KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Tana tafiya yayo kan Zainura zai damkota ta Mike da gudu ta shige dakinta tare da sa key,Yace ki bude ko na balla kofar nan tace bazan bude ba Allah,me yasa kike haka? Zainura tace haka kawai ba na kori Usman Ba nace anmin miji shine kai zaka kawo wata,to ina ruwanki da ita wajenki tazo,ae amma ai Na yarda Ina Sonka,Irfan dadi ya kamashi yace sai dai Ku zauna Ku biyu na aureta na hada dake,ni yangau inji kishiyar me hakori bazan auri wanda zai min kishiya ba,kama daina tunanin wata,yace kince bakya sona ai? tace hehe dama karya nakeyi ina sonka amma Allah bazan iya fada ma a gabanka kunyarka nakeji yanzu ma fa dan na rufe kofa ne,amma ina kallon wannan Hancin naka zarkadede bazan iya fada ba,amma yanzu kuwa tunda ba a gabanka nake ba ina sonka harda kwalla da karfi tace  karya na dingayi Allah nace nima sai Naja aji,hhhh Irfan yayi dariya yace to ai kin tonawa kanki asiri,nima na iya ta yan Birni kuma watarana ba irin wannan salon zanyi ba wani daban zanyi baza ka gane ba sai idan na fada,Na iya yanga nima dama ai cewa nayi sai na gwadaka Ashe nima ba karamar yar gari bace,ta fara gwada muryarsa Zeena ki aureni pls,ina Sonki,bare yafi na gida,na wanashi kamarka ni yar Zainura na dinga juyaka kamar waina.

Irfan yana jikin kofar yana dariya tayi abinta ta tonawa kanta asiri abin na Zainura harda Kuruciya,yace nan gaba zaki ga yanda ake juya waina ai sai na kamaki ya wuce ya tafi cike da murna sosai,tana jin ya tafi ta fada saman Bed tana sai aure muma Iskanci is arround the corner,ana ta zancen Iskan cin nan kullum sonsa nake to nima dai ya kusa karaso min heee ta dinga tsalle da murna.

Salma ce kwance Saman Na’im Sam baya daga mata kafa kullum cikin bukata yake,yanzu kamar handbag haka Salma take duk inda zai matsa tana kusa,bashi da hakuri ko kadan wajen bukata sai dai idan bata da lfy ko yaga ya dan takurata sai ya dan kyaleta ta huta duk da cewa Salma ma kusan kai daya suke basa gajiya,watarana ma itace take nema da kanta yanda take masa salo bazai iya hakura ba,Salma mabukaciya ce ta gaske har mamakin kanta take,ita kanta bata so ko da Sec su rabu da Na’im shi yasa shi kuwa wannan abu yana masa dadi,Mummy kuwa tana hado mata kayan gyara iri iri masu tsada na manyan mata,shi yasa ma Na’im yake kara Manne mata kullum kamar jela,daga Office sai gida,yanzu ma murzata yake amma kafin me ta hargitse baza ta iya Control ba sai taji Na’im cikin jikinta,duk dadewar da Na’im yake ko a jikin Salma dadinta ma takeji,domin yanzu idan Mummy tace dana maza ma a maganin da ta bata sai taje ta durawa Na’im susha abinsu suyi ta tsula tsiya a saman Bed,ko motsinsu ba a ji, iyakaci suyi ta cin abinci me inganci kuma ba lallai Xxx sukeyi ba watarana a romancing suke gamsar da juna,sabo da ba a son xxx din yayi yawa,Ba kullum take Shan maganin matan bama sai jefi jefi tafi karfi wajen cin kayan itatuwa haka Mummy take tsara mata.

Bayan su Malam Magaji sun huta suka tattara nasu ya nasu sai gasu Sunzo Abuja,Na'im da Salma sai murna,Mummy ta basu part dinsu,Dada ma tace haka kawai an wareta kamar mayya,itama ta dawo gidan ta nemi dakinta,Salma ta kawo Shawara wajen Na'im wai dama Mummy ta auri Malam Magaji,Na'im ya dinga kishin Ubansa yace wlh karma ta soma yaji zancen,Mummy baza ta auri kowa ba sai iya Ubansu,kuma ita Umma an mata adalci daga zuwa ayi mata kishiya,wlh indai kika fada sai na miki kishiya kiji idan da dadi,Salma ta dinga bada hakuri taji ance za ayi mata,tace subutar bakine wlh bazan kara ba,yace oh to Umma ce bakya so zaki ce ayi mata kishiya,Salma tace bazan kara ba wlh kuskure ne,ni bazan kara magana ba.

Malam da Umma sunji dadin jin cewar Irfan zai auri Zainura za a hada bikinsu duka rana daya Alhmdllh,Zainura tunda tasan yanzu ta gama samun Irfan bata cika magana ba yanga take masa itama fa tace Yasin Yanzu ta fara gogewa,Zainura ta Zama yar gayu ta gaske ga gwalli da iyayi sai dai fa akwai abin dariya har yau ba fashi,Irfan jin sa yake kamar ma ya Zama Angon.

Takanas Su Malam sukaje wajen Iyayen Zainura aka tsayar da maganar biki rana daya dana Hunaif da Aisha,an dauke musu komai na biki ko cokali baza su siya ba,Aisha ma yanzu ana barinta tana fitowa Palo har tsakar gida,Mummy ta dauko musu me gyaran Amarya har Salma ake yiwa gyaran Na’im yace komai sai anyi mata itama,har lefe da aka hado harda na Salma itama ba abinda aka banbanta su sai dai kowa da kalar kayansa daban,Zainura sai dai tayi ta tsokanar Salma cewar ita an gama komai idan an koma sabon gida ba abinda zata kaiwa Na’im sabo sai dai watakil ko jinjirin ciki,Aisha kuma tace mata ragowar mata,har Hunaif tace shi kuma tasa tana turai wa yasan tsiyarsu data shukawa,ita kuma da Irfan tace su kadai ne cikakkun Ango da Amarya na kirki,Hunaif sai dai su dinga dariya.komai sai tace ita za a fara yiwa itace budurwa hhh.
Kullum sai sunyi fada da Aisha basa fasawa wai dole sai Aisha tace mata Anty Zainura,Aisha tana magana zatace mata yarinyace itace Anty ,Mummy tana jinsu sai dai tayi dariya,Yanzu kuma Anty Salma take cewa Salma wai kannenta ne yanzu,Salma ma yanga take itace matar yaya Babba,itama tace sai abinda tace Zainura zatayi tunda itace Babba ai,Zainura kuma akwai bin doka sai ta bi abinda Salma tace,Salma ma fa yanzu ta Murda kambumta ta boye virginity nata cewar baza ta kara yarda da Na’im ba sai an gama gyara ta dawo Budurwa idan sun koma sabon gida sai a Sha Amarci,amma yanzu ko Romancing hanawa takeyi sai an gama gyara an kai Amare,Na’im ya biye mata shima yana ta dauriya,tunda yaga idan ma ya matsa ba yarda zatayi ba,Zainura ta gama zuga masa mata ita ta bawa Salma shawarar nan.Umma kuwa gyaran da takewa Salma na daban ne wai yartace,tana bawa Su Zainura ma amma basu kai Salma ba.

Love u all.

AsmaBaffa
[1/14, 5:14 PM] Sis Asma: ????KAMARSU CE DAYA????

181-185 186-190

Official

By
AsmaBaffa

 UMMU KHALEED ths page is for u.

MOMMYN ZAHRAH taki ba irin tasu bace Ina gaisuwa Allah ya bar kauna.

 Maimuna Matar Hashim laulayi yayi sauki cikinta ya girma,tayi kyau da haske,yanzu Hashim bashi da matsala kauna yake nunawa Maimuna sabo da ta samu lfy,Allah shirya wasu mazan,da yawa lafiyar mace suke so,idan bata da lfy babu kauna ba tausayi ba mutunci,sai ta warke kaga sun lallabo,wasu ma sai dai macen ta koma gidan iyayenta idan ta warke ta dawo gidan miji,ko ya kara aure ya dinga wulakanta marar lfy.

Iklima matar Ubale ta yiwa Maimuna Nasiha da fada kan maganar batsa da sukeyi a majalisar gidan ana fallasa siririn mazaje,Maimuna ma yanzu bata zuwa majalisa ita da Iklima suke harkarsu.

Salma Amarya karfi da dole itama ji take da kanta,Na'im shi ba son wannan Amarci da ake masa tanadi yake ba gwara a kyaleshi ya kwashi gararsa yanda ya saba,amma Salma ko ganinta ma bayayi wasan buya sukeyi bata bari ya ganta.
Gajiya yayi ya nemo Zainura yace lallai ta nemo Salma duk inda take ta kawo masa ita,Zainura a ranta tace Salma ta shiga uku ba zai bari ayi gyaran nan ba,Taje ta sanarwa Salma,Salma taki zuwa,har dare ya tako da kansa ya iske Salma tana kwance abinta tana bacci ma,ya tashi Salma tare da cewa taso mu tafi,Salma tace ni dai baccina zanyi a nan,Na'im yace nifa Bana son wannan Amarcin wlh mene wani tanadin Amarci mun rigada munyi abinmu,ni bazan iya jira ba,Salma ta saki Kuka cike da shagwaba,haushi  yasa Na'im ma yayi zuciya ya tafiyarsa,Ganin yayi fushi yasa ta bi bayansa da sauri,yana shiga tana bayansa,yace jeki zan rufe room dina,to ni me nayi maka?nace kinmin Laifi ne? To kayi hakuri gani nazo tunda baka so na hakura,gani yayi tana son Amarcin nan da take masa tanadi kawai sai ya fasa tunda ko jikinta bata so ya taba yanzu yasan zai takurata kawai yayi murmushi tare da cewa jeki kiyi bacci na hakura har sai an yi bikin ba matsala,Salma taji dadi tace bakayi fushi ba?yace yeah ai na yarda zan hakura,ta dinga murna sannan a masa goodnight ta fice kamar wasu saurayi da budurwa.

Aisha da Doctor Aliyu bata wani sonsa amma ba yanda zatayi haka ta hakura tayi biyayya ga yayyenta,abinda suka yanke dole zata bi sabo da sune kamar Abbansu tunda bashi da rai,a yanzu zamanin nan waye yaya ko wasu yan Uwa kowa abinda yaga dama yakeyi,ba biyayya iyayen ma bare yan Uwa yayye,wasu kannenma za kaji suna zagin yayyensu face to face ba tarbiya.
Na’im ya kai Malam bangaren Business dinsa na noma yana aiki a nan tunda dama shi bashi da karatun boko sai Arabic sai noma,shi yasa ya dorashi akan abinda Malam ya sani kuma yana aiki yanda ya kamata,
Rahina da mijinta ma Abubakar suna Abuja duniya sabuwa Na’im ya gama musu komai,sai waya da sukeyi suna jira bikin Irfan yazo suzo ayi dasu,haka ma Su Barira kawayen su Zainura jira suke biki ya matso su taho bikin kawarsu,
Aikin da Na’im ya bada Kwangila ayi a kauyen an gama komai da komai,da kansa yake shi kadai Da chairman na Lg din suka bude wuraren akayi addua sannan aka yiwa mutane bayani aiki zai fara ranar Monday.

Zainura Amarya ko Zance bata damu su zauna suyi da Irfan ba daga makaranta sai gyaran jiki,sai dai dole idan watarana yaje dauko ta tofa shine za ayi hira,gaba daya ta gama sanarwa yan schl za ayi bikinta har yanga take zata yi aure,Irfan ya kirata tazo garden sai da ta dauki dogon lokaci tana tsantsara wanka ta cakare kamar zataje Dinner sannan ta tafi wajensa,tana yanga ta karasa gabansa tare da Sallama ta zauna saman kujera kusa dashi,Irfan sai kallonta yake kamar maye,Zainura taji kunya har wasa take da yatsunta,kin San me?taji muryarsa me dadin saurare da sanyi sai ka fada,ki daina min shuru shuru nan Bana so yanda na ganki naji ina Sonki to hakan nake Sonki shi yasa har zan aureki,Yanda kike Zainuranki ta asali me surutu da abin dariya haka nake Sonki ni duk wannan yanga,jan aji,basa birgeni ga mace,indai zaki min abinda nake so ki min biyayya,da tsafta iya kwalliya,shike nan wannan shuru shuru din naki ki dauki abinki kiyi shi a waje ni kuma tsakaninmu ya Zama normal yanda kike da,
Da yawa maza wasu ba son yangar nan ta mata tayi yawa ko mace tayi ta faman masa iyayi wasu ma mazan haushi suke ji wlh ba birgesu take ba kuma basa Jin dadin Zama dasu,komai baza a fada ba,ba wasa ba dariya sai kayan iyayi wai Jan aji ne to dai maza da yawa ba a birgesu ta nan,amma ace kuna tare tsakaninka da miji kullum cikin nishadi ana Jin dadi,amma wasu sai suyi duf suna cika suna batsewa ana magana da kyar wai shine Jan aji ta ya zaiji dadin Zama dake,ke kullum sai serious abu ba wasa ba dariya,yana da kyau ki dinga sashi nishadi ba lallai ace sai ta hanyar kwanciya ba,ko a gida kullum gidansa a nishadi ake ko da za ayi yangar ai ba kullum ba,amma su wasu Sam mutanenmu basu gane yanga,iyayi,da jan aji ba,kuma wai abin haushi kullum a haka suke a gidan ba canji,wasu ma gani za kayi sun dauki waya suna chat mijin shima ya juya baya can yana danne danne ba wanda ke magana,kowa Danna waya yake abinsa,itama tana can tana chat ta hade rai,tana ta faman yanga da kyar take masa magana kamar yar sarki,ga karyar iyaye,wai matanmu yanzu karya har miji ake yiwa,ta siyi kaya da kanta tace iyayenta suka kawo,ta siyi abu tace yar uwarta ko Kanwarta ta kawo mata,a gidansu basa cin kaza kaza suke ci,babansu kaza yake dinka musu,basa sa atamfa yar kaza karya iri iri,kuma wlh mazan suna ganewa kawai sharewa sukeyi,to ci gaba kikayi ko baya me karyar zata miki?miji yasan ke makaryaciya ce ai ba sauran daraja.
Ya kamata mata mu hausawa mu gyara zamantakewa wlh ba a iya komai ba,kowa abinda yaga dama yake har mazan,ba a tunanin wasu ka’idoji da dokoki da Allah ya daurawa masu zaman aure a’a kawai abinda naga dama ko taga dama ko yaga dama shi zaiyi .

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button