HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 16-20

Farin ciki ne ya kama su Mamma suka hau murna, bata fuskantar komai, a daidai lokacin sakon sa ya shigo wayar ta, 

“Duba whatsapp dinki amarya tah.”

Da sauri ta shiga whatsapp din har ta mantawa bata kunna data ba ,kunnawa tayi messages din suka shigo tayi saurin bud’e nasa. Hotuna ne masu yawa, ta hau bud’e su tana kura idon ta, hoton farko ya saka numfashin ta tsayawa na dan sakanni

“Capt Muhammad Ahmad Santuraki.”

  

Yayi captioning hoton, yana sanye da nadi irin na sarauta, da kunnuwan sa guda biyu a sama da yake nuna yadda tsarin sarautar take, gaba daya gani tayi an sauya mata shi,shine sai wasu abubuwan da yawa da suka dauke ta zuwa wani tunani na baya tana kokarin alakanta abubuwan da tayi ta shakku akan sa. Kwanciyar fatar sa, da yadda yake magana yana bata mamaki matuka. 

   Sauran hotunan ta shiga bubbudewa, duk akwai shi aciki tare da manyan k’asar da ma ketare, hoton sa da Takawa da yadda Takawan ya rik’e shi says alot. Ji tayi gaba daya ya goge mata hadda, ya bar kanta blank bata ma san wanne irin tunani zatayi ba.

   Wasu mata ne suka dinga shigowa, wanda kana ganin su zaka san su din hadimai ne daga gidan sarauta, duk suka taru waje daya cikin girmamawa suka hau gabatar da kansu. 

   Kayan hannun su Mamma ta saka suka ajiye a gefe sannan ta aika wata bangaren Gaji akan wasu suzo a cikin dangin Abban, hakan ya bawa Iman damar sulalewa ta shige dakin Umma, sannan ta kira Ya Maryam ya waya tace dan Allah tazo dakin Umma. Sai gata tazo har da saurin ta, murna fal fuskar ta dan suma ba karamin mamaki suka shiga ba.

  Hotunan ta soma nuna mata, sannan ta hau mita kamar zatayi kuka, katse ta Ya Maryam tayi,

“Yarinya kad’an ma kika gani, sai kin ga uban lefen da aka kawo miki, wallahi Iman Allah ya baki miji, miji na kere sa’a me sonki tsakani da Allah, kinyi sa’a, halin ki ne ya jawo miki amma.”

“Amma me yasa zai rufe ni?”

“Haka tasa salon soyayyar yake, kin ganshi kuwa? Salo,aji kyau ga kudi.”

Turo baki Iman tayi, ta rasa me ma zatayi, Itace zata shiga gidan sarauta? Sarauta ma babba irin ta Kano? Katse mata tunani yayi da wani sakon nasa

“Meet me a seat room din Abba, na matsu na ganki, I want to feel you right close to me.”

Da sauri ta kife wayar,. Maryam da taga komai ta kyalkyale da dariya

“Su Iman an shiga sahun manya, jeki dan Allah yaji duminki, halal dinsa ce ke yanzu ehe.”

Duka ta kai wa Maryam din ta manta ma basa yar haka da ita, ta sake kwanshewa da dariya tana tsokanar ta

“Saura kije ki dinga wannan nuku nukun naki, tashi ki sake gyara jikin ki, bari naje na karasa jin drammer da ake a gidanku, Zeenat na chan ta tada aljanu wai ba ta yarda ba, kinsan an riga an daura itama.”

“Kamar ya?” Tace cikin mamaki

“Jeki ke dai wajen aikin Allah, bari zan baki labari in details.”

Ta juya da sauri ta fice bayan ta sanarwa da Mamma cewa Iman zata je yarima na seat room suyi hotunan tarihi.

  

Rano💕💕

#Note edited

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI’AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*

_1aHALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

1/21/22, 12:58 – Buhainat: Halin Girma

    18

Hafsat Rano

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

**************

Shigowa Mamma tayi, ta same ta a tsaye ta ma rasa abinda zatayi. Hannun ta, ta kama ta zaunar da ita, ta bud’e jakar da suka zo da ita ta ciro turare me dadin kamshi na daban ta fesa mata, ta duba fuskar ta sannan tace

“Ki kwantar da hankalin ki dan Allah,bari na duba kayan da yan matan nan suka kawo, ba za’a rasa alkyabba ba. ”

Fita tayi sai gata ta dawo tare da daya daga cikin yan matan, ta russuna har k’asa ta gaida Iman din da gabatar da kanta da sunan ta Ummimi sannan ta matsa daga gefe,

” Tashi ta taimaka miki ta saka miki. ”

Mamma tace tana murmushi, wani banbarakwai Iman taji, ta tashi cikin sanyin jiki yarinyar ta hau saka mata alkyabbar cikin k’warewa. Ji take tamkar mafarki, kamar zata farka taga komai yana yadda take. Har ta gama gyara mata, ta kawo sauran kayan ta sassaka mata ta fito sosai a gimbiyar ta mamaki be bar ta ba.

   

   Khadija da Zahra ne suka shigo, kusan sa’annin Iman din ne a family, doki ya saka su zuwa suka Iman din suma su bawa idon su abinci, suna shigowa dakin suka ganta cikin shigar da tayi masifar mata kyau, shigar alfarma.

   Hoto Zahra ta ciro waya ta hau daukar ta, kala kala har da videos dan dole ne yau followersa dinta na Instagram su kara kiyayarta.

   Kiran ta ya sake yi dan da gaske ya matsu ya ganta, irin matsuwar ba don idon sirikai ba, da dumbin jama’a da sai dai kawai ta ganshi a duk ma in da take.

   Mamma ce ta dakatar da hotunan haka, tace suyi mata rakiya zuwa in da Muhammad din yake, ko tace Yarima Muhammad dan sunan kam be chanchanci a dinga fadar sa haka nan kai tsaye ba.

    Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki, haka ta tashi tana turo baki. Tare suka fito da biyu daga cikin hadiman yan matan nan, suna daga bayan ta suna take mata baya, domin da gaske Ammi tayi musu gargadi akan surukarta ta, su kula da ita da komai nata

    Suna zuwa daf da seat room din suka soma jin hayaniyar maza,amma ba irin hayaniyar da zaka ji ba irin ta wasu mazan marasa aji da tsari. Hayaniya ce ta nuna farin cikin su da taya murna cikin ilimi da wayewa. Ji tayi kamar ta koma da baya, dan yadda ta tsani taro na maza har ya zama tana ciki, bata san kalar kunyar da zata sha ba, dan da alama dukkan su masu surutu ne. Bata dai ji muryar uban gayyar ba, ta kamo addu’a ta soma yi har ta samu nutswar ta 

“Iman.” Ya kirata yana karasowa wajen, tare suke da Habib da abokin sa Sadeeq. Murmushi tayi masa

“Uncle Khalil, ashe kazo.”

Murmushin yak’e ya maida mata, ya tuna da warning din da Moh ya kada masa, duk da yayi kokari matuka be saba ka’ida ba, yanzu ma dole ce ta sakashi zuwa tun da dai ba zai ki zuwa daurin auren Zeenat ba.

“Nazo Iman, Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya.”

“Amin.” 

Ta amsa a ciki tana jin babu dadi, lokaci daya yanayin sa ya sauya, yayi saurin barin wajen yana yin gaba, suka gaisa da Sadeeq da Ya Habib sannan suka wuce zuwa in da zasu.

   Sallama Ummimi tayi daga kofar, ta sanar da zuwan Iman din kamar yadda yake a tsarin masarauta, murmushi Moh yayi me aji, ya mike da kansa yana hararar su Ja’afar

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button