DUBAI PART 2

DUBAI PART 2

Kuka takeyi sosai tana juyi a cikin bargon tana ambaton ya Allah tare da danna qirjinta son Taheer qila ita kuma shine ajalinta, a galabaice ta miqe ta sauko tana dafa bango ta shiga bandaki ta kama ruwa ta dauro alwala tazo ta tayar da sallar azahar tana kuka tana fadawa Allah damuwarta.
Bayan ta idar ta dauki qur’ani data gani a gefe ajiye ta fara karantawa tanajin sassaucin nauyin da qirjinta yayi bayan ta idar ta daga hannunta tana kuka kunyar ubangijinta takeji ta kasa bude baki ta nemi yafiyarsa gani takeyi kamar bazai dubeta da idon rahmaba.

Amma data tuna Allah gafuru al rahim ne sai taji sanyi a ranta ta fara neman yafiyarsa da zuciya me tsarki ta jima tana Istigfari sannan ta rufe qur’anin ta koma ta kwanta tunanin baya yana dawo Mata da irin alqawurran da Taheer ya rinqa yimata lkcn da yana kwadayin jikinta.
Safnah tafi komai tsaya Mata a ranta tunanin kalmar da zata fadawa yarinyar lkcn data girma taji irin hanyar da sukabi suka samar da ita takeyi.
Toshe bakinta tayi da hannunta saboda ita kanta tagaji da kukan da takeyi so take ta saba da wannan rayuwar data samu kanta a ciki saboda tasan itace qaddararta, Addah ce ta shigo da waya a kare a kunnenta ta zauna kusa da ita ta dafata tace “na fada miki banson damuwar nan da kike sanyawa kanki Habbatullah muyi hqr komai yayi farko zaiyi qarshe ga yar uwarki zakuyi mgn”

Kara Mata tayi a kunneta tayi sallama da murya me rauni Fatima tace “Yaya Habeey ya jikinki ince dai kin warke?” Ajiyar numfashi tayi tace “gangar jikina ta warke amma zuciyata zafi takeyi Fatima nafi buqatar mutuwa akan wannan rayuwar da nakeyi mara albarka na rasa farin ciki ta ko ina…” Saurin katseta tayi da cewa “ki daina wannan zancen Yaya wata rana sai lbr don Allah kiyi hqr ki manta da wannan mayaudarin insha Allahu Allah zai saka miki”
Lumshe idonta tayi tace “don Allah Fatima ku dawo gda kada kiyi sha’awar yin rayuwa irin tawa babu komai a cikinta sai tozarci da qasqanci ki fito a kamoki ko ki bawa argent dinki number ta ya kirani na bashi kudinsa ku dawo mu nemawa rayuwarmu makoma, bana fatan rayuwarku ta lalace kamar tawa nikam nasan babuni babu farin ciki a rayuwata”

Jikin Fatima yayi sanyi matuqa sukayi sallama ta Addah ta dubeta ta kawar dakai tasani duk itace ta jefa rayuwar Habeey cikin wannan gararin, miqewa tayi a kasalce ta nufi nata dakin tana kukan zuci dana zahiri yarinyarta me biyayya dason faranta mata yau gata tana kuka saboda wasan da tayi da rayuwarta ta rabata da gatanta ta kawota ts hadata da muguwar rayuwar data zabawa kanta yanzu ta Yaya ma zata tunkari Salahu da mgnr wata ya dake tsakaninsu balle har ya karbeta ya a matsayin jininsa bayan an fada masa cewa cikin ya zube?
Hakanan suka yini a daki kowa zuciyarsa babu dadi sai yamma sannan Habeey ta qarfafa jikinta a qoqarinta na sanyawa kanta dangana da rungumar qaddararta ta fito tsakar gidan ta zauna Addah na gyaran kubewa ita kuma tana gyara Mata ganyen ugo saboda rashin wadataccen jinin da Habeey ke fama dashi shiyasa ta bayar aka siyoshi zatayi mata miya dashi.

Rayuwar Habeey da mahaifiyarta da yan’uwanta gwanin dadi cikin kwanaki ukun gata sosai suke nuna Mata basu barinta da damuwar komai ko yaushe cikin sanyata dariya suke, biye musu takeyi amma qasan zuciyarta ta kasa cire Taheer a cikinta kullum mafarkinta shine ko magana akayi mata wani lkcn shi take ambato.
Lamarin da yake damun Addah itadai da gaske batason ko wani abu daya shafi Taheer so takeyi ya fita cikin qaddarar yarta har cikin ranta dadi taji days karbi yarsa, cikin kwanaki ukun ne Addah tasa aka ciro Mata kudin da governor Waziri ya basu kudine ba kadan ba batare da kowa ya sani ba tasa aka nema mata babban gida na alfarma a cikin birnin gombe ta siya da sunan Habeey ta zuba musu komai na more rayuwa sauran ta dora jari sannan ta biyawa Habeey kudin wata babbar makarantar islamiyya.

Kwana daya suka qara sun gama shirinsu tsaf tace zasu rakata unguwa Habeey tana daki zaune tanata gwada wayar Taheer taqi tafiya sukaji sallamar mutane a tsakar gidan gaban Habeey ne ya fadi saboda tunaninta Dr Shattima ne saboda ya takura musu da ziyara cikin kwanakin nan.
Amsawa Idris da Ibrahim sukayi suka fita da sauri itama ta miqe ta fito sanye da hijjab dinta har qasa saboda dokace Addah ta sanya mata ta tsaya a bakin qofar dakin.
Shigowa sukayi ta dago kanta a dan tsorace saboda jin muryar Governor Waziri ta zuba masa ido gabanta na faduwa itadai kawai governor Waziri kama yake Mata da wani Wanda ta sani, a bayansa wasu mutum biyu ne sai Shattima dake biye dasu.

Janye idonta tayi dagakan governor Waziri ta saukeshi akan wanda yakebin bayansa shima ita yake kallo ga mamakinta sai taga kowa ya tsaya amma shi ya nufota tayi saurin rintse idonta kawai saijinta tayi a jikinsa ya rungumeta tsam ya fashe da kuka yana fadin.
“Itace wlh azeem Habbatullah yatace yayar Saudat ce Innanillahi wa innah ilaihirraji’un dama zanganta ashe mafarkina gaskiyane da yake nunamin zuwan wannan rikitaccen lkcn meyesa Yaya meyasa kuka boyemin bayan kunsan inda take meye yasa baka sanar dani ba Saida aka daura auren Taheer da Saudat”…………

UMMUH HAIRAN

[8/9, 4:08 PM] OPEN EYES MULTIMEDIA: HABEEYTAH
DUBAI PART 2

FAUZIYYA TASI’U UMAR
UMMUH HAIRAN

9

Zamewa tayi a jikin Alh Sahabi ta zube a qasa summamiya Taheer dake shigowa ya hankade governor Waziri dake riqeshi ya fada kanta ya dagota yana jijjigata yana Kiran sunanta kawai shima sai ya zame a kanta zuciyarsa na harbawa da sauri, a haka Saudat da Bushirah suka shigo suka samesu.
Saudat ta sulale qasa cikin kuka me gunji tace “ni dama tun ganina na farko da Habibah nasan akwai wani abu tsakanina da ita wlh na hqr da Yaya Taheer koda soyayyarsa zata kasheni Dad dama tun kafin nasan da wannan jumurdar ya sakeni saki uku minti uku bayan daura aurena dashi….”

Salati Dad ya saki cikin sarewa zuciya ya qarasa gabanta ya riqota yace Alh Sahabi ya sunkuya ya janye Taheer daga jikin Habeey yace “hakan yayimin dadi ya burgeni sosai Saudat yayi abinda ya dace dama bansan da cewa bashi ya amince da aurenki ba da tun farko bazaayi sa ba” Addah ce ta shigo daga maqota data shiga sallama ta tarar da gdan cike da mutane da sauri taja baya saboda hada idon da sukayi da Sahabi tace “Salahu!” Da qarfi tayi mgnr ya kawar dakai tare da cije lebansa ya kinkimi Habeey ya fice da ita ya sanyata a mota zuciyarsa na bugawa da qarfi Alh Aminu da governor Waziri sune suka fito da Taheer sai Kubrah da Bushirah da suka kamo Saudat da taketa gursheqen kukan rabuwa da masoyi tasan Koda Taheer bai yanke igiyoyin aurensa da aka daura awa da suka wucce akanta ba to bayyanar Habeey matsayin yayarta shaqiqiya uba daya zaisa ta janye ta sallama Mata Taheer domin tafita buqatarsa tasani Habeey tafita son Taheer kuma sunmafi dacewa da junansu kasantuwar jinin dake gudanawa a jikinsu ma iri dayane.

Wani babban asibiti dakenan cikin garin gombe suka nufa Abba gudu yakeyi kamar zai tashi sama saboda a yanzu ji yakeyi kamar mutuwar Habeey mutuwarsa ce, suna zuwa ya qara sunkutarta ya nufi cikin asibitin da ita ma’aikatan suna ganinsa suka rinqa darewa suna bashi guri kasancewar asibitin kansa mallakinsa ne.
Shiga yayi da ita dakin agajin gaggawa yasa aka kira masa likitocin shima ya cire babbar rigarsa suka baje fasaharsu wajen ceto rayuwar gudan jinin nasa daya dade yana mafarkinta ya dade yana ganin surarta a baccinsa wannan rans daxai tsaya gabanta yana qoqarin dawo Mata da rayuwarta da take qoqarin qwacewa ta dade tana zuwar masa a baccinsa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24Next page

Leave a Reply

Back to top button