ALIYU GADANGA 1-END

ALIYU GADANGA Page 21 to 30

Tundaga Falon sukafara Rikita juna,Aliyu ya Ruda Azeema da salon yadda yake shafata,itama ta Rudashi da salon yadda take lasan gefen wuyansa cikin kwarewa dakyar suka yada zango abedroom aka Shiga Second Round na biyu,lalle Azeema ta Fahimci gidan Soja ba wajen wargine bane sai da ta dinga hadawa da roko da kuka da magiya kana ya Saurarata mata,ammh bawai don ya gaji ba,Lakwas tayi ajikinsa tana kananun kuka ya Rumgumeta yana dariya yake fadin”Srry pretty Za”a bani na anjuma…”Harara ta dago ta makamai harda murgudamai baki,Saurin Cafke lebenta yayi yana Tsotsa sai da ya sha ma”ishi kafin ya saketa yana fadin”Horo mai hade da gargadi ko hararata kika kara wlh sai na kara..”Jin haka yasa tayi gum da bakinta tana kara lafewa akirjinsa Rikota yayi dakyau yana fadin”Afuwa Afuwan Zeema kaduna,Allah ya biyaki Kinji matata ngd sosai Nasan ke Jaruma ce,Tunda kike iya daukan Nauyi Aliyu..”Yafada yana leka Fuskatarta Kin yarda tayi saima kara dunkula kanta da take bisa kirjinsa tana shagwaba Shiko yana tsokanarta yana dariya Ahaka barci ya kwasheta Shiko Shuru yayi yana Nazarin yadda rayuwarsa ta chanza lokaci daya ta dalilin Azeema Kanta ya Sumbata yana fadin” *I LOVE U AZEEMA..Buh not Azeema gombe i mean ZEEMA KADUNA.* yafada yana dariya Shikadai.

   

___________________

  _Gombe_

       

  “”Azeeza tana ta Sauri zata gida tadawo daga shago inna ta aiketa Siyo suga alokacin da misalin karfe Goma ne na safe,Taji Sauki ba kamar da ba,ammh haryanzu ramanta na nan da yadda duk Fuskarta ta chanza,Saurin datake Shiyasa bataji karan hon din da suke zubamata ba,sai da suka zo gabda da ita suna Rangadamata sallama.

Afirgice ta waigo take kallonsu Suna zaune cikin wata bakar Venza mai kyau da yarari,Dukkansu matane,sanye kuma da bakaken abaya kowacce tayi Rolling din kanta da dan gyalen Abayan bisa kanta,kallo  Farko tayi musu ta Fahimci tsantsan wayewa tare da Hutawa atare dasu,wacce ke zaune gefen mai zaman banza ne,tacire wani babban glass wanda yakusa cinyema rabin fuskarta takalli Azeeza a karkace tace.

  “Ammr  don Allah baiwar Allah Tambaya muke? Da mamaki Azeeza ta tsaya tana gyara mataccen hijabin jikinta tana fadin”Toh Allah yasa na sani…”Kada kai tayi kafin tace”Gidan Su Captain Aliyu muke nema? Kur da ido Azeeza tayi musu tana kare musu kallo,lokaci daya zuciyarta da gangan jikinta suka bata Ni”ima ce,mirmishin Nasara ya subucemata kai tsaye tace

  “Wani Captain Aliyun? badai wanda ke aiki a barikin kaduna ba..? Saurin Amsamata Muneera tayi tana fadin”Yes Shikuwa don Allah ina ne inda mahaifiyarsa ke zaune..? Baya Azeeza taja tana nuna musu gidan goggo tada wuto tana fadin”Kun ma zo kan gaba ai ga gidan nan..’tafada tana wani mirmishi Waigawa sukayi Atare suna kallon gidan kan Munera tace”Ok tom mungode baiwar Allah…”Tafiya Azeema tafara tana fadin”Ah bakomai yiwa kaine..”Tafada tana kara Sauri ta Shige gida,Suko Ni”ima tayi Ribas suka koma gidan goggo dabaya baya,kafin kuma tayi kwana su Faka motar daidai kofar gidan,Dukkansu suka Firfito suna bin gidan da kallo,dama layin gabadaya Yamutsa Fuska munera tayi kafin tace”Tabdijam waima Ahaka wannan gidan shine Gra,Gaskiya na Raina samun Captain din naki..”

  Wani banzan kallo Ni”ima ta watsamata kafin tace”plz Sweetheart u better mind ur tok in bahaka ba zaki iya komawa gida nagode da taimakonki…”Kallonta Muneera tayi kafin tace”Au hakane toh Allah baki hakuri..”Daga haka taja bakinta ta Tsuke tana bin gidan da wani kallo,Ko kallonta Ni”ima batayi ba,Ta sanyama motar key din Rufewa kan Ta nufi gidansu Captain kai tsaye,bayanta Muneera tabi tana mamakin Soyayyar wahalar da Ni”ima take ma Captain,in don kyanshi ne akwai alot mazan da suke da kyau kuma suke hauka akanta buh ammh ita ta nacema Namiji kwara daya sai wahalar da ita yakeyi.

  

Goggo na cikin Daki ta hakimce Afalonta tana kallon Arewa Aminu shariff Momo,na gabatar da Shirin Sharhim Fina Finan mu,gurguru ne cikin wani dan Roba tana afawa abaki rabin hankalinta na wajen kallo,Taji ana ta sallama Daga dakin ta amsa tana mikewa,zanin leshin dake jikinta ta gyara kafin ta Daga labulen dakin tana Fadin”Wa”alaikas salam…”Tafada suna hada ido hudu da Ni”ima.

   Kallon Sama da kasa Goggo ke jifan Ni”ima dashi kafin tace”Daga ina bayin Allah…? Muneera dake bayan Ni”ima ta bayyana Fuskarta dauke da wannan Gilashin tace”Muna neman mahaifiyar captain Aliyu ne..? karkace kai goggo tayi tana fadin”Ayyah Gani,Ina Fatan lafiya ko? ta Fada tana kallon Ni’ima wacce kanta ke kasa,Mirmishi Muneera tayi kafin tace”Eh toh lafiya ba lafiya kawata ce tazo Rokonki wata alfarma..”Sakin labulen Goggo tayi tana fadin”Ku Shigo ku zauna,Allah yasa zan iyamata alfarma datazo roko..”Haka kurum goggo Ranta yabata Ni”ima ce,Duk da bata taba ko ganinta ba.

Suko ganin Farko Da sukayima goggo suka ga kamarta da captain duk da A fizgene yake kama da ita,Falon suka Shigo Kai tsaye Ni”ima tanemi waje ta zauna,itako Muneera tana ta karema falon kallo tana yatsina baki,Kafin ta nemi waje ta zauna,Kichen goggo ta Shiga Ta dauko musu Ruwa kafin tazo ta zauna tana fadin”ga Ruwa kusha..”Dan mirmishi Ni”ima tayi tana fadin”mungode goggo,munsha Ruwa..”Tafada tana sadda kanta kasa.

   Da ido Ni”ima tayi ta ma Muneera alamar tayi mgana,gyara zama tayi kafin tace”Sunana Muneera,ga Ni”ima nan Munzo rokonki alfarma ne Akan Don Allah kibama Captain hakuri yadawo ya Aureta wlh ba laifinta bane laifin Mahaifinta ne,kuma Shi yayi Nadama wannan karon bazai kara gaddama ba,Don Allah ki taimaketa Tunda Abun nan yafaru bata kara lafiya..”Tafada tana kallon kwayan idon goggo.

      Gyara zama goggo tayi tana fadin”Allah Sarki to ai ni bani da keda ikon zaban ma Gadanga Abunda yadace dashi ba,Da farko Shiya zaboki da kankishi don yana ganin kin dace da Ra”ayinshi,daga karshen mahaifinki ya hanasa ke,saboda wani dalili nasaa  mara tushe,toh barikiji na gayamiki koda gadanga bai yi Aure ba, ni mahaifiyarsa bazan taba bashi goyon bayan ya Aure ki ba,Saboda na nuna muku babu wanda aka haifa baida Uba,yanzu ku tashi kikoma wajen mahaifinki domin ni babu Abunda zanyi iya miki,Tunda haryanzu gadangar bai Kawo Asalin Uban nashi ba,ba Shi mahaifinki yace sai yakawo zai bashi ke ba.?.,”Tafada hankalinta kwance.

Tunda goggo Tafara mgana Idanuwan Ni”ima suka tara kwallah,tana gama mganar hawaye suka zubomata Mikewa goggo tayi tana fadin”Ngd ku gaida gida…”Daga haka tashige bedroom ranta bace,Muneera dake zaune ta mike ta isa ga Ni”ima tana rikota lokaci daya tana fadin”Kinji kingani ko? dama narigaya dana Fadamiki zamu wahalar da kanmu oya tashi mutafi…”Mikewa Ni’ima tayi tana kuka kamar ta Shide Hannunta muneera ta rike suka Fito daga dakin tana Fadin”Kinga ki cire Captain Aranki don ni banga alamun Nasara ba,Yadda yake baida Mutumci haka uwarsa take,gado yayi..”Tafada suna Ficewa daga gidan,Suna zuwa kofar gidan sukaci karo Da Azeeza jingine jikin motarsu tana kallonsu tana mirmishi,Cak suka  tsaya suna binta da kallon mamaki kusa dasu ta karisa tana fadin

  “Dama nasan bazakuyi Nasara ba,Don goggo bazata taba Sauraranku ba…”Kallon mamaki suka bita dashi kafin Ni”ima tace”Wacece ke? Mirmishin kasaita Azeeza tayi kafin tace”Sanin wacece ni bazai miki amfani ba,Abun da zaifi miki amfani Shine yadda zaki mallaki Abun Kaunarki Captain..”Zaro ido suka atare suna mata wani kallo ganin haka yasa ta juya tana fadin”Au naga baki Shirya ba,in kin Shirya kya nemeni,Sunana Azeeza…”Tana fadin Haka tafara Tafiya da hanzari Ni”ima tataka ta rikota tana fadin”Konawa kike bukata zan biyaki matukar zan mallaki Captain,..”Waigowa Azeeza tayi tana dariya kafin ta harde hannunuwanta akirji tana Fadin”Bada kudi nake so ki biyani ba,Zamu Taru ne mu Taimaki juna…”Da Hanzari Muneera tace”Kinga Baiwar go to d point,meke tafe dake.”Mele baki Azeeza tayi kafin Tace” _KI RABASHI DA MATARSHI AZEEMA NI KUMA NAYI MIKI ALQAWARIN MALLAKANSHI AMATSAYIN MIJINKI.._”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button