KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Zainab tace kai dan muhammada Rasulillahi Ku dinga salalawa junanki kamar zaku ciye juna,wai haka ake wannan soyayyar ne  irin taku ta shiga da masifa baza a dinga hutawa ana sakewa ba sai dai a junanku,bakwa gajiya da juna,ni wlh irin wannan damuna zatayi kale kale a wajen miji baza ayi Harka da Alumma ba sai iya miji,Barira tace ke kyalesu zamu koyi Darasi,Zainura tace lallai Sabo zaisha love,Barira tace ai wlh ya matso kusa dani ma sai na tsandara masa mari,Jamila tace ke ki bar ganin Sabo haka figigi jikinsa kamar itace haka yake ke bakya ganin kaurinsa,Zainura tace da zaki kyasta Ashana a kauriin Sabo kamawa zaiyi da wuta sabo da bushewarsa,nan ma suka kara shekewa da dariya,Barira tace ko a gari ba dukansa idan fada ya kama,Rahmatu tace bare kice zaki mareshi ai gwara ki cijeshi,Barira tace kaji banza cizo salon na karto dauda da hakorana kenan,Sabo bazai taba Jin dadi ba idan ya sake ya Aureni kin San Allah yana Palo ina ciki,yana ciki ina Palo,Zainura tace ga shawara idan ta tabbata an daura ki kulle shege ki tsiyaya petir kina daga waje kice ya sakeki ko ki cinna wuta,Rahina tace a'a ai tayi sake an daura idan ya saketa ta Zama bazawara ba daraja,kawai ta masa tun a waje yace ya fasa aure,Zainura bada shawara kinfi kowa iya mugunta,Salma tace ni zan bayar ki samu idan yazo zance ki dauki dutse ki shammaceshi ki faki Ido ki rotse masa kai,ki tabbatar jini ya zuba zai ga lallai zaki iya daukan ransa a waje zaice ya fasa,

Salma ta bawa kanta amsa tace idan yaki yarda fa kun san Sabo da taurin kai shegiyar Hammata kamar bishiyar kaya cako cako hhhh suka sake dariya,Har Na’im dariya yake ta yi Salman tasa ma Ashe shu’uma ce bai sani ba,Salma tace Plan B ki tafi da Reza sabuwa sai kuna hira ki lallaba ki dora masa ita a gadon baya kawai yaji kyat kin yankeshi kice idan ya aureki da Wuka zaki farke masa Hanta,Zainura tace plan c ki tafi da kwalabar lemo ki fasa ta a jikin katanga kiyi kansa kamar da gaske zaki caka masa,zaiga fa lallai kasheshi zakiyi zai fasa aurenki,amma idan har ya daure ya aureki haka am so sorry Barira sai dai buzunki domin sai ya dauki fansa yaci ubanki a gidansa,wlh sai kin raina kanki,Hhh Hunaif yace ga tawa Shawarar kawai ki lallabashi yace baya Sonki da kansa Barira tace kai maye ne wlh karata ma zai kai gidanmu baka San muguntar Babanmu bane gashi masifaffe,Hunaif yana dariya yace to Kiyi addua kawai mafi Alkhairi,Zainura tace sannu Ustaz to Sabo ba Alheri bane ka auri mutum irin Sabo Kazami ina khairi ciki,ga taurin kai baza a nuna masa gaskiya ba,komai shi ya iya nasa ne me kyau,ba a isa an canja masa ra’ayinsa ba bare ace Barira zata iya koya masa tsabta,bazai yarda ba,Barira tace ai sabo gani yake yafi kowa wayewa da komai a duniya,kai ko kai baka isa sabo ya saurari shawararka bare mu na kauye.

Hunaif yace dan Allah gobe a nuna masa Sabo ya ganshi,Salma Da Na’im sai kus kus sukeyi a gefe su kadai,Zainura tace dare yayi goma ta wuce Ku tashi mu tafi gida,gaba daya suka Mike tare da yiwa su Rahina Sallama sai gobe,Abubakar ya rakasu ya rufe gidansa,ko wacce budurwa ta tafi gida,Irfan da Hunaif har gida suka Raka Zainura sannan suka koma gidan Malam cike da nishadi,Hunaif yace amma wanne yan mata kwai yan banza,ga surutun tsiya ko baka so sai kayi dariya,Irfan yace irinsu Zainura haka Allah yake yinsu komai wayewarsu duk inda suka shiga sai anci dariya,abin dariya ne dasu,haka wasu suke ba yanda za ayi Ku hadu basu bada dariya ba.

Gaba dayan su Irfan su uku bangaren su Na'im da suka zauna nan ne masaukinsu,Irfan da Hunaif suna bed room saman Bed,Na'im kuma a Palo ya samu an shirya masa yar katifa madaidaiciya,shi bazai iya kwana shi daya ba Bai ma saba ba,Salma kuma tana wajen su Mummy can zata kwana,Na'im tunani yayi dabara ta fado masa wurin 12am dole so yake ya bar wani tarihi a kauyen shi da Salma,bedroom din ya shiga ya tashi Irfan,Irfan cikin bacci yace wai dan Allah mene haka ka damu mutane kamar kai kadai kafi kowa matar aure,me za ayi maka,Na'im ya bata rai sannu yayana gadonmu zaka daga mana Ku koma Palo ai ba gidanku bane,

Hunaif yace wai bro ba kwaya kakesha ba?kai wai kullum a Iskanci zaka kare,to mu bazamu fita ba,kun San ai ba kunyarku nakeji ba wlh Ku fitar min daga Bedroom ai ba gidanku bane,Irfan yace muje Hunaif idan ya fara masifa wlh bazai bari muyi bacci ba.
Suka koma Palo saman katifar,shi kuma ya kara gyara bed din ya fita tsakar gida yana ta faman kiran Salma a waya tana bacci bata daga ba sai da ya kira yafi sau goma,Sannan Dada ta farka a tsorace tace Innalillahi kunnena za a kashe min dodon kunne ke tashi ki daga waya ko na jefarta waje,Salma ta farka tana ganin Na’im ta Marzaye dan kar ta tashi Mummy can kasa tace hello Honey,preetyna fito ina tsakar gida,kai dare fa yayi Honey kuma Mummy da Dada fa zasu ce ina naje,su suke aurenki? Sanda aka daura suna ina?kizo ko na shigo na fadawa Mummy da kaina a gabansu ma Daukoki zanyi bare wata Dada kunyarta zanji?
Salma tace to tsaya karka zo gani nan,Sai da Salma ta faki Ido ta tabbatar sunyi bacci yayi nisa ta lallaba ta Mike tare da Zare Sakatar dakin,Mummy ta farka dama taji Hirar da Salma tayi,tace ke dawo dan Ubansa ya kwana a waje,baza kije ba,Salma ta kwanta tayi luf,Na’im ya kara kira Salma tace yana kira fa kuma a waje yake gwara na fada masa kin hana sai ya tafi,Dada tace kyaleshi ya bushe,Salma tace kai Hajjaju,Na’im ya kara kira Salma ta daga tace Mummy ta hana,Na’im yace ta bawa Mummy wayar,Mummy ta karba yace Mummy yanzu fa zata dawo Paracetamol zata kawo min kaina ke ciwo idan baki yarda ba to ta baki ki kawo min da kanki,jin yace a bata ta kawo masa sai Mummy ta yarda lallai gaskiya ne,Salma tana ji tana dariya a boye,Mummy tace dauko maganin na gani a Idona sai ki kai masa,Salma ta duba ta dauko paracetamol kamar gaske tace gashi,to jeki ki dawo da wuri,tace to.

Dada tace ke dai kwai sakara yara suna miki wayo to bari ki gani baza ta dawo ba zaki ce na fada miki.
Mummy tace Hajiya ai Salma bata da wasa da dai Zainura ce nasan zata aikata amma Salma ai akwai kunya,Dada tace Salma wlh tafi Zainura Fitsara Salma a boye take yi,Zainura kuma dan tana da baki ne ita barta wajen dariya a yaran yanzu waye Ustaz?
Mummy tun suna jiran Salma ta dawo suka ji shuru har bacci ya kara tafiya dasu.

Salma kuwa tana fita ta hango rabin ranta yana ta jiranta,tace yanzu ina zaka kaini?yace me ai na koresu daga Dakinmu suna Palo,Salma tace amma baka ganin suna Palo ai bai dace ba dani da kai a bedroom,Na'im yayi murmushi yana shafa fuskarta yace kina wasa da aure,a filin yaki ma ta kama kebewa zamuyi,muje ni su ba ruwansu da kike gani,kune Hausawa kuke irin wannan kunyar mu bamu yi,kuma ko Mummy da kike gani ko itace a Palo zamu iya kwana a bedroom bare wani su Irfan yan Iskan duniya.

Ki Bari ki gani suyi aure zaki ga yanda ake rashin kunya,Salma tace to ni zanji kunyarsu ai,kinyi ta banza su basa Jin taki Babyna sai kace kwartanci nazo wai ba mata ta bace,iyakaci fa Ko muna abu baza aji Sound ba wa yasan me mukayi? In ma an sani ai da aurenmu,nan dai Na’im ya dinga tsara Salma har ta yarda ta bishi,Su Irfan bacci yayi nisa basu ma San sun wuce Bedroom ba.

 Salma tace ta ya za muyi wanka to?ai da Asuba zaki koma wajen su Mummy,Salma tace to kaga dai wannan Second ne pls karkayi da Zafi Allah dan ma Anan gidan ne ka damu sai ka yi amma ni da bazan yarda ba,Na'im ya kashe Salma da kalamai tayi shuru duk da cewar tana tsoro bata so,haka ya tallafo wuyanta da hannu daya ya fara kissing dinta Daya hannun yana zame mata rigar baccinta dake jikinta,Salma ta fara daukan Zafi zata kama da wuta tana so ta fitar da Sound ba hali,shima haka idan daya zai loosing Control sai daya ya rufe masa baki,Salma da kanta ta cirewa Na'im kaya shima haka,sun firgita junansu yanda ko wanne ke nunawa dan Uwansa kauna ba a cewa komai,I love u kuwa anyi ruwanta kasa kasa,
Salma tasha tsotse iri iri lungu da kwazazzabo duk wani kusurwa, Tudu da gangare tasha murza shima haka sabo da Salma gwana ce wajen  Bedding,wannan lokacin Na'im ya kusa Suman dadi Haukacewa yayi sosai yanda yaji Salman tasa wata zam zam,Salma kuwa bata ji Zafi sosai ba can kadan taji bata Sha wahala ba yanda ya bi da ita itama ta dan ji dadinta da Zafi,Na'im kamar ya taka rawa sabo da dadin da yaji a duniya babu kamarsa,ya rasa ma inda zai sa Salma,Ya rasa me zai mata ya birgeta shima,Albarka yake sa mata yana godiya,Salma tace ka daina gode min pls kai da abinka.

Bacci sukayi me dadin gaske wanda babu kamarsa dole a tuno da wannan lokaci,Asuba nayi ta gyara dakin fes kamar ba ayi komai ba,Na’im yace ba zai tashi su Irfan ba sai dai su makara,ana Zafi kawai sukayi wanka tare da Salma dana tsarki da normal wanka da Sabulu,da ruwan Zafi a flask ta gasa jikinta kadan kafin da safe ta samu me yawa, Salma tayi alwala ta lallaba ta tafi Dakin da su Mummy suke,Na’im kuma yayi Sallah har gari ya fara Haske sannan ya tashi su Irfan suma sukayi wanka da Sallah.
Lokacin da Salma ta koma dakin Mummy sun idar da Sallah suna Azkhar,Mummy tace sai yanzu kika dawo? Salma tace Laaa ai kuna bacci da Asuba na shiga dayar toilet din wanka nayi amma ai a nan na kwana,na dawo dana kai masa magani kunyi bacci ne,Dada tace uhmmm gaskiya ne tsari Master yan Iskan karshen Zamani Ku bakwa so mazajenku suyi fushi ko,Mummy tayi murmushi kawai domin tana son mace irin Salma baza su bari mazajensu su shiga damuwa ba,suna kula dasu,taji dadin Samun suruka me Kula da Danta bashi da matsala,ga kunya da girmama surukai,Salma ta kalla tace to yi Sallar mana Rana zata fito,Salma tayi Sallah da Azkhar tayi waje wajen Umma da Anty Rukayya tana tayasu hada breakfast.

Irfan ya Kalli Na'im da ya Mike saman doguwar kujera yana ta shakar bacci,Hunaif yace wlh Na'im yafi kowa jaraba Allah ne kadai ya kareshi bai taba kusantar mace ba sai da yayi aure,amma bashi da hakuri a harkar ko kadan,Irfan yayi dariya tare da cewa dan rainin Hankali ka ganshi dai kamar baiyi komai ba,yanzu zai ta yiwa mutane muzuran banza,Hunaif yace cewa zaiyi ma bata zo ba shi kadai ya kwana bari ya tashi kaji.
Na'im bayan yasha bacci ya tashi Hunaif yace Wai Anty Salman Mummy ta barta tazo wajenka kuwa jiya ai kace Mummy ta hanata da farko,Na'im ya basar yace bata zo ba fa ai Mummy ta bani matsala ta hanata haka na kwana ni kadai,da kyar ma nayi bacci jiya,Hunaif yayi dariya yace gaskiya kam ka kwana ba bacci Salma bata kusa,Na'im yace hmm kai dai bari waya nayi ta dannawa ina aiki ciki,Irfan yace ah lallai kasha aiki maimakon kazo ka tashemu mu koma Bed din,Na'im yana tabe baki yace mantawa nayi,
Irfan yace wlh karka raina mana hankali Bro naga sanda kuka bar Palon nan tare da ita da asuba har da kin tashin mu Sallar asuba,Na'im ya bata rai yace zanci Kutmar...bai karasa ba yayi kwafa tare da cewa yan sa idon banza yau baza ku kwana a nan ba Allah.Hunaif ya dinga dariya yace haba dan Allah mu ai yan zaman dakinku ne yanzu muna yara me muka sani,Zaman daki muke muku.
Salma da hijab dinta ta shigo ita da Anty Rukayya suka jere musu breakfast,Hunaif yace Anty ina kwana Salma tace lfy,yace nifa ba da ke nake gaisarwa ba babbar Anty Rukayya,Rukayya ta amsa tana dariya suka gaisa,yanda suke birgeta ba ruwansu da wani girman kai yan turai kenan,Salma cike da shagwaba ta kalli Na'im wai ni bazai gaisheni ba sabo da ya girmeni,Na'im yayi murmushi yace kyaleshi mu bama son gaisuwarsa.

Irfan yace ita waccen wai sai ta gudu gida taki fitowa,Zainura ai tazo gida ta manta kowa kuma ma ai yanzu safiya ce me zata fito tayi maka cewar Na'im.
 Bayan sun karya kowa yayi shiri suka fito gaba daya za aje gidan su Zainura su gaisa da iyayenta,Irfan yafi kowa Zumudi.

Suna zuwa sunsha tarba da karramawa Mummy taji dadi Iyayen Zainura ba ruwansu wayayyu dasu,Umman Zainura itama akwai Surutu da hira sosai,Zainura bata gidan ma wai ta tafi gidan yan uwansu.
Sun Dade sannan suka dinga zuwa gida gidan da suke mutunci dasu Salma frnds harda me gari duk sunje, dangin Malam dana Umma duk sunje an gaisa sun musu godiya,ko wanne gida in dai sunje to zasu Sha kyautar kudade kuwa,har na gari idan aka gaisa in dai Na’im ya sanshi to sai an masa kyautar kudi,gari ya dau Murna da jin dadi.
Na’im yace Zai gina musu makaranta da hospital Gomnati zata dauki ma’aikata,zai musu titin kwalta,sannan kuma za ayi musu tuka tuka da yawa a garin,yan gari sai murna da jin dadi ana godiya,Yace kuma Malam da Umma su shirya dasu zasu tafi,Malam yace ba da ba jika zasu bisu zasu dinga zuwa ganin dangi ana gaisawa.
Zainura ba a ganinta gaba daya tunda sukaje a yawo take wajen yan Uwa da abokan arziki.
Abubakar da Rahina kuwa Na’im ya bawa Abubakar Manager na Company nasa a Kano tare da kyautar gida dallele da mota sabuwa,sannan yace ya koma Ya karasa Degree dinsa,Dangin Rahina da Abubakar sai godiya domin Salma Dubu Dari ta bawa Rahina Jari.
Anty Rukayya da dukkan frnds din Salma dana Na’im tare da iyayen. Zainura kujerar Makkah ko wanne za a tattarasu su tafi gaba daya,Zainura tace pls a hada da ita,Irfan yace a’a sai idan Zasu je a gidansu dasu Na’im zasu tafi har ita.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button