KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Washe gari Mummy tace ai bazai yuwu Salma da Zainura suje su kadai ba sabo da dole ayiwa dangin Salma bayanin aurenta maganar Aure bata yara bace kuma ba wasa bace,Haka Mummy da Dada suka shirya takanas suka bi flight suka fara Sauka a Borno state gidan su Shehu da Malam Musa,ganin masu kudi Salma tazo dasu ba wasa,Shehu duk da a wulakance suka karbesu amma sun sauraresu,Dada ta musu bayani Malam musa yace Allah sanya Alkhairi,Shehu yace na taba ganin iyaye mata da shiga sabgar Aure? Kuma za a rufe mu yar da take tamu shine za a mata auren bariki sai daga baya za a zo a sanar mana sabo da ba a daukemu da muhimmanci ba,ba a mai damu iyaye ba,to Allah ya bada zaman lfy me kuma zamu yi mu ai sai Ku tafi da abarku,Mummy da Dada suka dinga basu hakuri ana musu bayani amma sukace su fa basu ce komai ba kuma Salma dole dai tasu ce ba uban wani ya haifeta ba dan haka dole ta nemesu aure kuma Allah bada Lada suje kar a cika su da surutu.

Hashim ne kadai ya kai su Mummy bangarensa Maimuna ta musu sauka ta mutunci,kuma ya tsaya ya gane duk abinda su Mummy suka zo dashi ya rufawa Salma baya,haka dangin uwar Salma Ubale da Matarsa Iklima sunyi murna kuma sun fahimci komai tare da sa albarka.
Mummy tace su kwana wajen Hashim Salma da Zainura wajen Ubale da Iklima suka kwana cikin Jin dadi.

Washe gari sukayi shirin Tafiya Mummy ta bawa Hashim Dubu Dari wai idan Maimuna ta haihu ayi suna,ya dinga murna da godiya,haka Ubale ma ta bashi Dari,harda durkusawa dan Murna,ta bawa Malam Musa shima,haka Shehu uban yan son kudi nan take ya canja ya fara nunawa Salma so yana mata fara’a sabo da kudi,matan gidan kuma kaf Dubu Ashirin aka ba ko wacce ta ja jari sannan suka tafi.

Zainura tace Bala'i Wallahi Salma danginki son kudi garesu,jiba rashin mutuncin da suka mana,daga Hashim sai Ubale ne suka karbe mu amma sunji kudi sun rude Allah ya shirya gwara da basu suka raineki ba Alquran da tuni sun jona miki son kudi.

Abuja suka dawo basu koma gida ba Mummy tasa Driver ya wuce dasu kauyen su Affa,suna Sallma a gidan Affa yana gyarawa Akuyarsa igiya ya hango lallai Salma  ce da iyayen barikinta,Ummitu ta fito da kwarya da gari ciki,Su Mummy suka mata Kwarjini da gani an San kudi ya zauna musu,shuru sukayi basu ce su shugo ba kuma basu ce ga wajen Zama ba,Zainura ne ta shiga tare da rafka Sallama ta hango tabarma a jikin bishiya kamar gidansu ta jawo ta shimfida tace Ku shugo Mana,Affa dai basu iya magana ba sunga Mummy kalar Naira ba wasa,Bayan sunwa Kansu masauki nan Mummy tace Ku zauna Malam za muyi magana akan hanya muke,da kyar Affa ya zauna can nesa tare da zaburowa da Masifa muna saurarenki.

Mummy ta fara da Nasiha haka Dada ma ta nuna musu hakkin Salma dake Kansu a Matsayinsu na marikanta sannan ta musu bayanin komai har auren Salma,tare da fahimtar dasu su Affa sun San gaskiya amma suka take sani wai dama to mene a ciki sai me kuma dan tayi aure Allah sanya Alkhairi,Mummy sunga rashin Imanin su Affa,Salma kuwa murna tayi tasan an samu ci gaba domin da ace dane basu isa ma sun shiga gidan Affa ba,amma yanzu har sauraransu sunyi ai abin farin ciki ne,Mummy taga harkar ta su Ummitu ba mutunci ciki tace to Salma zamu barki a nan gobe kya dawo ko?
Affa yace ina? Yanda kuka zo da abarku Ku tafi da ita,Dada tace oh Ku kuwa bayin Allah kamar baku San darajar Dan Adam ba?Ummitu tayi tsagal tace kija girmanki iya mun fiki Sanin wace Salma ba ruwanku,Salma tace ya isa a bar zancen nan take Salma ta rubuta address kamar yanda ta bawa su Malam Musa haka ta rubuta Address na inda take da Phone Number ta mikawa Ummitu tace a kyale zancen haka gashi nan duk ranar da kuka huce kuka gane gaskiya zaku nemeni,Mummy Ku taso mu tafi,Nan Mummy ta zaro makudan kudi ta mikawa Affa ya buga tsalle yace bada ni ba,baza a siyeni da kudi ba,na karbi Dubu Dari nazo ina asarar milliyan daya ina dalili kuje da tsiyarku.

Mummy tayi murmushi ta maida jaka abinta,Zainura tace Alquran baku da rabo, 
Salma tace Zainura Bana so muje kawai ina ruwanki iyayena ne fa,Zainura tace Allah ya huci zuciyarku Affa sai dai ayi hakuri damu na daukar muku tabarma ba izni,Affa dan Fulani da mugunta masu taurin kai yace can da matsalarku zaki zo da kafa kamar ta sauro ke ga marar kunya ko ya fadawa Zainura,Zainura ta dinga kunshe dariya har sai da suka fito tayi abarta wai kafata kamar ta Sauro,Dada suna dariya suka ce ai gaskiya ya fada,Mummy tace Amma ko a yan Fulani wannan na daban ne wajen taurin kai,aya hadisi duk basuyi ba,Salma tayi dariya tace ai baku gani ba da muka zo da Na'im ba arziki,hhhh Dada tace shu'umi shi yasa yace bazai zo ba Ashe shi yaga abinda ya gani,Salma tace ai da kun gani da kunsha mamaki,Zainura tace Allah sa dai bai kwadeshi da sanda ba,Salma tace Saura kadan wlh hhhh sai dariya,Mummy tace ki rabu dasu duniya zata nuna musu gaskiya Allah zai ganar dasu addua kawai zakiyi ki kwantar da hankali har gida zasu sameki,muma ai iyayenki ne ba abinda baza muyi miki ba,Dan ma Memory dinku bai dawo ba sai kinfi kowa gatan iyaye,gasu Malam Magaji,ga danginki na Borno,gamu muma,ga su Affa idan Allah ya ganar dasu kinga ke iyaye ko ina,dadi Salma taji tana dariya sosai taji hankalinta ya kwanta.

Tunda suka dauko hanyar dawowa City Zainura take ta labarin jirgin da suka hau,yau ta hau jirgi har Borno itakam da sa’a take a duniya.
Dada tana ta dariya tace Wai jikata yaushe zaki zo min ne ko kwana Uku muyi tare a gidana,Mummy tace ai sai dai Irfan ko Hunaif ya kawo ta idan ta shirya,Zainura tace ko Aisha ta kaini ba,fada zakuyi a hanya cewar Salma,Kiran Na’im ne ya shigo wayarta,sai da ta kusa tsinkewa ta daga hello ta furta cikin nishadi,ya aiki? Alhmdllh dazu na kiraka baka dauka ba,Ina Office ne,ya sun huce?Salma tace kadan ba har yau dai basu huce ba amma dai ba irin da ba,yace ok Allah yasa to su huce gaba daya,tace Ameen ina su Mummy?,gasu muna hanyar gida mun kusa karasowa,yaji sanyi a ransa tare da cewa can’t wait to see u Baby missed u Badly,Salma su Mummy na kusa tace zan maka text ya gane baza ta iya magana ba sabo dasu Mummy,kiss ya mata ta waya tare da cewa ina jiranki a part dina ba sai kinyi text din ba,need to see u Hearty am just wanna feel u,Murmushi Salma tayi me Sauti tare da furta me too a hankali ta kashe wayar ta wani basar irin fa ba wani abu akayi ba.

Zainura tana can tana kallon gari har suka shigo cikin gida ta hango Irfan ya fito da shirin fita yayi hanyar wajen Zalleliyar motarsa,da sauri ta danna glass yayi kasa ta leko da Kanta tare da kwalla masa kira Irfan dan gayu....da sauri ya juyo ya San dama sai ita,dariya yayi tare da dago mata hannu,zai shiga mota kenan tace ka tsaya labari zan baka,motar na parking ta fito a nutse ta karasa wajensa tare da cewa ko kace Sannu da zuwa ya hanya,ya kalleta kawai yace to sannu da hanya,tace yawwa dama fada maka zanyi ta kare maka gaba daya ka daina min iyayi da kuri dan jirgin da kake jin ka hau nima na shiga kuma me zaka nuna min,kai kenan ka dauki photo a jirgi to nima na shiga dai.

Murmushi yayi tare da cewa ai ke na kauye kika shiga na Nigeria ni fa?duk dai sunansu jirgi ko,ina zaka je da yamma haka? Yace masallaci,Masallacin sai anje a mota sabo da sangarta,Mota ya shiga tare da cewa sai na dawo kya bani Labarin naki sauri nake,yau Hunaif ne nawa shi zan bawa Labarina sai na kureshi yau naji a ina karyar wankan nasa ya tsaya,Irfan yace sai dai kiyiwa Aisha,Zainura tace ai nafi karfinta Yasin Hunaif kadai zan kure yau naga shi yafi kowa rainani,Irfan yace to shi dai kika masa Zaneki zaiyi ba ruwana,jeka kawai bari naje na huta,Irfan yaja motarsa ya tafi,Zainura tana shiga gidan,tana shiga Hunaif ya kalleta tare da cewa ai na dauka an maida ke kauye,Zainura tace ka fara kuka ko? Allah sarki ai baza a maida ni ba ka kwantar da hankalinka ba sai ka fada min ba nasan sona ya kamaka Ashe kana nan kana ta tunani na ko an maidani zaka shiga uku ko?Hunaif ya dinga dariya tare da girgiza kai domin shi Zainura tafi karfinsa a magana,tace yaushe rabon da ka hau jirgi?kamar abin kirki yace tun last yrs,ta sheke da dariya tace to ni ba ajinka bace domin jiya i yanzu ina ta shawagi a sararin samaniya kamar tsuntsu,kaifa har shekara guda idan kuri ne kafi kowa,ni kuwa jiya me tukin jirgin da kansa yazo har wajena yace yan mata kece Zainura ko? Nace ae ya kalleni yace Zeena Baby kin tafi dani daga yau idan kina so kullum kizo zamu dinga yawo cikin gajimare,yau ma Mummy ce ta hanani amma da a jirgi za a saukeni a cikin gidan nan,Hunaif yace
Shi kuma duk ina tukin jirgin?ya barshi kuna yawo a sama yazo wajenki?Zainura ta zaro Ido tare da cewa sabo da na isa, jeki ki huta kizo yau na cinyeki a game Idan Irfan yazo kije kici gaba da raina masa hankali shi zai dauki shirmenki.

Aisha da tsokana ta fito tace a'a ba sabanba an hau jirgi duk an damu mutane a gida,yar talakawan kauye,Zainura taji haushi yau a maganar Aisha amma sai ta kyaleta bata ce komai ba,sabo da ta fuskanci sam Aisha wulakanta talaka ne da ita ba irin su Hunaif ba za ayi wasa da dariya,ita Zainura bata saba shuru shuru ba tafi so ayi wasa da dariya ana nishadi ta tsani shuru shuru.

Salma bedroom dinta ta shiga tare da sheka wanka ta shirya tsab ta dau wanka cikin wata yar Gown mitsil da ita ta daura hijab tana kamshi ta fito da niyyar zuwa part din Na’im sai taga Dada da Mummy,sai ta Rabe a Bango wai kar a ganta zata je wajen Wani,sai ta leko ta koma,basu san ma me takeyi ba,sai da ta tsaya ta shirya dabara sannan ta fito zuwa wajen Mummy tace Mummy Na’im ya baki Sako ki bani yanzu? Mummy tace ai ni tunda yayi min sannu da zuwa ya koma part dinsa,Shagwaba ta fara tana doka kafa niā€¦Haka fa yace zai baki yanzu maybe ma ya fita,Dada ta saki baki tare da cewa ke baki san inda yake ba kije ki karba mana zaki damemu wlh shi yasa bana son zuwa gidan nan duk fitsararru aka tara daga matan har Mazan,Salma tana dariya tace Bari na dawo Hajjaju muyi hira zaraf kamar walkiya ta haura samansa,Na’im kuwa yana sama ya leko ta wajen steps yana kallon abinda takeyi,komawa yayi tare da labewa jikin labilen Palonsa,tana shugowa yace tatttt ta Tsorata sosai sai da ya fito yana mata dariya,Hararar wasa ta masa tare da cewa ka tsoratani zan rama,murmushi ya mata wanda ke kashe mata jiki,yana kallonta ya zare mata hijab yayi arba da rashana,Daukanta yayi tare da dagata sama suna dariya,zamota yayi kirjinta saitin kansa,ya tura kansa tsakiyar kirjinta yana shakar kamshi,Salma ta lumshe ido tare da makale shi,a hankali yace kinci abinci?Salma tace a’a,me zaki ci?Salma tayi wani fari da ido tare da juyasu tace shawarma,nan take ya jawo waya tana jikinsa ya Kira Irfan,kana ina?yace yanzu ma ina hanyar gida yace Dan biya ka siyo min shawarma,Salma tace da hanta,yace da liver,ta kara rada masa da zuciyar Kaza,Na’im yace da Heart din kaza,Irfan yace wlh baku Isa ba kun raina min Hankali ina Jinta fa sai dai taci ta Rago ko ka bata taka ta cinye,
Suna dariya Salma ta kara Radawa Na’im da Icecream da Doya da kwai,da soyayyen dankalin Hausa me yaji,Irfan ya kashe wayarsa tare da masifa abinda naga dama zan siya sai dai kar taci,nan ya tuna da Zainura baiwar Allah,ya Kira Mummy yace ta bata wayar,Zainura tana kwance tana hutawarta ita daya Mummy ta bata waya ta bar dakin,Zainura tayi Sallama ya amsa yace me kike sha’awa zaki ci ko sha?Zainura ta rasa me zata ce ta shiga tunani,yace fadi tace koma mene zanci,Irfan yace ki fada ko mene zan siya miki,Zainura dadi ya kamata dama sha’awar shan abun takeyi Baffansu na siyo mata idan yaje kasuwa sai ko tace yashin Madina ko carbin Malam,idan babu kuma ka siyo min tsami Gaye,Irfan bai taba ma jin me kama da sunan ba,yace mene wannan abin mu babu anan ban sansu ba,Zainura tace ni Alquran su nake so idan babu shike nan ni,yace nawa ake siyarwa?tace yashin Madina Yanzu yayi tsada Uku Naira biyar,Carbin Malam guda biyu Naira biyar idan Katon carbi ne,tsami Gaye biyar Naira biyar ne,idan yayi tsada kuma na hakura ka kyaleshi kawai,Irfan saida ya dinga dariya kamar ta kasheshi yace kinga wani abu zaki fada ko nama,shawarma,burger,icecream etc,Zainura tace tab ni na sansu ne,Nama fa kullum sai munci a gidan nan yanzu ma gasu can a kitchen sai kalar da nake so dan ta’adin kudi da almubazzaranci nace ka kara siyo min,Irfan yace to zan siyo miki ko mene,Zainura tace ni Alquran bana so Bazan ci ba,haka kawai mene babu a gidan nan,Irfan yana ta dariya yace to kayan kwalliya fa?dana sawa?Zainura tace kai kayana yanzu har sunfi kala ashirin fa,a kauye kayana kala Bakwai ne gaba daya a haka kuma ni yar gata ce,amma dan rashin godiyar Allah nace sai ka sai min wasu ai sai na zama me handama,idan ka dawo lfy ma ai munji dadi,banda tukin ganganci Allah kawoka lfy idan ka samu Yashin Madina to ina so sai anjima kit ta kashe wayar ta bar Irfan da dariya.
Zainura haka ta dinga mita wai ana kashe kudi a banza.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button