KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

KAMAR SU CE DAYA COMPLETE HAUSA NOVEL

Zainura kuwa ta gaji da borinta ta jawo wayarta tare da danna Number zata kira Irfan suyi hira,kawai Ashe wayar Zainab ta kira,sai murya taji tace Hallo Zainura shegiyar ya gari,Zainura tace Wai Zainab ce?ae nice Zainura,dalla jeki gobe zan kira ki yau ba taku nake Zainab Bala'i ya sameni ta kashe wayarta,Zainab dama tasan iskancin Zainura kawai ta share tana dariya.
Irfan ta kira ya fara bacci kamar yar giya tace Hlo,Irfan yace baki bacci ba ya jikin zan  dubaki nayi tunanin kinyi bacci ne,Zainura tace banga ta bacci ba wlh nifa na gaji da boye boye zan bar wasiyya idan har kunga gobe ban warke ba to kawai Ku daura Min aure,Irfan yayi dariya yace Tsaya muyi magana ko dai maganin matan Salma kika Sha mata ne?ki fadi gaskiya idan ba haka ba sai kinyi wata guda kina wannan halin kuma ba aure za ayi miki yanzu ba,gwara ki fadi gaskiya a baki magani ya kashe karfin maganin da kwadayi ya kaiki kika Sha,Zainura ta saka kuka tace wlh shine nan tsinanniyace Salma tasan kwadayina ta ajiye dan nasha,Irfan yayi dariya tare da cewa sannu kinji,kwadayi mabudin wahala Zeena yanzu kinga Salma ita da mijinta ke kwadayi ya kaiki,me zan miki yanzu to? Zainura tace yo me zaka min ance ma bazan daure ba ne zaka dinga yiwa mutane habaici.

Kashe wayar yayi ya dinga kiran Na’im lokacin suna holewa da Salma bai ma ji kiran ba,haka ya musu knocking duk basu sani ba,Doctor Aliyu ya kira ya karanta masa matsalar Zainura,Doctor yace wacce me karambani ce haka iceko dai ba Aisha ta bace,Irfan yace ba ita bace kawai kayi sauri ka kawo magani,minti kadan a daren Aliyu ya aiko yaronsa da magani ya kawo,Irfan ya fita ya karba,ya dawo ya dauki Ruwa ya yiwa Zainura knocking da kyar tace a shigo tayi lakwas gaba daya ta birkice,tana zaune ta tara Lemon tsami a gabanta da wuka wai zata yanka ta matse ta shanye su tunda a kauye taga maza masu sha’awa suna Sha idan matansu sunyi tafiya shine itama ta ebo a fridge me uban yawa Allah ya kawo Irfan.
Kallo daya ya mata dariya ta taso masa yace Zainura yan mata har kin San irin wannan hadin magani Ashe,Zainura tayi shuru taji Kunya wai,ya mika mata magani da ruwa Sha ki bani cup dina na tafi,ta karba ta shanye tare da mika masa Cup din,yace tashi to ki koma bed din,Ba musu ta kwanta da yar rigar baccinta ta dan wuce gwiwa,Blanket ya rufa mata tare da kashe mata light yace kiyi addua ya kwashe lemon tsamin kana ya rufe mata kofa,ya maida komai kitchen yaje yaci gaba da baccinsa.

Zainura tana kwanciya tayi addua bacci ya kwasheta me dadi da nauyi,kwana tayi tana mafarkin Irfan yana making love da ita,suna ta Romancing zaiyi Sex da ita kenan ta farka gari Ashe ya waye har rana ta fito gashi akwai schl,takaici ya kuleta dama anyi Sex din dadin da taji a mafarkin nan ya wuce tunani,komawa tayi cikin bargo tana addua bacci ya kara kwasheta ta karasa mafarkinta ko ta kara na Romancing din da taji dadi,har kanta ta danne da pillow ko bacci zai kara dauketa amma har ta gaji ta tashi tare da shiga toilet harda yin wankan tsarki tare da yin wanka normal tayi brush da alwala ta gabatar da sallah.

 Yau baza ta iya zuwa schl ba sabo da maganin bai sake ta ba kawai bacci tasha ta koshi sanadiyyar maganin da Irfan ya bata,amma game da sha'awa da abarta ta tashi sosai musamman da tayi mafarki abin sai ya kara yawa, shuru tayi saman bed ba ajin ko motsinta kowa ya fito anyi Break babu Zainura,tunaninsu ko ta tafi schl yau ba Sallama,Irfan sai da yayi shirin fita sannan ya nufi dakin Zainura,ya hango ta kuwa tana kwance abinta,Yan mata ana Sallama bakya ji ne? Zainura tace na amsa mana,murmushi yayi me yasa baki je schl ba kuma ko wanka baki ba? Zainura tace yo ba sai da lfy ake komai ba,wlh indai ban warke ba bazanyi wanka ba,hmm amma ai kinsha bacci cewar Irfan,nayi bacci ban warke ba me kenan? Irfan yayi dariya yanzu dai Zeena Namiji kike so? Wannan maganin bani dashi tunda kwadayi ya kaiki ai sai ki ci gaba da hakuri,dole baza kije schl ba karki yiwa mutane shirme acan da ace ma kinje da tuni naje na daukoki hatsari ne a barki ki fita yanzu,

 Zainura tace Wai kai nace ma Namiji nake so da za dinga min habaici kana zagina? Yana dariya yace yaushe na miki Habaici harda zagi?gashi nan kanayi,wanne namiji zan so a duniya ni yaje can da abarsa kyauta Bana so,daga nace ayi min aure sai ace Namiji nake so,ah to so kake naso Mata,Irfan yace to ni da kike min masifa me nayi miki?Na fada Namiji dai kike so ku dama mata ko chat kuke hirarku bata wuce haka,Zainura tace ai gwara mu ku mazan fa wani ma ba Virgin bane,Irfan yayi dariya yace ae naji ai dai na tuba na daina kuma ko inayi bazan miki komai ba Bana cin Amana,Zainura tace ni yanzu ko gida da mota aka bani me zanyi da kai ai janka ma damuna zaiyi,ba gwara Hunaif ba,Tashi kiyi wanka yan mata ko kiss na miki kya farfado,Zainura taji kunya tace Allah ya shiryeka sai wanda ya biya sadaki,Ni ai wannan harkar bata dameni ba ko zanyi aure badan haka zanyi ba,Irfan yace uhm naga Alama ai to bari kiji yarinya duk rikicin duniya da maza da mata keyi a kansa ake yi ana ta gwagwarmaya,Zainura tace kune kukeyi sabo dashi banda ni,Irfan yace uhm naga Alama,je kiyi wankan yan mata,

Zainura ta kama Kuka ita kadai ba a mata komai ba, Irfan ya kyalkyale da dariya Allah sarki Zeena nasan me kikeji, Zainura tana Kukanta tace ni wlh ba yar Iska bace,Na sani ai Amma ke in ba Rashin ji ba me ya kaiki yan mata da Shan maganin mata,shi yasa ake saurin lalatasu yanzu mace tana tasha bata da aure saurayi yana taba ta sai ta biye masa baza ta iya control ba,Zainura tace nifa ka isheni daga fada ma abu ta karashe tana harararsa ai laifinsa ne da zai zo yayi Iskanci da ita cikin mafarki shine ya jawo taki warkewa,zama yayi kusa da ita,tace matsa ni bana son naji hucinka,hhhh dariya yayi sosai yace kamar wani abinci me Zafi, hannu ya mika mata Zainura tace kai matsar da hannunka hannun me,me zanyi da hannu,Irfan yace ki kawo naki ban son shashanci magani zan miki,Zainura tace da hannun?yace yes.

Kin bashi hannun tayi ya Mike tsaye tare da mikar da ita itama,bata zata ba taji yayi hugging dinta Zainura kamshi da dadi suka ratsata tayi luf harda kwantar da kai a kinjinsa,Shuru taji yayi kanta ta dago da niyyar taga me ya yake,a hankali ya daura goshinsa saman nata,hancinsu yana gugan juna ya hade bakinsu yana mata kiss me shegen Salo abinka da wanda yasan ta kan mata dama,Zainura taji azabar Dadi tayi luf a jikinsa,sai da ya dan dauki lokaci ya cireta daga jikinsa tare da rike babban yatsanta yasa abaki kamar abin arziki sai ko ya cijeta da karfi me zafi,ba shiri Zainura ta zaro Ido tare da kwace Hannun tana yarfewa,sam bata ma jin sha’awar Sai Zafi daya dameta,murmushi yayi yace na miki maganinta baza ki kuma ji ba,idan kika kuma Sha wlh wuka zansa ko Allura na cake miki yatsu,idan na dawo baki warke ba da Allura zan miki sai na tsire miki yatsunki.

Zainura ana Jin dadi ta koma jinyar yatsa har ya kumbura sai zogi yake,a hakan kuma tayi wanka ta shirya taci abinci,idan ta tuna abinda Irfan ya mata sai wani dadi ya kamata tayi ta murmushi tana rufe ido ta buga tsalle ta fada saman Bed,tayi sufa nan ta tashi ta kwanta ta rungumi pillow tayi tunani tana Jin dadi sai kuma ta bugi kanta tace to mene abin jin dadi,wani lokacin kuma tace shegiya Salma Ashe abinda take ji kenan,yan iska mata.

Koda Irfan ya dawo a Palo ya sameta tana kallon American film taji sauki kenan,kashe TV din yayi yace kiyi game ko ki kalli News sai anzo wajen Yin iya shege ki birkicewa mutane,Zainura tayi shuru domin ita kunya take ji ana cewa tana sha'awa.

Washe gari
a gurguje ta shirya tsaf cikin Uniform dinta green and white da dan ficicin hijab a jikinta ta fito,Mummy,Dada,Irfan fa Hunaif suna Palo suna ganin Zainura sai da kowa yayi dariya domin 9am ta wuce ma wai kuma zata je schl,ba wanda ya San dalilin makararta sai Irfan tunda kullum tana riga kowa tashi,Gaishesu tayi tare da komawa saman Dining taci chips and egg tasha tea ta Mike tare da cewa na tafi Mummy,Hunaif yace ashe lallai zaki ci duka yau,Zainura tace Wai karfe nawa ne?Irfan yace pass 9 fa,Zainura tace an kusa Break dai dai kenan,Mummy tace Drivers kaf basa nan na aikesu ba ko daya,Salma yau bata da Exam ni na dauka ma kin tafi,Zainura tace to yaya Hunaif ya kaini mana ko Irfan ko kuma a bani kudin Taxi tunda jiya fa banje ba, Mummy tace yanzu ke baza ki hakura ba sai gobe tunda makarar tayi yawa,Zainura tace ni dai zanje,Dada tace Allah kiyaye Hanya a bata kudin Taxi ta tafi,Mummy ta bata kudi ta musu Sallama ta wuce,Tana fita ta shiga Taxi,Sai da ya kaita yace Naira Dari biyar ta dinga masifa wai Ku komai dan ana Abuja a Ingila muke ne wai azzalumai ungo dalla kaje kai da Allah,ta fita gate a rufe sai masu Carrots rake,agwaluma,Aya etc suna jira ayi Break su shiga ciki, Zainura ta kalli Carrots ta dauke kai wai kunya ta matsa ma daga can nesa da shi.

Suka ga Zainura sai yanzu ma tazo taki shiga saida akayi Break sannan tabi rubibin yan talla ta shiga kamar Break ta fito,Me raken jiya yaje ya kai karar Zainura wajen PC,aka nemota a class taje hannayenta a aljihun wando PC yace ke me yasa kika masa asarar Rake kin San baza ki siya ba,Zainura tace ni din?yaushe?ni bana siyan komai a schl din nan kowa ya sani sai dai idan Hassana ya gani ai mu biyu ne a schl din nan Ni Zainura Usaina,ita kuma Zinaru take mantawa kayi pc,yau bata zo ba tana gida amma gobe idan tazo zan turota,pc ya zaro Ido  tare da cewa to kuzo tare na ganku Hassana da Usaina,Me rake yace karya take wlh itace,pc yace ayi hakuri da yara bari gobe su zo ai zai kure karya.

 Tunda Salma take bacci taki tashi har 12 Na'im ma haka,Sai da Mummy  taje da kanta zata gani ko lfy,Knocking ta Dade tanayi da kyar Na'im ya bude kofa daga shi sai Boxers,Mummy tace lfy kuwa tun jiya har 1pm ta kusa? Na'im yace lfy Mummy bacci ne kawai zamu fito ne,Mummy tace tunda lfy ai shike nan,yace lfy ta juya ya rufe kofar suka ci gaba da bacci yunwa ce ta tashesu 2 saura ya tashi Salma ta hanyar kissing dinta a goshi da saman tip na hancinta,idonta a rufe tana murmushin kunya tare da kara nutsewa a bargo,Dariya yayi yace Darlin yunwa nakeji tashi muyi wanka,kasa tashi tayi ta turo baki tace ni na kasa tashi,daukanta yayi ya gasa mata jiki sukayi wanka da Brush,shiryawa sukayi tsab,kamar wani Ango yasha shadda fara dinkin zamani yana sheki,Salma ma irinta sak ya sa mata dinkin mata na gaske,bata Jin dadi haka ta danyi kwalliya sama sama,kinyi kyau naga baki da lfy ba sai kin daura dankwali ba,da kansa ya zauna ya busar mata da gashin da Hand drier ya taje mata tare da gyarashi ya shafa mata mayuka da Hair spray ya mata parking dinsa yasha ribbom farare  ta yafa dan siririn gyale fari,yace Bana son kina rufe min gashin nan naki ina sonshi amma sai mun koma gidanmu  ko?
Salma tace Allah kaimu Mummy ce tace ba yanzu ba sai nan da 1mnth zamu koma gidanmu,bari Zainura ta dawo musha hira tunda yanzu na gano ta,Allah sarki Rahina,nan take Na'im ya kira Malam cike da murna ya sanar musu yanzu sun tuna zamansu tare komai ya dawo zasu zo next wk ma,Malam sabo da murna kasa magana yayi,Umma kuwa tana ta murna yaranta sun dawo dai dai sun Dade suna waya,lokacin Salma ta rike hannun Na'im pls ka kashe wayar haka yunwa nake ji ta furta kamar zatayi kuka,Dining sukaje suka ci abinci lunch domin breakfast ya wuce su.

Yau Irfan yana gida bai fita ba,driver ya tura yaje ya dauko Zainura amma sai yaki tura matashi Sabitu ya tura Baba Tsoho,yauma Zainura tana gaban me Aya zata siya wai amma baza ta bari ya auna mata ba sai dai ta dauki gongoni ta dinga tsince me kyau kadai tana zubawa har ta cika tin din ta juye a leda tanayi kuma tana ci,Me Aya yace ni bazan yarda da haka ba idan kin Zabe me kyau sauran fa?Zainura ko kulashi batayi ba ta gama ta bashi ashirin yace Hamsim kudin gongoni Zainura ta rike baki ta mika masa Hamsim ungo kar kace na cuceka ni sai dai a cuceni Bana cuta,dan kuna Abuja shike nan babu sauki ba rangwami,me Aya ya dinga masifa Zainura ta cuceshi,Baba Driver ba wasa ya dauko Zainura,Irfan ne kadai a Palo yau tana shigowa Hijab a hannu jaka a hannu Dankwali a hannu haka Sandal da safa ma duk ta riko su,Sallama tayi ta shige kitchen tasha ruwa ta fito sai lokacin tace Yaya Irfan wlh yau karfi nake ji Saura kadan na Zane wata,Mugunta ta tace ta motsa yau,yau Salma tana fitowa a kanta zan sauke ta,ina ma ace Aisha tana fitowa yau Allah da sai na ballata,Irfan yayi dariya shi dai Zainura tana birgeshi,yace Zeena tamu je ki cire Uniform din kiyi Sallah da wanka ki dawo ina jiranki hira zamuyi yau.

Ba musu taje tayi abinda yace ta Sha wanka yau kyan da tayi yafi na kullum ma,ta fito tana taku dai dai,Salma ce ta fito da sauri tare da fadawa Jikin Zainura tana ta murna tana Zainura dama kece na ganeki haka kikayi kyau Zainura,ina su Jamila wayyo ashe da ke muka taho memory dinmu ya dawo banza.

Zainura tace kai…ni wlh kin bani tsoro Yasin to Alhmdllh tunda ya dawo amma ya naga kina dangisa kafa kamar kafar kaza ta karye daya,tafiyar ki yau kamar ta agwagwa wani karuwancin ne aka samo za ayiwa me gidan? Salma tayi dariya Zainura baza ki canja ba wlh,kalau nake baki kula ba amma ba abinda ya sameni,ae ai tuwo ne a Idona Salma zaki raina min hankali waye Bai San halinki ba,me ya sameki dan Allah ? Tsaki Salma taja tace hmm dazu na bige a step ne,Zainura ta dan ture Salma kadan sai ga Salma ragwaf a kasa tayi zaman cin tuwo,an fama rauni taji Zafi kamar wasa ta saka kuka,Zainura ta dauka akasi aka samu ta balle ko wani abu,Salma ta dinga Kuka ta kasa tashi,Zainura tace Salma me ya sameki haka daga dan tureki,tana koka rin dagata Na’im ya fito zai dan fita wai ai ba lfy da sauri yaje ya dauketa kamar jaririya ya tafi da abarsa,

Irfan ne ya fito cikin shiri na gaske yasha kana nan kaya larabawa kenan,Zainura ta kafeshi da Ido yana saukowa daga step,lets go yan mata,ina zamuje?yawo mana kinyi kyau ne zan kai ki yawo,Mummy ta sanarwa zasu fita da Irfan ta musu a dawo lfy suka tafi,Zainura an fara wayewa fa harda sa takalmi me tudu,dagwas dagwas ta fito,Irfan yana kallonta yana murmushi harda rike pose yan mata,tana shiga motar ta canja murya ta wani makaleta can kasa tare da cewa what are u waiting for? Da Sauri Irfan ya kalleta tare da sakin murmushi,Ya Irfan wai ba yaya Ya Irfan ma,yace uhum ina jinki muje mana,ya fara driving suka bar gidan,Wayar Zainura tayi kara a saman cinyarta tana dubawa taga Classmate dinta ne Najeeb, tayi murshi ta daga Hello Naji Boy Naji Boy,Najeeb yace ke ban son sunanan fa, gobe weekend zamuzo gidanku ni da su Ahmad,Allah ya kaimu Hanifa da Fatima tare zamu zo dasu,Zainura tace Allah ya kawoku lfy,sai da sukayi ta hirar schl sannan ta kashe wayar tana Murmushi ta juyo da niyyar Bawa Irfan labari sai taga kamar an aiko masa da mutuwa ya bata rai.

Me ya faru? Irfan cike da masifa yace dama Maza ne frnds naki? Zainura tace yo mate na schl ba dole ayi mutunci ba ka taba ganin anyi schl tare ba a mutunci,ai mu hirarmu muke ci sit dinmu daya da Najeeb da Hanifa da ni,haka Fatima da Ahmad da Nusaiba,haka fa ake Zama a ajin makarantar wai mata surutu sukeyi shine ake samu haka,Salma ita tana da aure sit dinta daban ita kadai a ajinsu,Irfan yace amma baki fada min ba sai yanzu?kai da ka kaini da hannunka schl din ai tunanina kafi ni sani mu yanzu hirarmu muke muna Shan dariya da dadi schl din,Irfan yace Monday new schl za a canja miki iya mata,Zainura tace ni dai a barni a wannan nafi sonta,sabo da takaici ma Irfan shuru yayi,next wk za muyi Hutu zanje kauye naga Baffa da Ummanmu da frnds dina a can zan gama Hutu na,Irfan yace tare zamuje harsu Na'im kuma gaba daya zamu dawo harda ke yarinya,suna ta hira har suka je suka dawo ya mata siyayya ta gaske,tsaraba sosai ya mata wanda zata tafi dashi,da kuma nata da shi ya siya mata na amfaninta,

Sunzo layin bra da panties Zainura tana rike dashi kamar yar kanwarsa ta rufe ido wai baza ta iya gani ba,Irfan ya jawota ta karfi yana dagawa wannan zatayi musu? Zainura tace tab kuma haka kawai sai na kwashesu na zuba a ciki ni wlh bazan iya ba,panties kawai zaka siya min ni Allah baza zuba su cikin wannan abun ba,Irfan ya dinga dariya tare da cewa sai kace wani kaya Allah ya shiryeki, ameen tace,haka kawai yayi Hasashe ya iba mata da yawa,suka je layin pad nan ma Zainura tace ita fa bata period baza ta dauka ba,yace karya kike,wai ke yaushe idonki zai bude ne u better shine ur eyes.

Da kansa ya jidar mata pad din wai ita baza ta taba da hannunta ba,ledojin da ya miko mata ma tace Allah indai da bra a ciki baza ta dauka ba,ga me pad ma a ciki harda cewa yanyanyanyan kayan kazamai bada ni ba.

Sunzo zasu fito sai ga Rayhanat budurwar Irfan da tayi zuciya ta daina kulashi akan kudin man mota,Ta gansu tare kishi ya cika ta,Zainura ta ganeta ta kara rike Irfan kam tace muje wajen Ice cream ta janyeshi suka canja layi,Rayhanat tayi kwafa tare da cewa wlh sai taci uban Zainura zanyi maganinta.

Yau kimanin 5days kenan Na'im bai kara yin wani abu da Salma ba yana jira ta warke,yau Friday yaune kuma sukayi shirin Tafiya Katsina gaba dayansu banda Aisha dake kulle a daki yan aikine zasu Kula da ita har su dawo,booking flight akayi da komai,Zainura da Irfan suka hada kayan da zasu tafi dasu,Na'im  da Salma Hunaif su Mummy duk sunyi shiri Har Dada.

Zainura da yamma duk sun shiga mota za a kaisu airport ta koma cikin gidan da gudu ta dauko manyan Bread irin na Oasis biyu da Apples guda goma a leda,Ga wasu flasks manya har uku daya doya da kwai ce ta soya wai duk tsarabar kayan dadi ce,daya farfesun kaji,daya kuma dankalin turawa chips yasha abubuwa ciki,Ta shirya abunta a katuwar leda,Mummy suka dinga dariya domin basu San ta shirya abinta bama,da asusun kudin makarantar da take Tarawa domin bata kashe kudinta Tarawa take zata kaiwa iyayenta wai.

Lfy suka sauka a birnin Katsina,An kawo musu motoci da Drivers aka kaisu har kauyen su Zainura,ba wanda ya kai Zainura Murna sai Salma da Na’im,Mota na tsayawa a kauyen Zainura ta fito tare da shakar Iska,Salma da Na’im basu kula kowa ba suka shige gidan Malam suna kwada Sallama,tuni Su Zainab,Jamila da sauran Frnds dama sun San Zainura zasu zo da sauri suka taho yuuuuu kofar gidan Malam.

Next page zamu Sha hira za a ci dariya Zainura da Frnds ga labari,Salma da Na’im da Iskancinsu hmmm.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button