KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

A gabansa Salma tayi Sallah ta idar,tana idarwa Aljanunta na tashi ta fara yage yage da bige bige,tana Farawa Na’im ma nashi suka tashi ya fara kalar nasa wanda ba a San yana da su ba,Na’im ya damki Salma itama haka suka dinga cin uban juna suna ta kokawa ba wanda yafi karfin wani,karayar Salma ta kara karyewa baras sai an gyara amma bata sani ba,
Na’im yaji ciwo a kafarsa fata duk ta yayyage,malaman Hospital suka taho da gudu akayi musu Allurai bacci amma suka ki yin bacci duk karfinta bata sasu bacci ba, kamar wasa suna ta aljanun
Suna ciwa junansu mutunci,Salma tace Kai kamar na kunkuru,Na’im yake baki kamar na tsuntsu, Idonka kamar na kunama,Naim yace kanki kamar takalmi,saina yankaki,saina fede ma ciki, mutanen asibiti dake dakin dariya ma abin ya basu dama idan mutum na Aljanu sai aga kamar yana sani yakeyi karyace kawai kuma da gaske ne.

Wani malamin Doctor ne a Hospital din yazo da Qur’ani ya musu ruqiyya duk da cewa Aljanun basuyi magana ba guduwa kawai sukayi amma sunji sauki nan suka kwanta ko wanne a bed dinsa suna ta bacci basu farka ba sai da gari yayi haske tangararan.tun jiya da dare an kara dora Salma Living things tana bacci,haka shima Doctor me Imani anyi masa Treatment na rauninsa.washe gari da suka farka babu wanda yasan yayi komai sai Raunin da suka gani,Na’im yana yin Sallah ya bar asibitin ya tafi gida,ita kuma brush kawai tayi ta hau gado ba sallah ba komai tayi kwanciyarta tana tunanin Ina Raheel ya tafi karfa ya gudu ya barta da ciki,

 Yunwa ce ta addabeta tana ta faman tunani to wai wannan idan ba Raheel bane waye?kamshinsu da kayan da yake sawa duk iri daya dana Raheel,kamarsu daya da Raheel komai nasu ba banbancin

, ta dauki lokaci me tsawo har Mummy,Dada,Aisha,Hunaif,da Irfan suka shugo suka taddata ras da ita,Mummy da murmushi tace sannu ya jiki,ita dai Salma kuka takeyi Raheel ya tafi ya barta nufinta Na’im ne Raheel ya tafi kuma,
Irfan duk sun mata sannu sun dauka zafin ciwo ne yasa take hawaye,Irfan yace wa ya miki wanka?tana shesheka tace Ni…ni…ce nayiwa …kaina da hannu daya,Kaya wa yasa miki?tace Raheel mugu ne ya sa min,Kallon kallo sukayi Mummy tace dan Ubansa ga nurses ba zai kira su sa miki ba sai shi Allah ya shirya,

Ita dai Kukanta takeyi ta kalli Dada tace dan Allah Iyya ba Raheel bane wannan din nan? Dada tayi murmushi tace ba shi bane wannan Na’im ne jikata,ba wani ke dai kice kin kare Jikanki cewar Salma.

Abinci Aisha ta mika mata,Salma ta kalleta kurrrr tace ni bana cin abincin yar shaye shaye,wlh Mummy ki mata fada kwayoyi da syrup take Sha,dazu ma da sassafe da Codein ta karya ko ba haka akayi ba?kuma kina neman mata yan uwanki jiya ma kunyiwa juna kiss da wata.

Aisha kunya ta kamata tayi miki miki tabbas gaskiya Salma ke fadi ko Aljana ce ne?

Mummy ta Kalli Aisha tace kinji kunya dama baki daina halinki ba?Dada ta fashe da kuka Wlh baza su koma turai ba zuri’ata da shaye shaye wannan mutanen boye ne da ita gaskiya ta fada.

Irfan a dole na kirki ya fara cin uban Aisha, Salma ta kalleshi tana Kukanta tace hmmm kai har kana da bakin magana?abinda jiya jiya a Sheraton Hotel ka kwana da wata,Mummy ko ya kwana a gida jiya?
Mummy karya ya miki yace yana da meeting a Kaduna a hotel ya kwana da Arniya Amy wogu sunanta, Irfan yayi mukus ya tabbatar Salma Aljana ce tasan komai,nan Mummy taci Ubansa son ranta,Hunaif ya sheke da dariya,Salma ta Galla masa Harara tace kai fa jiya har wiwi kasha kaje club kaida frnds naka kuka dinga Romancing yaran mutane.

 Na'im a kunnensa komai ya faru yazo shigowa Room din kenan yaji Tonon sililin da Salma keyi,haka ya daure ya shigo ta daga kai ta kalleshi Salma ta saki murmushi dimple dinta ya loba me kyau tace wannan Mummy da kike ganinsa duk kalar giya ba wacce baya Sha,yanzu ma ya jefar da kwalabar da ya shanye wata yana Dustbin na jikin dakin nan,aje a duba idan karya nake Allah ya tsine min na zama Barewa a daji.
Mummy ta fashe da kuka yanzu duk yaranta ba wani na gari ciki,da kyar Dada ta lallasheta,Na'im yaji haushin Salma yace ke kuma wanne laifi kike aikatawa? Tace yo ni me nake yi ai ni ta gari ce, in banda Sallah dana ke dan kin yi amma ai gwara ni Sallah ce kawai Ku fa?giya fa giya fa,neman mata ga shaye shaye da chasu tirrr daku.
 Ai ke kinfi kowa ma lalacewa tunda Sallah ce guda bakyayi duk wanda baya sallah baya musulunci,duk aikinki a banza ba a karba tunda bakya sallah wawiya, baki ta murgudawa Na'im tace kaine kake ba da Ladan? Kuma na fika dai wooooo tayi masa gwalo.

 Mummy tayi ta salati tace yo ke yar nan ai kece me babban laifi ma ai kuwa kiyi gaggawar tsaida Sallah,
Abinci Mummy ta mika mata amma taki ci akayi akayi taci taki kuma Allura ake so ayi mata,Na'im kayi shuru kasa baki taci mana mu Kebbi zamu wuce Allah kara lfy sai jibi zamu dawo ka kula da ita dan Allah kaji abinda nace ko Na'im karka yarda ka saba min a bayan Idona kan wannan yarinya na fada ma,to Mummy Allah kaiku lfy,suka fita Driver ya jasu sai Airport.

 Tsawa Na'im ya bugawa Salma ci mana ban son Hauka,ba shiri ta fara ci,da sauri zakici da yawa kuma haka yanda yace takeyi,Rankwashi ya zuba mata a kai kin jawo min masifa,mayya wlh na kara ji kina cewa Mummy munyi Bad something sai na karyaki again,Dariya Salma tayi tace Fada kyau yake ma Raheel mugu kalli dan lips dinka ta kai yatsa zata shafo da yatsanta ya make hannu,zafi ya ratsata sosai sai da tayi hawaye tace haba Raheel Haba Raheel dan kaga ina sonka? Kaine fa ka samin sonka ka dinga zuwa zance wajena,cikinka ne a jikina,kaine fa ka bani ajiyar cikin nan dana ke Shan wahala dashi,kasan me nake ji a jikina?kasan irin ciwon da nake yi?kasan irin yanda na rabu da masu riko na?dangina basa Sona basu da zumunci iyayena kafi kowa Sanin sun rasu ban san kalar Uwata ba ban san Ubana ba,haka sabo da kai ka rabani da masu rikona na gaskiya Affa da Ummitu na,Yan gari da yan Uwa duka zagina sukeyi suna ce min karuwa,bani da sauran mutunci.

  Ka hanani karatu ka hanani muamula da kowa,kana yawo dani a duniya har daji da bola amma haka baka hakura ba ka samin ciki na daya nasha wahala,yanzu ga na biyu, Bana komai amma still ina sonka,ina sonka Raheel,kana mun mugunta iri iri kamar mahaukaciya ka maidani,amma ina sonka har yau Bana Jin sonka na raguwa ko digo sai ma karuwa da yakeyi kullum.
Ana cewa Aljani ne kai Raheel amma ni nasan kai mutum ne,ko kai Aljanine ina sonka haka wlh ina sonka Raheel,me yasa ka cuceni kazo min a suffar mutum idan ma Aljani ne?me yasa kazo a suffar mutum kake min komai na mutum har kasa min sonka na shaku dakai,Ba karya nake ba,da hankalina ba Aljanu nake ba kamar yanda nake ji mutane suna fada wlh da gaske ina sonka hankalina daya sonka ya kamani tun ina yarinya gashi kayan da kake sawa same dana Raheel dina,turare,kamarku daya,motocin da Raheel ke zuwa min dasu irin naka ne,abu daya ne baka min baka kaini Different Countries,baka tarairayata kana lallabani kana nuna min zallan so irin na Raheel dina,baka yi mini yare iri iri,Raheel dina ko wanne yare idan yayi min na iya shi nima,har Spanish da  French etc ya akayi kai turanci kawai kakeyi baka sauran yare kuma nima yanzu duk naji ban iya yaren ba Sam iya turanci da Hausa da fillanci nake ji why ban iya wanda mukeyi da Raheel ba?
Amma har yau na kasa ganewa na kasa tabbatarwa zuciyata cewa ba kaine Raheel dina ba,photocopy ne na Raheel kai baku da banbanci ta ko ina,kuka take dirza sosai tana Koro wannan bayani nata,I love u Raheel ta zame dankwalinta tace kalli gashin da kace duk kafi so a jikina,wanda kullum sai ka shafa shi in kazo zance,me yasa nake sonka da yawa Raheel?kana azabtar dani Raheel ta kara fashewa da kuka ta fada Jikin Na'im wanda take ganin fa Raheel dinta ne,

Tausayinta Na'im yaji sosai ya kyaleta a jikinsa tana ta sheshekarta fatar fuskarta tana gugan  fatar wuyansa zuwa gefen fuskarsa har ta gama kukanta ta share hawayenta tace I really Really missed u Na'im me yasa kake min haka?, 

Na’im cike da tausayi da rauni a hankali yace sabo da bani bane Raheel dinki,ya kamata ki gane bani bane Raheel,kinga ni bana jin yare da yawa,ban sanki ba,bana nuna miki so,bana lallashinki da lallabaki kamar wancan Raheel naki kinga bani bane Raheel kenan,ni Na’im nake ba Raheel ba kinga bani kike nufi ba,ki yarda kamar muce kawai daya da shi,dama ai Allah yana halitta haka kuma ki kwantar da hankalinki ki nutsu ki dinga Sallah ki tsaida Sallah kina addua ina tabbatar miki Raheel dinki zai dawo,zai daina baki wahala,zai dinga ci gaba da Sonki yana lallabaki yana ji dake ko?Kuma cikinki zaki haifar masa lfy ko? Dagowa Salma tayi cike da murmushi me tsanani hannunta daya sakale da wuyan Na’im tace To na hakura kuma zan jirashi har ya dawo,amma kuna kama dan Allah idan Bai aureni ba zaka aureni? Na’im Bai kawo komai ba yace na miki alkawari indai Bai aureki ba ki dawo zan aureki in dai ina raye,baza kayi min kishiya ba?Kuma ko ka auri wata sai ka aureni,kuma idan an kusa bikinka da wata zaka fasa ka aureni? Na’im dan ya huta da surutun Salma yace kwarai ma kuwa na miki alkawari.
Salma tace to na gode bani address din gidanku aiko Na’im ya bata katin gidansu dana Hospital,Embassy da duk inda yake aiki saida ya bata address shi baya son Surutu ne shi yasa ya bata.

 Tace to yanzu Saura abu daya dan Allah,yace me? tace dan samin kaina cikin rigarka na shaki kamshim turarenka zan daina yin Amai da tashin zuciya,

Ido ya zaro waje yace ai iskanci ne fa?tace ae shi nake so yau na danyi kadan nima kullum sai in ta Zama ni shike nan a ta gari nake,bana wani laifi kullum a ta gari ai gwara na dan ajiye record nima,Na’im Bai San sanda ya dinga dariya ba,ita kuwa birgeta yakeyi sai kallonsa takeyi kamar ta lasheshi tana murmushi ta shafa masa girarsa da yatsa,da karfi ta damki rigar Na’im ta dage ta sama ta tura kanta cikin kirjinsa suka fadi a kasa ta danneshi ta shaki kamshi da yawa saida ta gaji sannan ta fito da kanta tana murna,tace tashi to na Shaka sai kuma gobe da safe zan kara.

 Bani abincin naci kaji,mamaki yakeyi yanda take da karfin gaske,gata kuma hannunta ya karye sai yaga tana amfani dashi kadan kuma baiyi komai ba gaskiya wannan Aljanin nata ma me sonta ne da yake mata haka.
Abincin ya dinga bata a baki tana ci tana kallonsa yana goge mata baki da tissue,tace ka dinga ci kaima kaji? Yace to,tace mu gama ka kaini yawo a kafa zamu zaga ko?nanma yace to,tace wai kaine me asibitin nan naji ana cewa naka ne?uhm kawai yace,tace kai me kudi ne gaskiya,Raheel dina ma me kudi ne yayi ta bani kudi ina kashewa,sai fa ya bani Dubu Dari biyu etc,Na'im yace ya kyauta,tace kasan me? No, hmm ban taba period ba ni ko zaka dubani tunda likitane?yace age naki nawa?kwana nan na shiga 17 fa,zaki iya Farawa ai nan gaba,ok to kunna min kida kaji? Nan ta shiga lissafo masa latest wakoki da suke tashe na shekarar,ido ya zaro yanda duk tasan abubuwan yayi na zamani,yace duk ina kika sansu?Raheel dina ke kunna min har rawa ina yi fa,kaga kuwa wayar da computer ta tab masu tsada ya siya min suna gida na ajiye zan nuna ma watarana.surutun ya ishi Na'im yayi mata banza har ta gama ci ta koshi.

AsmaBaffa

Masu Sharhi kune nawa tnx
[1/14, 5:14 PM] Sis Asma: ???? KAMARSU CE DAYA????

    36-40  41-45

Official

By
AsmaBaffa

      Yana gama bata ya mike ya tafi Office nasa ba tare da yace mata ko a ba,allura likitan ya zo yayi mata da kyar ta yarda,kwanciya tayi sai bacci,yana can yana duba Patient,y ama manta yana da wata maralafiya da yake jinya, sai daga baya ya tuna nan take ya tura wata Nurse ta gano masa ita ya take,

Nurse tana shiga ta hangota tana zaune sai kuka takeyi Raheel ya gudu ya barta,
Da Sauri Nurse taje ta sanarwa Na’im abinda ta gani,yace je kizo min da ita Office dina, minti biyu sai gasu sun shigo tare da Nurse, Salma da doguwar rigarta purple tare da siririn galenta harda kwalliya a fuskarta bakinta da jambaki,Na’im a ransa yace wato Nurse tayi mata wanka ta shiryata domin wannan rigar cikin kayan da ya siyo mata ne,kuma tayi masifar kyau lips nata abin kallo,gashinta ya kwanta gaban goshi,Nurse din ya kalla yace wa ya shiryata?tace Nurse Zahra ce tayi mata komai har abinci ta bata,ok kawai yace ita kuma Nurse ta juya tare da Barin Office din.

Salma sai murmushi takeyi tuni ta daina kuka tunda taga Raheel dinta,saman Table dinsa da yake rubuce rubuce ya nuna mata da Biro dake hannunsa ta hau ta zauna,ko ta zauna kujerar dake Office din,wow Office din ya tsaru ya hadu karshe an kashe masa kudi,sai kamshi da sanyin Ac ke tashi,saman Table din ta dane daf ta zauna kafafunta suna Lilo a kasa,hannunta ya kalla yaganshi ma kamar ya warke shuru yayi mata baice komai ba,kunya da dariya ta kamata ta dinga kunshe dariya tayi kasa da kanta tana duba yatsunta masu kyau,ya rasa me takewa farin ciki,tana ta faman murmushi da jin kunya yau wannan salon tazo dashi kuma.
 Kallonta yayi cikin kasa da murya kamar me rada tare da cewa ya akayi? sai ko ta rufe fuska da tafukan hannu,tana ta murmushi sai da tayi ta koshi sannan ta bude idonta tare da cukulewa kuma irin ba wasa, kin iya hada Coffee? Yeah ta fada da karfi,yace good kinga machine can da komai ciki jeki hado mu gani,
Sai da ta dafa kafadarsa ta sauka kasa coz wajen yayi mata tsayi,tana zuwa sharp sharp ta hada masa a glass cup na tea,ta kawo masa ya karba tare da kurba yaji wani shegen dadi,muryarta yaji tace da dadi? Sosai ma cewarsa,hmm kawai tace,ya tambayeta a ina kika koya?kuma a kauye kike fa? Raheel ne ya koya min komai du na iya,baki ya tabe ke komai Raheel baki komai sai da Raheel,everything Raheel,kamar gidanku daya i can't understand am so confused, Salma tayi warr da Ido ni kuwa ina ganewa ai,must ai dama cewar Na'im.
 Zauna na tambayeki amsa kuma nake so me ma'ana,zama tayi a kujerar dake facing nasa,yace bani labarinki,tun mutuwar iyayenta da masu riketa,da Raheel,danginta duk ta iya bashi labari,yace kina kauye ya kika iya turanci haka?kika iya kwalliya da shiga,kin iya komai why?haka ta faru?tace ni Raheel ne ke koya min fa,cikin dake jikinki wa ya miki?Raheel ne ya saka min ba yimini yayi ba,Countries da kike zuwa kin San duk kasashe ba adadi wa ya kaiki?da wanne kudin? Nan ma Raheel,komai Raheel,tun kina 3yrs Raheel,everything Raheel ta tabbata Raheel ba mutum bane kenan ko?,

Kuka Salma ta fashe dashi ita dole fa Raheel mutum ne,zaka ce ba mutum bane kaine Aljani ba shi ba,ta dinga masifa ba ji ba gani wai yana zagin Raheel,tsaki yaja tare da cewa bani Address din gidanku Driver na ya kaiki gida wajen iyayenki ni bazan iya ba kin fiye shagwaba da yawa ,Raheel ne yake shagwabani fa kuma ai Mummy tace ka bari ta dawo,baki da matsala baza tace komai ba gobe za a kaiki gidanku, baki ta cuno wlh bazan tafi ba Raheel ina tare da kai.

ko an kaini sai na dawo wajenka.

Numfashi yaja kene Mayya?ya tambayeta,ni ba mayya bace,to kene Mannira?dariya tayi tace sunana Salma,yace no…no yana dacewa ace iyaye naka Mannira suka sa miki ko mayya,kaine Dan Fulani masu shaniya da noanoa?,yes muna da shanu da Nono kana Sha?baki ya tabe Kazami.. kazami kune Bana so na Shaniya sai na kwali Holandia understand?ni sai na dura ma na Saniyata ka shanye,hannu ya fara karkadawa wai no…no bazan Sha bama na kulle bakina harda tsuke dan bakinsa,Dariya tayi sosai,ya tsaya yana kallonta, Raheel me yake damunka ne? Kana ce mini Raheel ba shine ba,Na’im ne ni,aiki..aikina inayi kazo kana damuna pls back to ur Room banma san Why na kiraka nan ba kana damuna cewar Na’im.
Kida ya kunna na turanci a wayarsa nan take Salma ta fara bin wakar kamar ita ta rera har kada kai takeyi.

  Affa da Ummitu suna can takaicin rashin ganin Salma ya ishesu ga talauci,can Affa ya kokawa yan uwansa matsalar da suke ciki tare da abinda Salma takeyi,nan take yan uwansa suka hadu suka zugashi, shi yasa watarana ma shawara da wasu matsala ce, cewar Salma idan ta dawo ya koreta kawai yayi mata korar kare Domin zata kasheshi tun kwanan sa Bai kare ba,ya dawo ya Sanarwa Ummitu,itama ta gano zancensu gaskiya ne tace Malam wannan gaskiya ne ka duba farar kafa irin ta yarinyar nan tunda aka bamu ita kullum talaucewa mukeyi bamu taba ci gaba ba,munfi kowa talauci a garin nan namu,yanzu akan nema mata magani duk abinda muka mallaka ya kare,saniya ko daya babu,kayan dakina,gonakinmu duk sun kare tas,a abinci har makwafta taimakon mu sukeyi kullum talauci yaki ci yaki cinyewa sai yawan Shan garin kwaki,duk ya tsotse mana jini da ruwa,Uban Salma mahaifi ya zalunce  mu dama yasan yarsa haka take Ashe ya lika mana ya mutu ya barmu da wahala..shi yasa yan uwansa suka ki riketa.
Affa ya nunfasa yace yanzu na tsani yarinyar nan wlh Bana kauna na bude Ido na ganta a gidana,dama kaddara ce tasa na dauki jaraba,tunanina munyi yar kirki Ashe jaraba muka Raina da hannunmu,
Bamu karu da ita ko tsinke ba sai raguwa,Allah ya gani munyi iya yinmu munyi na Allah munyi na Annabi munyi na Binta dan haka taje can tayi yawon duniyarta,wannan rainin hankali ne yarinya gantalalliya cewar Ummitu.

Affa yace ko ta dawo idan kika barta ta shigo min gida to Allah ya isa ban yafe miki ba,na gaji da talauci,Ummitu tace oh Ashe gaskiyar bahaushe da yace tsintacciyar mage bata mage mun karbi Bala'i da hannunmu,Affa ya kara da ni dama Bana kaunar rike dan wani,dan wani ko jaraba Allah bai bamu ba mu hakura,dama dan kar nace ban so ne kice wani abu shi yasa nayi miki kara naga kina sonta.

Ummitu ta tafa hannu tare da cewa yo aini ta Dade da sire min dama kwadayin yara yasa na karba jaraba ai zamu yarda kwallon mangwaro mu huta da kuda,nan take shedan ya kara dasawa Affa da Ummitu kiyayyar Salma a zukatansu suka ji ba wacce suka tsana a duniya sama da Salma,suna ganin cutarsu ma takeyi tun farko.

Dan Adam kenan bashi da tabbas,yanzu da Salma bata samu matsala ba ko Allah yasa suna daukota kudi suka samu ta hanyarta ko wani abu da yanzu basu da sama Salma, baza suce komai ba, amma an musu kyautar ya guda tsakani da Allah sabo da kaddara ta sameta ta shafesu suna furta kalamai munana,dan Adam me manta alkhairi,inama Tall Man Baban Salma Bai rasu ba yaga cin Amana,butulci da manta alkhairi wajen Affa da Ummitu,farko sunyi bajinta amma at the end sun kasa jure kaddara wanda ita kanta ba ita ta dorawa kanta ba,
Yanzu da yarsu ce ta cikinsu baza suce komai ba ta Zama dolensu,dole su hakura su karbi komai,kuma baza su taba tsanarta ba,amma wannan sabo da basu San ciwonta ba basu San zafinta ba sun zobe ladansu wajen Allah,dama haka dan Adam yake bashi da tabbas kuma ba a iya masa musamman zamanin da muke ciki,daga naka sai naka,naka iya naka,kowa kansa ya sani baza ayiwa wani Uzuri ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button