HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 16-20

Wani kallo tayi mata, kamar ma ta rufe ta da duka take ji

” Sai bayan an kai ta ya gark’ama mata ciki sannan ne kike tunanin zai rabu da ita? ”

” A ah Yaya, kinga wai ai dai yanzu daga daure aure yau ai ba za’a ce ya saketa ba, kinga hakan ai kema zai iya baki matsala da Dr. ”

” Matsala ta nawa kuma? Ni yanzu ya riga ya fita daga kaina, ta yata kawai nake, dole na bata farin ciki ko ta halin Kaka. ”

Shiru kawai Aunty Maimuna tayi dan ba kuma tasan yadda zatayi ta bawa Maman hakuri ba. Aunty Muhibba ce ta shigo, tace maman ta tashi ta gyara jikinta Iman da mijinta zasu shigo. Kamar ta danna ma Aunty Muhibban ashar taji dan dai akwai kunya tsakanin su kasancewar ta matar babban wansu, dole ta tashi ta wanko fuskar ta a bathroom ta shafa mai da yar hoda ta saka kwalli sannan ta fito.

***A zaune take ta tankwashe kafar ta akan dan carpet din da yake jikin gadon dakin, ranta a bace yake tun bayan da ta samu labarin auren da Yarima Muhammad zai, taso ta tada hankalin ta amma Kilishi ta hanata, yanzu gashi tana ji tana gani an daura.

  

“Laila!”

Ta kira sunanta tana daga zaune a gefen makeken gadon ta, da ido ta kalle ta ba tare da ta amsa ba, ta mike tsaye. Sanye take da doguwar gown ja, sai gashin ta da yake a tattare a waje daya da yasha gyara na musamman. 

“Yaushe zaki koma?” Ta ta da tambayar bayan tasan amsar da zata bata. Da ido ta sake dubanta, ranta na sake baci tace

“Na dawo kenan.”

Da sauri ta mike daga gishingid’ar da tayi, ta dauka zata ce mata soon zata koma kamar yadda take bata amsa a ko da yaushe idan tayi mata maganar komawar.

“Kinsan me kike cewa? Ba zaki koma ba? Me yasa?”

“Ba zan koma ba har sai na samu cikar burina. Ni ce na chanchanta da zama a wajen da aka bawa yar talakawa, wadda bata da komai da kowa. Yarima nawa ne ni kadai babu kuma wanda ya isa ya dakatar dani.”

“Har ni?” Tace tana zaro ido cikin mamaki

“Duk wanda yayi kokarin shiga hanya ta, ko waye kuwa, ko da Bubu ne!”

Tsam kilishi tayi a in da take tsaye ta kasa cewa komai. Tana son Laila tamkar yadda take son Kamal,sai da tafi son Kamal ya gaji ubansa akan yadda ita Lailan take so. Sai dai idan taga da gaske Kamal ba zai samu sarautar ba, toh zatayi duk yadda zatayi ta samu Laila ta shiga rayuwar Muhammad din. 

   Juyawa Lailan tayi cikin takun ta na isa, ta bar dakin. Da kallo Kilishi ta bita ta girgiza kai

“Ba zan taba barin ki da tsarin ki ba har sai na ga da gaske plan dina ba zai yiwu ba, wanda bani da shakku, Kamal shine zai gaji  ubansa a ranar da suka shirya bawa dan gatan dan nasu. Maimartaba da kansa zai yi fushi dashi, fushi irin wanda be taba yi ba!” 

Dariya ta saki ta koma ta zauna tana harda kafarta, indai tana numfashi Muhammad ba zai taba sarauta ba wannan alkawari ne da tayi wa kanta. 

****

    A gajiya Bubu ya dawo, shiyasa be samu ganin kowa ba ya shige turakarsa. Tun da wuri Ammi ta shirya tana jiran sa dama,aiko yana dawowa ta tafi dan tana so su karasa maganar da ya fara yi mata ranar basu samu damar gamawa ba

   Har ta karaso ta zauna be bar kallon ta ba, babu wani babban chanji akan sanin da yayi mata a dah da nayi yanzu, jikin ta me kyau ne zaka rantse bata ajiye garkamemen saurayi kamar Muhammad din ba.

“Barka da zuwa gimbiya a fad’ar Ahmadu.” 

Yayi mata kirarin da ya saba mata tun zamanin kuruciyar su. Dariya tayi ta zauna tana dora tray din da ta shigo dashi a saman table. 

“Sannu da zuwa, kun sha gajiya. An rabu da taro lafiya da kowa?”

“Lafiya Alhamdulillah, Takawa yayi matukar kokari sai dai muci Allah ya saka masa da alkhairi.”

“Ai dama yace shine uba, kuma shine kuma kaka, mu yan kallo ne kawai.”

Murmushi Bubu yayi yace

“Gaskiya kam ga zahiri nan mun gani ai.”

“Allah ya basu zaman lafiya, har na matsu su tawo nan wallahi.”

Hannu ya kai saman hancin ta ya lakace mata fuska yace

“Ko kunya, dan farin.”

“Kuma dan auta ba.”

Sai suka saka dariya a tare.

“Allah dai ya basu zaman lafiya da zuria dayyiba, kwanan nan zaki ga yan duguiw duguiw suna yawo a tsakiyar masarautar nan, lokacin na dawo gida nima na huta kamar Aji, kinga sai kawai na dinga kallon su ina jin dadi.”  

” Allahu ya sa, Allah ya nuna mana. ”

” Amin. ” Yace yana hasaso lokacin idan da rai da lafiya

” Ka gama yanke shawarar nad’in ranar juma’a din? ”

” Haka muka tsara da Aji kuma na sanar da Takawa shima yayi na’am da hakan. ”

” Kana ganin babu matsala? ”

Rik’e ta yayi a jikin sa, yasan me take tsoro take gudu kuma

” Babu komai in sha Allah, babu abinda zai faru. ”

” Aikin sa fa? ”

” Ajiye shi zai kinga ba zai yiwu a hada ba ai. ”

” Amma… ”

” Ki tayashi da addu’a har ma dani din ma, idan ban ajiye mulkin nan ba hankali na ba zai taba kwanciya ba. ”

” Allah ya nuna mana, Allah yasa ayi lafiya a gama lafiya. ”

” Yawwa ko kefa, addu’ar kenan. ”

#Rano💕

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI’AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

1/25/22, 10:41 – Buhainat: Halin Girma

      19

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

**************

Ta cikin ido Moh ya kalli Mama da ya lura kamar tsaiwar na neman gagarar ta tunda aka fara daukar hotunan, gashi sai dauka ake an ki dainawa itama a cikin yanayi take da saura kad’an ta zube a wajen idan aka cigaba da daukar hotunan. Sai da ya tabbatar da tayi masifar kaiwa karshe har tana neman fito da abinda yake zuciyar ta ne sannan yace ya isa haka, tayi saurin fadawa daki babu ko magana, hannun Iman din ya kama a gaban kowa, suka juya suka bar part din yana jin a kalla Mama zata yi hankali, a kalla zata san rayuwa da yadda take juya wa bawa.

    Tafiya sukayi bayan sun yi sallama akan zuwa magriba za’a zo a dauki Iman din. Sake chanja kaya tayi zuwa wasu kayan na daban, suka zauna cikin yan mata da sauran yayan da aka ma aure a family aka dinga hira cikin farin ciki. Bata saka musu baki sai dai tayi murmushi musamamn da ya zama kusan rabin maganar akan zaman aure ne wanda take jin kamar wasu maganganun sun girmi kanta.

   Gabatowar la’asar ya sake saka Iman din a cikin yanayi fargaba, irin wanda ake ji idan za’a rabu da gida. Tashi tayi ta ja Khadija suka fita zuwa shashen su, tana son ganin Zeenat sannan tana son daukar wasu abubuwan a dakin su.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button