KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Washe gari har 9am ko farkawa basuyi ba,ita dai Umma tana ta tunani domin jiya da dare tana Jin kwarafniyar da sukeyi da ruwa da botiki tare da bude kofa da rufewa.
  Salma ce ta fara tashi tayi Sauri tayi Brush da wanka tayo Alwala sannan ta tashi Na'im ya shiga wanka ta fara  Sallah,ta idar tayi azkhar shima tuni yayi Sallah bayan ya fito daga wanka da Brush,Suna ta Azkhar dinsu suka gama,sannan ya shirya fes cikin yadi dinkin da suka kai da Salma wanda suka kashewa Malam kudi,bari naje na gaida su Umma Baby,Salma tace ina kwana ?kin tashi lfy my heart?,tace lfy lau tana murmushi,yace ina zuwa,yana fita ta Mike bata shirya ba ta share gidanta wanda yasha siminti ko ina,ta wanke tsakar gida,ta wanke toilet fes ta kunna turaren wuta,ta dawo kitchen ta fito tayi wanke wanke tsab ta gyara komai na kitchen fes,ta koma Rooms dinsu biyu tayi shara da goge goge ta gyara gadonsu daf,sannan ta fesa Room freshener da turaren tsinke ta kunansu da yawa, gida ya dau haske da kyau,wanka ta sake sannan ta shirya cikin Atamfa baka da Golden color,kayan sun mata kyau,kamar yaune party tasha kyau,tana gama fesa turare sai ga Na'im dauke da flasks uku na abinci,ya kalleta sosai tare da ajiye abincin ya rungumeta yana rada mata kinfi ko yaushe kyau,gaskiya da gani jiya kinji dadi har kyau kika kara,fuskarta ta boye a kirjinsa tare da cewa kai ai ka fini kyau yau kaga kuwa ka fini jin dadi,anjima za a kara yi ko?Salma a kunyace tace ae,bari naje na gaishe dasu Umma na dawo,to amma kiyi Sauri Malam ma ya fita baya gida Ashe.

  Tsakar gidan Salma ta fita fes Umma har ta gama komai tana karasa dan gyara inda basu gyara ba,Anty Rukayya ma ta hada kayanta zata tafi yau,Har Kasa Salma ta gaisar da Umma tare da Anty Rukayya,Umma tasha mamaki ganin Salma fes duk matsuwar da Na'im yayi akan Iskanci ace jiya Bai mata komai ba,to ko gajiyar biki ce?ko kuma Salma ta taba aure baza taji komai ba oho,Umma dai tayi shuru tace Salma amma Kin gyara wajen naki ko?ae na gyara nayi komai shi yasa ma na Dade ban zo ba,to dan Allah Salma banda gardama ayiwa miji biyayya ko me yace indai Bana sabon Allah bane kiyi kinji? Salma tace to insha'allah Umma,Malam ya fita Ashe,ae tun safe yana da ayyuka ne,Allah dawo dashi Lfy,Ameen.
Anty Rukayya tace to ni zan tafi nayi Sallama da Muhd sai kuma na sake dawowa ko kinzo gidana Amarya,Salma tana dariya tace to Anty Rukayya Ki gai da gida mun gode,Rukayya tace yar duniya Umma jibi wannan uwar daukan wanka kamar baza a mutu ba anyiwa miji,Salma ta rufe ido da tafin hannu tana dariya,Umma tace ina ruwanki da sa Ido ke bakya yiwa naki,Salma kyaleta jeki Ku karya kar yunwa ta kama Muhd.

  Salma ta wuce cikin wajen ta masa Sallama yana Palo yana ta Searching yanda ake Romancing mace yana karantawa,Salma Saman carpet ta zauna tace bari mu gani me aka dafa mana,tana bude flask taga farfesun kayan ciki,daya kuma flask din na ruwan Zafi kunun gyada ne daya kuma kosai ne,Salma tace ka gani nasan ma kafin son Kunun gyada da tea ko?idan kuma zaka Sha tea sai naje na daura,sha zamanki wannan ya isa Allah ya sakawa Umma da Alkhairi,Salma tace Ameen ni banda ni? Yace harda ke ma to,a plate daya ta zuba musu,tace to yau dai ni zan baka a baki,Ya zauna tana bashi itama tana cin,Salma tace yanzu zamu fara baki masu ganin daki nasan su Jamila ma zasu zo,Na'im yace ashe watarana zan koresu kuwa idan na gaji,ni baza a dinga takuramin ana shiga hakkina ba,Salma tace kawayen nawa zaka kora,ai ba haka kawai zan koresu amma suna min shirme zaki gani da Kansu zasu rage zuwa,kalli yanda sukeyi kullum sai an zo wajen mutum haka naga sunayi a garin nan,Salma tace ai ni basu sanni ba suna zuwa zasu tafi.
Sun gama cin abinci ta wanke kwanikan ta kaiwa Umma ta dawo,Na'im yace Muje to saman Bed yau sai ki bani Labarin Kawayen naki,Salma ta dinga murna,suka koma saman Bed,yace shi kam yau shine zai kwanta a jikinta,Tace to kwanta jikinsa yana Saman bed kansa ya daura a dukiyar Fulaninta,tace a nan zaka kwanta?yace ai yafi ko ina laushi,Salma dai ta hakura tana bashi labarin su Zainura masu gwada tafiyarsa, Na'im yace ai nasan yarinyar abinda ma tazo tayi min magana,Salma tace me tace?yace zuwa tayi kusa dani tace Angon Salmaaaaa?nace na'am tace wlh Amaryarka tana can tasha wanka kayanku iri daya kamar India haka take,Salma ta dinga dariya tace me kace mata to? Haka nace Dan Allah?tace Yasin,nace to zanzo na ga abata.
Salma tace shi yasa ta iya gwada maganarga, Na'im yace tayi dai shirme har wani iya acting dina zata yi,bari suzo ka zauna a Bedroom ni kuma zan fita Palo wajensu zaka ji hirarsu kaf,sai ka so suzo gidan nan,Na'im yana goga kansa a dukiyar fulanin Salma, tana shafa masa gashinsa suna more juna sama sama kawai suka ji Sallamar su Zainura sunzo ganin Amarya,a ka'ida a kauyen da sassafe ma suke zuwa washe garin kai Amarya suje susha dariya suyi kallon tafiyar Amarya,suga anyi ko ba ayi ba,sannan suyi  shara da wasu ayyukan susha Hira su tafi,to Salma ba yar garinsu bace ba kuma Kawarsu ba shi yasa sai yanzu wurin 11am suka gaishe da Umma suka fada wajen Salma,suka ji gida yana kamshi ko ina fes dashi,Zainab tace uhmmm wannan waye yayi mata sharar ko Umma ce? Hadiza  ce tace kuyi shuru karfa Ango yana ciki Muzo mu ganowa kanmu,Wajen su takwas ne suka zo,Sallama suka kara yi sau nawa Sannan Salma ta fito kanta ba dankwali duk gashin ya hargitse zip din rigarta a bude,da fara'a Salma tace sannunku da zuwa Ku shigo mana kun wani tsaya a waje ai baya nan,Zainura tace too Alhmdllh har zan saki layi na tuna da Ango amma tunda baya nan an gama zauna na tambayeki kuma ni ban yarda baya nan ba,danmu ba mahaukata bane Mu ganki zii din riga a zuge,gashi a hargitse,Jamila tace mu dai baza mu fasa hirarmu ba wlh ko yana ciki idan tafi karfinsa ya fita,

Salma tayi dariya tace yana nan to,sukace Ahab ai mun sani,Barira tace to ya muka ganki ras ne wai? Salma tace ya kuke so ku ganni? Rahmatu tace wannan gyaran gida haka da kwalliya cab dan Allah Zahra’u idan a garin nan yarinya take kin taba ganin wacce muka je da safe tayi shara da gyara haka bare kiji kamshi?Zahra’u tace Sabo ma kike yasin babu sai ka ganta kamar daga bakin Kura aka kwatota.
Zainura tace a dinga rage Murya kasa,Yanzu Amarya ina ragowar kazar jiya?Salma ta Mike ta tafi kitchen Zainura tace kai wannan wise ce Alquran kalli da yan garin nan ne da tuni sun fara bamu labari,amma ita ta share zancen,ga gida yaci Uban gyara,Zainab tace kwalliyar ce ni take birgeni,
Salma ta kawo musu rabin kaza cikin wacce ta ajiye jiya tace gata amma fa da Sanyi,Zainura tace ah ai ko kankara ce nan suka cinye kaza tas suna hira,Salma tace ya gajiya? jamila tace tabi lfy yasin tuni,
Kai rawar Dan Dini na tuna jiya wlh cewar Zainab,suka sheke da dariya,Zahrau tace ai kwai jaki a nan wai shi fa ya birge,Jamila tace harda kwama bakin glass na masu walda, Barira tace Zainura ya Iron gidan Iya me Waina jiya,Zainura ta Mike tana dariya tace ai ba karamin dabba bane Iro Rawa kamar yana ebo ruwa a Rijiya,shegiyar kafada kamar Allo,Hhhh suka dinga dariya harda Jamila tace wlh da za ayi rubutu a kirjin Iro ko gargada baza a samu ba,Zainura ta fara gwadawa suna ta dariya,Na’im shi kanshi tun baya sauraransu har ya koma ji yana dariya,
Zainura dan Allah yan garin nan suna kwalliya da safe?Zainura tace ina fa zasuyi balagaggu ai sai dai kiga zani nan miya can kanzon shinkafa nan manja, kirji duk kirci.,haka Ummanmu takeyi cewar Zahra’u bazan boye ba haka Ummanmu take,Nononta wlh kamar gugan roba talau dashi,ta sakeshi yarab,nace haba dan Allah Umma abu kamar tsohon takalmi,tace dan Ubanki shi kika Sha kika girma,Zainura ta kyalkyale da dariya tace Allah yasa na Babarmu kamar kwallon goruba yake bashi da girma kuma ita na gado heeeee sukayi shewa,Barira tace Yasin bazan boye ba na Baba ta kamar botiki dan Dari uku da hamsim ga girma ga kauri sama dangangan kasanta tsilili ta karasa da dariya tace wlh gwara da Allah yasa na yo suffar Babanmu,

Nan ma suka sheke da dariya,Zainura tace ai Barira babarku batayi ba wlh ga masifa Yasin,Zainab ta rare makogwaro tare da yin tafi tace To ni dai Na tsohuwata gashi nan kamar Wainar flour labebe ni kullum idan tana shafa mai billahuwallazi Rahamanu dariya nake Alquran sai dai taji haushi,Baba yana kallo na rannan yace dan ubanki kin haukacene?a raina nace Allah sarki Baba ba wayo da zai gane da yayi Amarya ya samu me taushi,Jamila tace ke baza ki taya uwarki kishi ba? Kishin me?ni yayi Amaryarsa ba ruwana Alquran.
Jamila da Rahmatu sukace ai ko mu baza mu fadi na iyayenmu ba mun San darajarsu,Zainab tace kan Uba to uban waye Bai San darajar nasa ba abinda ke Jamila waye Bai San taki ba yanzu babu ko daya a kirjinta ya kare sai kansa kawai kamar Dan Kulikuli karami,Zainura tace Ita Rahmatu Na Babarta me kirar sinasir suka dinga dariya kuwa.

 Zainura tace kai Ku tashi mu tafi mijinta yana ciki bamu sani ba ko mun shigar masa lokaci Salma tace kuyi zamanku muyi hira mana bacci yake,Zainura ta kalli Zainab ya akayine ta Usaini me agwalima? Zainab ta bata rai tare da cewa me zanci da wannan hakori kamar katangar kashi, Jamila tace kai kuzo mu tafi nifa na fara abin yau,suka ce inye kinji dadi yau ba Sallah kenan ba salati a arniyarki kike.

Allah sarki Zainura Naji tausayinki rannan a gona kika baci,Zainura ta rike haba tace na shigesu bakya mantuwa aiko mun hadu da Lawandi yaganni a zaune naki tashi lokacin kun tafi dauko min kaya zan canja dan iskan bawa yace dole sai na tashi tsaye,nace bazan tashi ba yace wlh sai na tashi ya ganni kamar bani da lfy?nace kalau nake amma dan Iska yaki yarda,wai ya miko min hannu taso na rakaki gida,in fada muku nayi kamar zan mika masa hannun na kwanya masa mintsini,sai ya janye ba shiri kunji hannunsa kuwa?ai Alquran kamar jikin bishiya kaushi da tauri,kai lawandi yana fama da kazanta bayin Allah.
Zainab tace ina kika bar yusha’u me tantan,na tabbata da za a duba hammatar yusha’u to sai an ga gansakuka koriya a ciki,Zainura tana dariya tace na taba ganin hammatarsa yana wanki a gidansu wlh idan kin gashi sai ki rantse Allurai aka caccaka a Mike cako cako masu tsayi,hhhhhh suka dinga dariya Jamila tace ko ba ranar da muka shiga gidansu ba gumi yana ta Shar yana wanki,Harda kallon Zainura yaga yar fara ya washe baki kamar mangalar jaki yace Zainura ana ta yan matan ci?Zainura tace kin manta yace mata Mata mutanenmu Zainura Zainura na dallawa shege harara amma ko a sai lashe harshe yake,yo na taba ganin maye irin wannan ni.

Barira tana dariya tace to Amarya zamu wuce koma aci gaba da Gabatar da darikar kwana ba wando mu kuma sai watarana idan Allah yaso zaki ganmu katsam munzo.

Salma sai dariyar hirar take Take tace to Allah kaimu nima zanzo watarana,Zainura tace wanne zuwa ai ke kam yanzu darajarki ta Karu sai dai Muzo amma idan kinzo din zamu ji dadi,Sai anjima dan Allah idan ya farka kice ina gaida me kyau na duniya cewar Zainura,Salma tace to zaiji,kice gaskiya nace yayi dace ya auri mace kuma kema kinyi dace domin wannan mijin naki akansa yan mata sai su bijirewa Iyayensu,hhh suna dariya,Zainura tace kuma kullum kice ya dinga yi miki murmushinsa domin yafi komai yi masa kyau,da tafiyarsa mu mun tafi ta fita tare da cewa ki kalleni da kalar tafiyarsa zan bar gidan nan ta fara gwada tafiyar Na'im suna ta dariya.

Salma ta koma bedroom ta samu Na'im yana ta dariya kamar sabon Kamu,yace ke wannan yan iskan fa?Salma tace sune su Jamila ai Na'im ya girgiza kai yace waccen yarinyar ta karshe da tayi magana duk tafisu iskanci,Salma tace Zainura ce, dan ma suna tunanin kana ciki ne amma abin ai yafi haka,Na'im yace lallai dole su bawa mutum dariya,baka gani ba zasu fita ta gwada tafiyarka,yace wataran zan gani ne ai.

Ban so ma suka tafi ba cewar Salma Na'im yace ni kin barni ni kadai ba kina can.

Salma ta kulle musu kofar suka koma bedroom,Na’im ya karaso wajenta tare da jawota jikinsa Zip dinta ya zuge tare da da cire mata kayanta gaba daya,ta cire masa nasa itama tare da rungumeshi,Na’im ya shiga kissing dinta sosai,yana murzarta son Ransa ,itama Salma haka take masa sun fita daga hayyacinsu tare da fadawa saman bed,Suna jiyar da juna dadi,Na’im yasa Salma ta haukace bata ma San me takeyi ba,yazo da niyyar shigarta Ko ma shiga baiba daga gogo wajen Salma ta saka kuka tace wlh ba a yin haka,kuma Zafi taji,Na’im yace shi kam sai yayi,Salma ta dinga kuka,Sai yaji tausayinta yana lallashinta tare da cewa kince baki sani ba?cike da shagwaba tace ae,Yace to na bari sanda zaki sani Amma wlh indai kika sani ba mutunci,tana dariya tace ae naji yanzu bari kawai muyi irin na jiya,Haka kuwa sukayi,Suka huta,da rana ma aka kara yi,haka da yamma,sai dai Umma ta kira Salma kawai ta karbi abincinsu ta koma aikinsu kenan yinin Ranar ba Hutu sun gama lugwigwice juna,daga Sallah sai cin abinci sai wanka .

  Dare ma basu huta ba haka suka kusan kwana,yanzu Salma har Sucking din boobs din ma bata hanawa,ko me yi suke rana daya sai da kowa yasan inda zai tabawa dan Uwansa yaji dadi.

Zainura suna fita suka ci karo da Sabo Saurayin Barira shima,yana dauke da farantin kwakwa a kansa yana kwakwaras a sai kwakwa, Zainura tace ga fa na karfen sarkin wanka,Sabo na Barira cewar Zainab,Sabo ya washe baki yace na baki Naira biyar,Zainura tace Allah ya kaimu ranar biki Sabo,Sabo ya sheke da dariya harda cewa da kuwa taci kwakwa ta koshi billahillazi Zainura baki da dama kema kin Samu goma,Jamila tace Allah ya baka Barira me kyau,Sabo yace hhhhh duk ni kadai nan take ya zaro Dari biyu yace naga duk ni kuka zabarwa kawarku gashi kuci kifi,suka karbe suna Sabon Barira..Sabon Barira,nan take ya zuba musu kwakwa a leda ya basu again,Sabo ya tafi yana zuba musu godiya,Zainura tace yau sai munci kifi ayasin,suna ta murna Rahmatu tace jaki Sabo gani yake da gaske muke yo me Barira zatayi dan wancan abu kamar kwado.

Barira tace ai dakikine Sabo yana fama da tallan kwakwa farin ciki Jan baya,ku kyale shege mu karya jarin cewar Zainura.

AsmaBaffa
[1/14, 5:14 PM] Sis Asma: ????KAMARSU CE DAYA????

101-105 106-110

Official

By
AsmaBaffa

 SUBY,XAHRA EABRAHEEM,MAMAN KHAIRAT,MAMAN WALEEDA,QUEEN MERMU,

ZAINAB ATIKU SALAMA
UMMU KHALEED
ga page naku nan.

  Washe gari kwana biyu kenan da auren Na'im da Salma,misalin 5pm Salma anci wanka an fito wajen Umma tana tayata girkin dare,Na'im ya fita tun 4 da ya fita Sallah bai shigo ba sai yanzu,ya hango masoyiyar tasa tana tankade garin Alkama,ko kunyar Umma ta saki murmushi tare da makale murya tace Sannu da zuwa tun dazu shuru ina ta tunaninka,Umma ta kalli Salma da Sauri Amma ta share kamar bata ji ba,Na'im yace Abubakar ne ya tsai da ni a masallaci shi yasa, Umma sannu da gida,yawwa Muhd Sannu,yana Yiwa Umma magana yana karewa Salma kallo,suka hada ido ya kashe mata ido daya,ta dauke kai,ta kara kallonsa suna hada Ido ya mata wani signa,Salma ta makale kafada tare da cuno baki,Umma tace Salma ajiye zan karasa kuje wajenku,mijinki ya dawo kina shirme tashi kuje,Umma dama korarsu takeyi su tafi wajensu suna sata jin kunya.

Suna hanyar shiga part dinsu Na'im yana baya ya manne da Salma ba space kamar jela kuma ya sa Hannunsa a Tudun Mazaunan Salma yana ta shafasu kamar dan Iska,suna shiga ya tura kofar ya dauketa cak tana dariya suka shiga palo a kasan carpet suka zube,kamar Yara haka suke wasa sun cika palon da hayaniya,suna ta tsokanar juna cike da shauki,Na'im ya kwanta kasan carpet yana kallon ceiling tare da dage kafafunsa,Salma tace sai ya daurata ya mata macilili,ta hau idan ya dagata yace wa kika bani?Salma tace Umma,Ya karayi tace Malam,yana yi tace Anty Rukayya,Haka take lissafo su yana shillata,tace sai ya mata doki doki,ya sunkuya ta hau tace Ina ma Umma na nan ta ganni Saman Doki na,dariya yayi tare da fado da ita kasa,ta fara Kukan shagwaba tare da kumburo baki Allah sai na rama,tazo tayi tayi ta ture Na'im ta kasa sai dan kansa da ya kwanta flat nan take ta haye masa ciki tare da cewa wa na kama? Yana dariya ai ni naga dama da kaina yarinya,kai nice yarinyar ma?ka ganni katuwa dani da hakorana kace min yarinya,Na'im yana murmushi yace to mece ke?to ai ba a goyani kuma ba a bani abinci a baki,bana shan nono zaka ce min yarinya,ko Rarrafe kaga ina yi? Na'im yace oho dai yarinya ce ke,Salma ita bata yarda ba yarinya itace me shan nono ko Rarrafe.

Kallonta yayi a nutse sannan yace yau ki dafa min Indomie da dare Bazan ci tuwon Alkama ba ni bana son tuwon gari ko wanne ne,da dadi fa?ae ni bana cinsa,ok to zan dafa ma karka yi kuka dan Allah ka kwantar da hankalinka,dariya ya dinga yi tare da cewa wannan ai sharri ne daga magana sai kice kar nayi kuka.
Radio ya kunna zai ji News kawai yaji ance a yaune garin Abuja aka gabatar da zanga zanga a fadar shugaban kasa,Na’im kansa yana Saman cinyar Salma yace kinji wani gari a kasar nan wai Abuja,Salma tace wai Capital city ne na Nigeria sai ka Isa kake iya zama ciki,haka naji ana fada wai in baka da kudi ko daki daya baza ka iya kamawa haya ba,Na’im ya zaro ido tare da cewa tab lallai abin babba ne ina ai sai kallo,Salma tace ko Kaduna Bazan iya zuwa ba bare wata Abuja,mu ina muka ga kudin zuwa ma,Na’im yace kika sani ko zanyi kudi na kwashe ki mu tafi,Salma tayi dariya tare da cewa Allah kace ai Allah yasa,aiko da na yi yanga a kasar nan,ko kai din nan da kake ganina sai na dinga maka yanga,sai kayi magana sau biyar ban amsa daya ba,to ai nine me kudin kuma kinga sai yanda nayi dake idan kina min haka sai na dawo dake nan na auri sabuwar Amarya, dama ni anan na sanki sai na dawo dake kuma na kwashe su Malam,Salma kamar gaske harda zubar da kwalla yanzu abinda zakayi min ke nan Amma ni na yarda na aureka ba komai tunda abin hakane,Na’im yana dariya yace wasa nake miki fa kece kadai,suna hirarsu har Magrib tayi yayi Alwala ya wuce Masallaci,itama tayi ta fara Sallah.
Saida ya dawo daga Sallar Isha sannan ta dafa masa Indomie da kwai tayi dadi,yaci ita kuma tuwon Alkama taci miyar Kubewa danya da manshanu.
Suna palo sun gama cin Abinci kenan sai ga Abubakar da Rahina sunzo ganin Amarya,Rahina da tsohon cikinta har 10 na dare suna nan ana hira sannan suka tafi gida.

Yau Sati biyu kenan da Auren Na'im da Salma,yau Juma'a ana yin Sallar La'asar sai ga su Jamila,Zainab,Barira,Zainura,Rahmatu da Zahrau sun kwada Sallama gidan Malam,Umma da Fara'a ta Amsa suka gaisa,Salma tana gyarawa Umma danyar shinkafa ta zuba musu hararar wasa tace ai nayi fushi sai yau?Barira tace ke kinji kawai sai mu kwaso kafa muna zuwa miki kullum kina Amarya,Umma ce tayi magana Salma tashi kuje wajenku dasu bar aikin zan karasa,Ta mike sanye take cikin English wears riga da skert tayi kyau,suna shiga wajen Salma Kamshi ya bigesu,Zainura tace Amarya sai da kamshi na baki lambar girma Amaryar me kyau,Jamila tace wani kyau da kiba take karawa,Salma tace aure dadi shi yasa,suka rafka shewa heeeee.
Zainab tace yau Me gidan baya nan mun ganshi a masallaci shi da wasu Samari,Zahrau tace har za muyi masa magana muka ja tsumman rayuwarmu,Rahmatu tace yo kwa soma yaje ya disga mu kuna gani Ba wacce ta isheshi kallo ko na mutunci bare magana,Zainura tace sai ni Zainura Yahaya Sani billahillazi Rahmanu da nayi niyya kusan kadan daga Halina har wajensa zanje na masa magana ehe,wa zai biyewa halinki Zainura ke da bakya tsoron kowa ke da Zainab,Zainab tace yo Allah na tuba kalli iya shege irin na Dan Isiya Amma ya buga ya barni.

Zainura tace ku bari ya shigo yasin sai nayi masa magana,Salma tayi dariya,Zainura tace ae sai daí kisa kaina gabas ki yanka Amma bari ya shugo ku gani.

Suna haka Sai ga Na'im tunda yaga takalma haka yasan sune domin yaga ma shigowarsu gidan,Sallama yayi ya shiga,Salma ance a zaman Aure ba kunya sai ka zama Karuwa gaban mijinka,aiko duk yan matan nan ko a jikinta ta mike tana karairaya tare da girza sassan jikinta har gaban Na'im ta makale murya kamar me rada sannan ta rungumeshi tare da Rada Masa a kunne Sannu da zuwa,yan mata suka dauke wuta duf suna kallo,Na'im ya dago da fuskarta tare da tallafo kumatunta da hannu biyu yana aika mata da wani mayen kallo me aika sakon zallar so sannan yace kinyi kyau My Heart,nan take ya hade bakinsu waje daya suka dinga kiss,Su Barira suka ja ajiyar zuciya,Zainura ce taga sunki dainawa sai tayi gyaran murya,sannan Na'im ya dawo hayyacinsa yaja hannun Salma tare da cewa muje ki cire min kaya ki canja min wasu wannan sunyi Nauyi,Jamila ta daura hannu aka irin abin ya wuce tunani,kallonsu Salma tayi tace ku dan jirani Kunji, muryar Zainura suka ji tace Ina yini mijin me kyau,jin tacewa Salmansa me kyau ya kalleta harda murmushi yace lfy ya kuke,suka hada baki lfy kalau kalau wlh,ya janye Salma suka shiga,da Sauri ta canja masa jallabiya fara,yana ta faman tabe tabe a jikinta,sai da ta gama ya dan dan rike hannunta da karfi ta kwalla kara,Su Zainura a palo kasa kasa sukace to fa Kunji mun shigesu kuji yan Iska,
Salma ta fara masa cakulkuli yana mata sai dariya sukeyi saman Bed,Zainab tace ko dai abin akeyi,Jamila tace wasa suke dan ubanku yau mun shigaigada mun lalace,Zahrau tace yan iska ne wannan sabon Salo kunga Amarya ba kunya ba tsoron lamyalid walam yulad,Zainura tace munga waje wlh baza mu tafi ba sai munga me sukayi.

15mnt sai ga Salma da Na’im sun fito sunga Na’im da jallabiya,Salma zata zauna yasa hannu a wuyanta tare da cewa Umma zan taya aiki tunda kinyi baki,Ok Honey ayi me kyau,ya fita yana murmushi,

Zainura ce ta fara magana yau naga abinda yafi karfin kuma wallahi Allah canja masa kikayi?Haka kamar jariri Salma? Barira tace gaskiya yan Iskane ku Salma Bazan boye ba,Zahrau tace wai muka ji kararki dukanki yayi ko mintsini?Salma tana dariya tace wasa muke, ke ki bari Dan Manzo ai yanzu har wasa kuke kamar wasu Yara yan firamari?Salma tana dariya tace to mene,To da kuke kyalkyala uwar dariya kuma fa?,Jamila ta tambaya tana tagumi irin abin mamaki Salma tace kuma dan bani da hankali sai na fada muku?wlh Bazan fada muku ba,Zainab tace ke Jamila kema kin san Iskanci sukeyi taya zata fada miki,heeeee suka kwashe da shewa tare da cewa wlh Iskanci sukeyi,Barira tace da aurensu fa ba Iskanci zaku ce ba Sunna sukeyi heeee nan ma dai,Zainab suka ji ta kwashe da dariya tare da cewa wayyo ciki na,Zainura dan Uwarki kin san me na tuna? Wai tsotsar bakin juna sukeyi dama haka akeyi ance a birni,Amma a nan garin yasin ban taba gani anyi ba a tsotsi baki cab,
Zainura tana dariya tace Na rantse Bazan yarda Isyaku ya makamin bakinsa cikin nawa ba,a haka ma gefe nake matsawa idan yana min magana wani hamami wlh kamar yaci daddawa Alquran Bada ni ba,ai ko an aura min shi yasin kaina na gefe,Kinsan rannan yace wai Zainura ina magana kina dauke kai?nace Isyaku kar kace naci ma fuska,dan Allah duk bishiyar dalbejiya dake garin nan da gawayi,ga Alimun yanzu ace har yau kana cikin duhu baka goge bakinka,shike nan matsiyaci ya kai karata wajen Babana har dukana akayi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button