ya addabi jiki da ruhin ta, yau kwata-kwata ba su yi waya ba, tunda tun jiya rabon ta da shi, ga shi ko text be tura mata ba, ta hau social media Nan ma bata ga saƙon sa ba, duk da kuwa ta ga ya hau, kuma ta tura masa saƙo be buɗe ba, ta rasa meyasa yau yaƙi kula ta, har kiran sa tayi ya ƙi ɗauka, daga ƙarshe ma sai ya kashe wayan, ko kaɗan bata san laifin da tayi masa ba, duk da kuwa tana ji a jikin ta fushi yake yi da ita..

     Ajiyan zuciya ta sauke, kana ta janyo wayan nata ta sake kiran sa, wannan karon ya shiga, sai dai har ta gama ring be ɗaga ba, sake kira tayi, anan ne yayi peacking

Wani sassanyan ajiyan zuciya ta sauke har tana lumshe idanu, sai ta kara a kunne kawai ta sakar masa kuka

Shiru Ray yayi a ɓangaren sa, yana me sauraron kukan nata dake shiga masa can cikin kunne, yana saukar masa da kasala, lumshe idanu yayi batare da yayi ƙoƙarin dakatar da ita ba, domin kuwa sosai sautin kukan nata yake masa daɗi

Ganin yayi banza da ita, sai ta ƙara Volume ɗin kukan nata, har da buga ƙafafu

Dariya ne ya so kufce masa, domin kuwa yana jiyo buga ƙafan da take yi akan gadon, danne dariyan sa yayi yace, “Sweetheart mene ne?”

Cikin kukan take cewa, “ba kai ne ba!”

“To me nayi uhm? Faɗa min inji?”

“Ka ƙi kula Ni yau gaba ɗaya, kuma yanzu na kira ka, but kana son share Ni har kaƙi rarrashi na”.

Murmushi me sauti yayi, cike da farin ciki a zuciyar sa yace, “I’m so sorry pretty uhm? Ki yafe wa Ƙalby bazai sake ba”.

“To sai ka faɗa min abinda nayi maka yau kaƙi kula Ni”. Tayi maganar cikin shagwaɓa

Lumshe idanuwan sa yayi, cikin sanyi yace, “Babe zaki kashe Ni da wannan shagwaɓar taki”.

Daɗi taji a zuciya, sai ta sake ɓare baki ta hau masa shagwaɓa

“Pretty idan na kama ki ko!” Sai ya cije bakin sa yana me jan numfashi sosai

Ita kuwa dariya ta ƙyalƙyale masa dashi tace, “to ka sanar dani meyasa ka ƙi kula Ni yau?”.

“Ina fushi dake ne sabida kin min laifi”.

Waro ido tayi, sai kuma ta marairaice fuska kamar zata yi kuka tace, “to me nayi maka?”

“Kin yi min alƙawarin Ni kaɗai zaki so, Ni kaɗai zaki kula a matsayin wanda zaki aura, amma kuma kina kula wasu”.

Sosai wannan karon ta waro idanun ta waje, cikin mamakin sa tace, “ban gane ba Ƙalby, ya akayi kasan cewa ina kula wani?”

“Ok da gasken kenan kina kula su?” Yayi maganar cike da kishin da dole sai ka gane ran sa babu daɗi

Tayi saurin cewa, “no Ƙalby, na rigada nayi maka alƙawarin kai kaɗai zan so, kuma kai zan aura, har yanzu kuma ban karya alƙawarin ba, har yanzu kai ne kaɗai wanda nake kallo a matsayin miji na uban ƴaƴa na, kai kaɗai ne a zuciya ta, domin tuni narigada na baka kyautar ta,”.

Sosai Ray yaji daɗin zantukan ta, har yana jin wani irin sanyi sosai wanda tun jiya be ji irin sa ba, gyara zaman sa yayi daga kan kujeran da yake zaune, sannan yace, “Allah ko Baby na Ni kaɗai?”

Murmushi tayi tace, “kana tantama ne?”

“A’a na yarda dake ɗari bisa ɗari, I love You My pretty”.

“Me too dear, amma yaushe zamu ga juna, na ƙosa wlh”. Tayi maganar cikin shagwaɓa

“Pretty kenan! To ki saka mana rana”.

“Da gaske Ƙalby? Tafaɗa da farin ciki

“Da gaske Baby na, ai nima na ƙosa mu riƙa soyayyar fili ba na waya ba”.

“To shikenan, ka bari zuwa bayan bikin Besty na sai mu haɗu, sabida daga yau har Sunday ba na da time”.

Yace, “amma kiyi min alƙawari duk rintsi duk wuya baza ki taɓa rabuwa dani ba, Ina jin tsoro Pretty, Ina jin tsoron idan kin ganni ki ce ba kya so na, baza ki aure Ni ba, idan kuwa haka ta faru mutuwa zan yi”.

“Ƙalby wlh nayi maka alƙawari, duk rintsi duk wuya ina ƙaunar ka, bazan taɓa rabuwa da kai ba, nayi maka alƙawari zan aure ka”.

Murmushi yayi me sauti yace, “Nagode Baby na, Allah ya bar min ke”.

“Ameen ameen Ƙalby”. Itama tafaɗa tana dariya

Daga nan sun taɓa hira kaɗan kafin suka yi sallama, ajiye wayan tayi tana lumshe idanu tare da faɗa wa duniyar kogin tunanin Ƙalby ɗin ta, murmushi kawai take zuba wa idanun ta a rufe

Numfashi taja kafin ta buɗe idanun tana ɗaura hannayen ta kan shafaffen cikin ta, sosai take jin yunwa don haka dole ta nemi abinci taci, tsaki taja tana tashi zaune tace, “bari inje wajen wancan mahaukacin sojan nace ya bani abinci, wlh yunwa nake ji bazan iya kwana a haka ba, dole ne ma yasan yanda zai yi dani…”

Bata ƙare maganar ba taji saukar muryan sa yana faɗan, “wato Ni ne mahaukaci ko?” Yayi maganar yana tsaye bakin ƙofa riƙe da handle ɗin, idanun sa a kanta

Waro ido tayi tana ɗan ja baya, mamaki ne ya kamata don bata ji motsin sa ba ko kaɗan har ta miƙe tana shirin fita

“Ki bar zaro min idanu ki amsa min tambaya na, Ni ne mahaukacin ko?”

Ɗaure fuska tayi tana me kawar da kanta, tare da kumbura baki, sai kuma ta taɓe shi tana me ɗage kafaɗa tace, “kafi kowa sani ai”.

Murmushi Ray ya saki yana me takowa cikin ɗakin sosai, ledan da ke hannun sa ya miƙo mata yana me faɗin, “zan ko nuna miki Ni mahaukacin gaske ne, na kula sabida ban ɗaukar mataki a kanki kike yi min duk abinda kika ga dama, komi dake bakin ki kina faɗa min batare da kin ji tsoro na ba, kin manta Ni Yayan ki ne, zan iya miki hukunci a duk sanda naga dama”.

Dogon tsaki taja cike da haushin maganar sa ta kalle sa tace, “waye kai? Ban san ka ba, kuma baka isa ka zama yaya na ba, idan ka isa kai kai ne, ka ɗauki mataki a kaina sannan zan tabbatar, ko kaɗan ba na jin tsoron ka domin kuwa baka kai matsayin ba, baka isa RAUDHA ta saka ka a cikin lissafin ta ba..”

Bata san sanda ya iso gare ta ba, sai ji kawai tayi ya murɗe mata baki, yana faɗin, “I will teach you a lesson now”.

Be bata damar ma magana ba ya saki ledan hannun sa ya janyo ta jikin sa, sai kawai ji tayi ya haɗe bakin su waje ɗaya

Wani irin zaro ido tayi waje, babu shiri ta haɗiye yawu cike da tsantsan tsoro da mamakin sa.

[4/7, 11:42 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

*RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button