HALIN GIRMA COMPLETE HAUSA NOVEL

HALIN GIRMA 16-20

   

***Text message ne ya shigo wayar Bashir din, ya duba yana sauri sauri dan yana so yaga Moh kafin tafiyar da zai yi, 

_”Ina jiran ka kaida kanwar tawa a gida, na saka an gyara muku daya daga cikin dakunan nan. Sai kunzo.” _

Gaban sa ne yayi mummunar faduwa, yayi sakale rik’e da wayar yana tunanin mafita, be shi da niyyar hada Zeenat da Hajiya Layuza gida daya, amma kuma be isa ya ki kai ta ba dan komai zai iya faruwa. Kiran ganin sa Ghali yayi ya tabbatar da sun karasa, yace idan kafa ta dauke ya kirashi ya sanar masa. Yana kashewa yayi mata reply da an gama hajjaju sannan ya saka wayar a aljihu ya fita yana sauri 

    Yadda dakunan suke kananu ya saka gidan ya chunkushe, kowa so yake yaga abinda zai samu na dorarwa a gaba, masu bud’e kitchen masu bud’e toilet har da masu bud’e rijiya dan tabbatar wa.

    Aunty Maimuna ce tace kowa ya fita za’a koma gida saboda zuwa kai Iman, mutane suka hau saurin fita dan kowa ta kama motar da taxo amma suna fita suka ga wayam babu ko mota daya duk sun gudu,. Nan fa waje ya rude kowa ya hau tofa albarkacin bakin sa, yan uwan Mama suka shiga tashin hankali dan babu abinda yafi ciwo a debo mata a kawo su gidan amarya a watsar dasu, komawa cikin sukayi aka tilastawa Zeenat kiran Bashir din, be daga ba har aka gaji da kiran sa suka hakura suka fita, aka fara tunanin yadda za’a yi kowa ya koma gida.. saukin ta ma dama duk cikn garin ne dan tuni wasu ma sun dade da tafiya sun tari napep. Wanda suka rage ne dole su Aunty Maimuna suka san yadda sukayi kowa ta samu abin hawa. Sai yada habaici da bakar magana suke musamman yan uwan Abba da Mama ta bata wa rai tun a farkon fara bikin.

   Sanda suka gama dawowa gida magriba ta kawo kai, a lokacin ne kuma motocin masarauta suke jere kansu a cikin layin wanda ya kasance tun daga farkon layin har karshen sa. Motar da za’a dau amarya daban take ta gaji da haduwa, anyi decorating dinta tayi kyau. 

   

Gashi nan na biya bashin na ranar Friday. 

   

#Rano💕

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI’AR ZUCIYA_

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

*_Zaku tura kudin a_*

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

08184017082

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

09134848107

1/25/22, 10:41 – Buhainat: Halin Girma

      20

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

**************

Gaban Iman din ne ya dinga faduwa sanda taji tashin algaita da bud’a a lokaci daya, rik’e hannun Mamma tayi tamau bayan sun dawo daga wajen su Abba da wajen Gaji. Zaunar da ita Mamman tayi tace tana zuwa Amaani tayi saurin dawowa ta manne kusa da ita hakan ya saka ta dan ji dama dama. Mukullin motar da Abba ya damka mata a hannun ta da wasu abubuwan ya sakata shiga yanayin da ta shiga, har yanzu bata bar mamakin yadda abubuwan suka sauya salo ba, wanda bata taba tunani ko hasashen hakan zai faru da ita ba.

    Bayan kamar minti biyar sai ga Mamma nan ta dawo ta kalli sauran tace

“Matar nan bata da kirki sam, bansan me yake damunta ba, amma ni dai na fad’a mata lallai ta shirya tazo ta kai Iman dakin ta, idan ma wani abun ne yake damun ta ko hassadace ita ta sani, na dai bata girmanta.”

“Toh ai Mamma kina gani kinsan bakin ciki take, dama kin kyale ta kawai mu kadai mun isa.”

“Ai ba haka ake ba, mu muka zo muka same ta kuma duk tsiya dai itace marikiyar Iman din.”

” Toh yanzu zata je din ko yaya?”

” Ban san mata ba wallahi, na dai fita ai ni dai,ruwanta taje ruwanta taki zuwa, babu abinda za’a fasa.”

” Wallahi kuwa, Allah ya kyauta.”

” Amin.” Tace tana zama.

     Kayan Iman din aka gama fitarwa, aka saka a booth din motocin, sannan suka shigo da kansu su uku, suka ce sun zo daukar amaryar su, akayi barkwanci dai tsakanin su da su Mamma sannan suka fita su kuma su Mamma suka fito da Iman din.

    A harabar gidan suka hadu da Mama, ta yafa mayafi ita da Aunty Muhibba, kallo daya Mamma tayi mata ta dauke kai suka fice, bayan su suka bi, suka tarar an gama tsara mutanen kowa ta samu mota ta shiga, kowacce mota da kayyadadden mutanen da za’a saka kuma kowa ya samu an shirya komai yadda ya kamata.

   Motar amarya ce kawai ta rage sai guda daya da tazo a karshe, wasu ne suka shiga dayar tare da Aunty Muhibban sai Mamma da Mama suka shiga ta amarya suka sakata a tsakiya kamar yadda ake yi. Chan jikin kofar motar Mama ta makale taki yarda ta rabi Iman din, jawo ta sosai Mamma tayi jikin ta ta dora kan Iman din a saman kafadarta ta kwanta sosai. 

    Lamido Crescent suka nufa in da nan ne ainihin gidan Iman din, sojojin da ke zube birjik a gaban gidan ya saka mutane sake jinjina lallai Babba ne Muhammad din, gida ne hadadden gaske wanda dama chan a nan Muhammad din yake amma an masa gyara sosai da ba zaka taba cewa ba a lokacin aka gina shi ba. Tsaruwar gidan da yadda aka kawata faluka da dakunan gidan da kaya na alfarma ya kusan saka Mama shan k’asa, ta rik’e hannun Aunty Muhibba dan da gaske ta tsorata da yadda taga gidan. Falo biyu ne daya sama daya k’asa sai dakuna biyu a sama, uku a k’asa kuma kowanne Masha Allah kaya ne aka zuba na alfarma, kar Azo batun kitchen wanda duk yadda Mama ta kai ga kure siyayyar ta sai taga ta raina kanta, komai na ciki unique ne ga wasu shegun electronics wasu ma bata san menene amfanin su ba. A daddafe ta daure ta shiga ko ina dan yadda kowa ya zura ido a kanta kowa so yake ya ga yadda zata shiga dimuwa ko ma ta kasa rik’e bakin cikin ta har ta nuna a samu abin fad’a.

   Basu wani jima a gidan ba suka fito, dama saboda dai su san gidan Iman din tunda yanzu ba anan za’a fara kaita ba, masarauta zash dan suna da shagalin bikin da zasuyi su ma.

    Kin yarda Mama tayi ta koma motar amarya ta fad’a wajen Aunty Muhibba dan komai zai iya faruwa idan ta zauna gata ga Iman din. Bata taba tunanin kalar wannan daukakar ga Iman din ba. Sai gashi in da Iman din taje ko zata je nan gaba bata isa ta taba kai wa wajen ba har abadah. Tayi mata nisan da za’a iya cewa ya kai tsakanin nisan sama da kasa.

    Bata kara raina kanta ba sai da ta gansu a cikin masarautar, babbar masarauta irin ta Kano, da bata kawo kanta a ciki ko da wucewa tazo yi kuwa bata taba hasashen kasancewar ta ba.

    Wani tsari akayi na tarbar su, wanda ya sake bawa mutane mamaki, kana kallon fuskokin kowa zaka tabbatar da yadda suke ciki. Sanda suka isa bangaren Fulani kakar Moh din da kanta ta taso ta rungume Iman a jikinta, ta kuma zaunar da ita a kusa da ita, jikokin ta sauran suka hau dariya suna tsokanar ta, ta biye musu suka dinga yi kamar ba matar sarki ba,  duk da ba kowa ne aka bari ya shiga wajen ba, iya makusantan Iman din ne daga Mamma sai Mama sai dangin Abba su biyu sai Amaani da take makale da Iman din, sauran mutanen a wani babban falo aka ajiye su aka shiga gabatar musu da nau’ikan abinci kala-kala na gida dana kasashen ketare.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button