RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

*MALLAKAR:* ✍️

_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*FEENAH WRITER’S ASSO*????

”’®Ɗaya tamkar da Dubu”’????✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*????

*F.W.A????/*

*RAMADHAN MUBARAKH*????????????

2021.

.

*NOT EDITED* ___________________________????

*SEASON FORTY NINE*

_______???? Sosai Ray yake tsotson bakin ta tamkar ya samu Lolipop, ko kaɗan yaƙi bata damar da zata iya ƙwatan kanta, duk da kuwa kici-kicin da take yi domin gujewa abinda yake mata

Sosai ta gaji dole ta ƙyale shi ta dena ƙoƙarin ƙwace kanta, sai kawai ta soma zubar da hawaye tana sauraron saƙon da yake bata, rufe ido kawai tayi zuciyar ta na ƙara cinkushe wa da tsanar sa

Ray sai da yaga ya kusa losing control ɗin sa, kafin yayi ƙarfin halin sakar mata bakin ta yana me ja baya a hankali cike da kasala

Kallon ta kawai yake yi yanda ta tsaya tana ta kwararan hawaye idanun ta arufe

“Daga yau ki sake yi min rashin kunya, tara ki nake yi dama, kuma duk zan fanshe, idan hakan ta sake faruwa a tsakanin mu, to ba iya nan zan tsaya ba, don dai Ni ina da tsoron Allah ne ba irin ki ba”.

Juya wa yayi ya wuce ƙofa zai fice

A lokacin ne ta buɗe jajayen idanuwan ta tana kallon sa, cikin ƙunan zuciya tace, “har abada bazan taɓa yafe maka ba, na matuƙar tsanar ka fiye da mutuwa ta, komi da komi dake tare da kai ba na ƙaunar sa, MAHAUKACI KAWAI”. Taƙare maganar cikin ɗaga murya, don ba kaɗan ba kalaman sa suka yi mata ciwo

Be ce mata komi ba, illa murmusawa da yayi ya buɗe ƙofan yana shirin fita

Hakan sai ya ƙara mata zafi a zuciya, domin so take yi ta ƙuntata masa kafin ya bar ɗakin, cikin tsanar sa tace, “Mutanen kirki ba sa nuna kansu, sai dai ayyukan su su bayyana su, kai ko kaɗan ba ka a cikin su, domin ayyukan ka tuni sun bayyana min kai tantirin ɗan iska ne, masu fake wa a cikin mutanen kirki, alhanin irin ku su ne ɓatattu”.

Sosai kausasan kalaman ta suka taɓa sa, juyo wa yayi yana kallon ta ido cikin ido, sun ɗau two minutes suna aika wa junan su kallo, kafin ya tako ahankali zuwa wajen ta, har yanzu kuma idanun su na a cikin juna, sai da ya tsaya gaban ta kafin yace, “kina bani mamaki RAUDHA, idan kina yin wani abu sai in ga tamkar baki da wayau, koda yake har yanzu ke yarinya ce, amma kuma ina me miki nasiha ki zama na gari a duk inda kike, har yanzu da sauran ki a cikin rayuwar nan, abu ɗaya yake hana Ni faɗa miki kalaman da zaki dauwama kina me dana-sani, dana-sanin rayuwar ki, amma kuma..”

Sai yayi murmushi yana fito da harshen sa waje, ya karkaɗa sa yana cewa, “amsa ɗaya nake so ki bani, ɗaya tak. Da Ni da ke ina son sanin waye ɗan iska?”.

Sai yayi dariya yace, “ba ma sai kin bani amsa ba shalele na, Ni ai ƙaramin ƙwaro ne a iskancin domin ban san komi ba, ke kuwa da, Kin dauwama ne a cikin ta tun kina ƙaramar ki, ga shi har yanzu kin kasa gane Allah ya faku bare ki tuba, ko ba ke ce na kama ki jiyan nan da ƙani na kuna abinda kika saba ba? To ki soma gyara kanki kafin ki ce zaki zagi wani”.

Juya wa kawai yayi ya bar ɗakin batare da ya jira cewar ta ba, yana fita ya zauna kan sofa a parlour, yana me ɗaura kansa jikin kujeran tare da lusmshe idanu

Allah ya sani shi kansa ya san yaji baƙin cikin kalaman nan da ya faɗa mata, amma ya zai yi? Yana son ne ya saka mata zafi a zuciya, ta yanda zata gyara halayen ta, domin idan taji raɗaɗin maganar sa wataƙil ta iya gyara wa, amma kuma yaga da alamu yana son ɓata rawan sa da tsalle, ko in CE ma tuni ya ɓata, kullum daɗa ƙara tsanar sa a zuciyar ta yake yi, shin ya zai kasance idan har ta gane shine masoyin ta taƙi shi? Yasan babu ta yanda za’a yi RAUDHA ta so shi, amma ya zai yi? Wani hanya zai bi don cire tsanar sa dake zuciyar ta, ya rasa ya zai yi, duk da kuwa sosai yake danne duk wani ɓacin rai da take ƙunsa masa, ya kasa ɗaukar mataki, idan da ace babu soyayyar ta a ransa, da tuni ya aikata mata abinda baza ta taɓa manta sa a rayuwar ta ba.

                    ????????????

    Tun sanda ya soma maganar sa hawayen fuskar ta suka ci gaba da tsiyaya kamar an kunna famfo, yana fita ta fashe da kuka tana zame wa ƙasa anan, haɗa kai da gwiwa tayi ta soma rusa kuka cike da baƙin ciki a zuciyar ta, “shin me tayi wa bawan allan nan ne ya tsane ta? Meye alaƙar ta dashi ne da yake shiga rayuwar ta?” Babu abinda ke ƙona mata rai sai kallon ƴar iska da yake mata, kalman iskanci da yake jifan ta dashi, shi yafi komi ƙona mata rai

Ɗago kai tayi da fuskar ta yayi caɓe-caɓe da hawaye, cikin kuka tace, “I hate you RAYYAN! I hate you so much!”

Ta sake fashe wa da wani sabon kuka, ta jima a wajen a zaune tana ta faman kuka taƙi ta dena, dama RAUDHA ga taurin kai da naci. Ahaka ta kwana a zaune bata ko jirga ba, duk da uwar yunwar dake addabar ta, amma ta gummaci ta kwana a haka, da dai taci abinda ya kawo mata

Da asuba ta farka daga figaggen barcin da ya ɗauke ta, daƙyar ta iya ɗago kanta da ya riƙe yayi mata zafi, idanuwan ta kuwa sun yi luhu-luhu alamun tasha kuka da kuma rashin barci, gaba ɗaya fuskar ta yayi jazur tamkar tattasai

Miƙe wa tsaye tayi daƙyar, ƙafafuwan ta sun rigada sun yi tsami, dole ta kasa taka wa, ta daɗe tana yarfe ƙafafun kafin ta samu su yi mata dama-dama, ahankali ta taka ta wuce Toilet ta ɗauro alwala, sallah tayi da Hijab, sannan ta miƙe ta ɗauki veil ɗin ta da ta cire ta mayar

Baza ta iya sake yin wasu mintoci a gidan nan ba, ko kaɗan ta tsani komi da zai fito daga Ray, ba don jiya dare yayi ba, da adaren jiyan zata bar gidan, sai kuma ta yanke shawaran da asubahin nan zata bar masa gida

Tana gama rataya veil ɗin taja Trolly ɗin ta tafito Parlour, ƙofa tayi ta buɗe ta fice, dayake ya fita zuwa Masallaci kuma be dawo ba, har tabar haraban gidajen bata haɗu da kowa ba, tafiya sosai miƙaƙƙiya tayi har tafito bakin titi, zuwa lokacin daƙyar take iya ɗaga ƙafafun ta, amma haka ta daure take ta jan su har ta fice bakin titi, a lokacin gari ya fara haske sosai har ababen hawa sun soma wuce wa, nan ta tare keke napep tace “ya kai ta Kawo tasha ta hau mota”

Suna zuwa ta samu taxi ta shige, ita ce ta farko, amma dayake ta ƙosa ta bar wajen, kar ma ya biyo bayan ta, tace ma me motan “su tafi zata biya sa kuɗin” haka yaja suka bar tashan suka yo hanyar Zaria.

                ????????????

     Sanda Ray ya tashi duba ta wajen ƙarfe 08:40am ne, koda yaga ba ta cikin ɗakin hankalin sa yayi matuƙar tashi, tunda yaga babu Trolly ɗin ta ya san tafiya tayi, nan ya biyo hanya ko zai ganta, amma Allah be sa ya ganta ba, dole ya ɗauki waya ya soma kiran ta, sai dai alokacin RAUDHA na cikin mota tana kallon wayan taƙi ɗauka, gaba ɗaya ba ta jin daɗin jikin ta, ga barci dake damun ta shiyasa taƙi ɗauka

Sai da taga ya ƙi ya dena kiran, kafin tayi peacking tana ƙara wa a kunne

Sallama yayi mata. Ta amsa shi cikin dashashshiyar muryan ta da ya ƙara shige wa sosai sabida kukan da tasha

“My Pretty lafiya dai naji muryan ki ba ta fita, ina fata dai lafiya ba wani abu ne ya same ki ba?”

Sai da taja majina tana jingina bayan ta da jikin kujeran kafin tace, “lafiya”.

“Anya? ban yarda ba, but naji kamar ƙaran ababen hawa, ina zaki haka da sassafen nan?”

“Ƙalby gida zan je, kasan dama nace maka ina Kaduna ne”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button