HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 16-20

“Amaryata tazo dan Allah muna bukatar privacy.”

Dariya suka kwashe gaba daya, ya hade rai da gaske ba da wasa ba,su ka hau tsokanar sa amma yayi fumfurus yace wallahi sai sun fita. Musaddik ne yace

“Ai ka bari ta shigo mu gaisa ko? Sai mu fita daga baya.”

Da kai ya amsa ya koma ya zauna yana jin rawanin da ke kansa ya soma gundurar sa. Shigowa sukayi bayan sun saka Iman din a tsakiya, idanun ta da tayi kokarin saukar dasu k’asa sosai suka shiga cikin nasa, da sauri ta dauke idon ta, ta zauna su Zahra suka sakata a tsakiya. Gaishe su sukayi suma suka amsa sannan suka gaisa da Iman din da take amsa musu ciki ciki dan ji take kamar ace fit ta fice saboda tsoro.

“Capt. Lets snap please.” 

Wani abokin sa Gbenga yace yana kallon sa

“Ok sir.” Yace yana tashi, taimaka mata Zahra tayi, ta isa wajen da yake a tsaye, daga gefen sa ta tsaya, sai taji kamar ana saka abu ana bubbuge mata kafafunta. Hannun ta taji yana laluba ta cikin babbar rigarsa, ta daga kai da nufin kallon sa, shima a lokacin kallon ta yake, Ja’afar yayi sauri ya dauki scene din, hoton yayi masifar kyau, duk suka hau yabawa.

   Masifaffiyar kunyar da take ji ta hanata sakewa sam, duk da haka an dauki hotunan sosai sun fita, banda camera man suma wayoyin su duk babu na banza. 

   Wani irin laushi hannun sa da yake cikin nata taji,ta tuna kullum cikin safar hannu yake zuwa mata, duk sanda zata ganshi hannun sa da kafar sa, na sakaye, sai yanzu ta gani dalilin nasa na yin hakan.

  Mammatsa mata hannun ya dinga yi, ya hanata sakat ya sakata a  wani irin yanayi me wuyar fassarawa, gashi ya saka shi cikin rigar yadda ba wani wanda zai lura, sai da aka gama hotunan tas sannan suka fita suka barsu da nufin idan sun gama gaisawa sai su fito a shiga cikin gidajen ayi sauran hotunan a cewar Musaddik.

   Kamar me jiran kiris kuwa, suna gama ficewa ya saka dukkan karfin sa, yayi hugging dinta kamkam yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. 

   

“Alhamdulillah.” Ya furta yana murmushi

“Mrs Muhammad Ahmad Santuraki.”

Ya rada mata a kunnenta, ture shi tayi tana turo bakin ta gaba, ya tsaya yana kallon ta dan be taba sanin ta iya shagwaba ba sai yanzu

“Me yasa kayi haka?” 

Tace cikin dan daga murya ita a dole ya bata mata rai, riko ta yayi da sauri ya dora hannun sa akan lips dinsa yace

“Shssh… Ba’a dagawa miji murya babu kyau.”

Kokarin ture shin ta cigaba da yi amma sam ya hanata damar hakan, sai ma sake manne ta da yayi sosai da jikin sa suna shakar kamshin juna. Luf tayi ta daina motsawa kowa na sauraron bugun zuciyar dan uwan sa. Wajen minti daya suna a haka kafin ya saketa yana jan ta suka zauna a saman kujerar, ya rik’e hannayen ta yana kallon cikin idanunta 

“I promise you ba abinda kike tunani bane, zan miki bayanin komai amma ba yanzu ba, yau ranar farin ciki ce, let’s not discuss duk wani abu da be shafi ranar ba kinji matata? ”

Turo bakin ta sake yi, ya saka hannu ya shafa yana murmushi

” I love that. ” Saurin rufe fuskar ta tayi kunya na kamata

” Itama kunyar duk ina so, komai ma ni so nake kinji? Amma dai ki ajiye mana zuwa sanda zamu tare a gidan mu, ko nawa ne zan biya na siya. Bana so a samu matsala dan zai iya yin abinda ban shirya ba. ”

Da sauri ta gyara bakin ta, ta kuma gyara zama tana matsawa kadan, matsowa yayi ta sake matsawa ya sake matsowa kafin ta samu damar sake matsawa ya saka hannu ya tokare ta, ya matso da fuskar sa daf da tata, tayi saurin runtse idon ta tana jin kamar zata saki fitsari. Light kiss taji yayi mata a saman idonta dake a rufe.

    A hankali ta bud’e idon ta, tayi saurin rufewa ganin yadda nasa ya sauya sosai.

” Amm.. amm muje kaga su Mamma da yan uwan mummy, sai Gaji da sauran yan uwan Abba ko? ”

” Hmm. ” Yace yana jan ajiyar zuciya

” Tohm bari na kira Musaddik yazo. ”

Tashi yayi tsaye, ita kuma ta dukar da kanta k’asa, murmushi ta samu kanta da yi, tayi saurin katse shi ta sake saukar da kanta dan kar ya gani.

Dawowa su Musaddik sukayi, su Zahra da aka samu sabbin samari suka shiga ciki don sanar da shigowar su Mubamamd din.

   Ta bangaren Gaji aka fara, akayi hotuna sosai da kowa da kowa, sannan aka dawo in da su Mamma suke nan ma akayi musu, sai sauran mstan gidan da jikoki da sauran yan uwa da abokan arziki har ma da makwafta da suka shigo ganin kwaf.

   

***Yadda Zeenat ta koma zaka rantse tayi shekara tana jinya, gyaran gashin ma da aka yi duk ya hargitse kamar ba’a yi ba, ta tada aljanu yafi kala biyar duk da muryoyi kala kala akan suns gargadin in dai aka sake aka kai ta gidan sai sun kashe ta.

   Ko da Mama ta kira Abba ta fad’a masa cewa yayi karya ne, ya kashe kiran dan yana cikin mutane ne, amma kuma sai ya dinga jin babu dadi yana kuma tausayawa Zeenat din sosai, amma ya zai yi? Su suka jawa kansu duk da ba irin muna musu da be yi ba.

   Kayan kitchen su Aunty Maimuna suka dauka, suka kira Bashir din dan ba ma a samu damar zuwa an yi jeren kitchen din ba. Cewa yayi zai aiko a tafi dasu, ba’a dade ba kuwa sai ga wani saurayi yazo a golf irin ta hayar nan, dole suka saka Habib bin bayan su da wasu kayan bayan ya dauko yar kurkura dan yawan kayan kadai sun isa a yiwa wasu amaren biyu amfani dasu bayan Zeenatun.

   Sanda suka shigo unguwar gaban kowa ya hau faduwa, basu gama shiga masifa ba sai da suka ga kofar gidan da aka tsaida, katuwar kwatar dake kwance a kofar gidan ce ta fara tsorata su. Haka suka daure suka fito ya bud’e musu gidan suka shiga.

   Babban tashin hankali sanda suka shiga gidan suka tarar da kayan da suke gidan da Bashir din yace ya saka mata kaya kar ayi komai, su kansu kujerun bayan yadda aka daina yayin su, ba set bane dan babu three seater ko kankantar falon ya hanata shiga ko kuma ba’a yi da ita ba oho.

   Sanda suka shiga kitchen din sai da suka kusa kurma ihu, kwatan kwatan abinda Maman ta siya ba zai shiga kitchen din ba. Babu wanda yake wa wani magana a cikin su, suka saka abinda zai iya shiga kitchen din da ko kitchen cabinets babu, sauran na amfanin suka saka mata a cikin sip dan wannan ba za’a kirashi da wardrobe ba sai da sip😢😂 ragowar kayan suka juya dasu cike da tunanin yadda za’a kare da Mama. Babu maganar uban kayan turaren wutar da ta siya wajen hadaddiyar me turaren wutar nan*yerwa incense and more.*

     Shigowar su kenan suka tarar ana ta hotuna da Iman, jiki a sanyaye suka wuce bangaren Maman suna taraddadin yadda za’a kwashe. Mama ma jin ance sun dawo ta yi zumbur ta tashi, sai dai tun kan su gama zama ta san da matsala.

   Aunty Maimuna ce ta jata daki tayi mata bayanin komai sai ragowar kayan da tace an loda su a motar Aunty Muhibba dan kar a shigo dasu saboda yan saka ido.

   A k’asa dirshan ta zauna, ta cire dan kwalin ta da take jin yayi mata nauyin gaske saboda yadda kanta ke masifar sarawa

“Amma Bashir ya cuce mu, ya cuci rayuwata, yanxu dan Allah wannan abun kunya da me yayi kama? Na shiga uku.”

Ta jefar da hannun ta gefe,

“Be kyauta ba gaskiya, ha’inci ne wannan kuma, sam be kyauta ba.”

Aunty Maimuna dake kokarin bata baki ta fad’a duk babu dadi

” Allah ya isa ban yafe ba wallahi,shege macuci. ”

“Kiyi hakuri Yaya Hajara, cuta dai Bashir ya riga yayi mana ita sai dai muyi hakuri, mu lallaba a kai ta idan yaso daga baya idan hankalin kowa ya dauke sai musan abinda ya kamata. “

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button