KAUNARMU COMPLETE HAUSA NOVELS

KAUNARMU COMPLETE HAUSA NOVELS

daɗa faɗaɗa murmushin dake saman fuskar ta fifi tayi tana jin dadin ta samowa aminiyar yar uwar ta maslaha mafi sauki kuma tayi kokari akan damuwar yar uwar nata..

Dagowa Hamida tayi ta shafa fuskar fifi tana kara gode mata da taimakon da ta mata sannan ta kara jaddada mata zata sanar da aminiyar nan nata shawarar kuma zata fada mata cewa nata yaruwar ce ta bata wannan shawarar..

Daga karshe bayan ta ma fifi godiya ta tashi da nufin fita sai kuma ta juyo ta kalle ta da murmushi mai ratsa zuciya sannan ta ce
“Na gode yar uwa ta Allah ya bar zumunci ya bar mu tare ba zan taba manta wannan abin da kika min ba yar uwa ta,InshaAllah wataran zan rama maki wannan kyakyawar ranar da kika min,kafin nan,ki koma baccin ki kin san daddy ni zai rike in har baki sami isasshiyar hutu ba

dan haka go back to bed twin sis sai mun hadu a wurin breakfast anjima”!gyada mata kai fifi tayi daga haka Hamida ta juya tana mata wani irin kallo..

Har cikin zuciyar Mufida ba karamin jin dadi tayi ba ganin ta warwarewa yar uwar ta damuwar ta,dama Hamida zurfin ciki ne da ita dan kullum shiru shiru haka take har takan yi mamakin yadda Allah ya halicci zuciya irin ta Hamida kamar bata da damuwa dan bata cika shiga sabgar da ba nata ba bayan ita da take yar uwar tama kan ta ita din irin mutanin nan ne da ake kira da extrovert masu son magana

Hamida kuma ta kasance kullum shiru sai abin da ya shafe ta take saka kan ta…

Komawa tayi ta kwanta dan cigaba da baccin dan dama bai ishe ta ba,bata dade ba baccin ya dauke ta..

A nan fannin Hamida kuwa duniya sabuwa dan ta samo abin da take so kuma ta samo facts da shaidar da ko da tace ga abin da take so babu yadda yar uwar ta zata ce ta mata kwace dan da kan ta ta bata shawarar kwato abin da yake nata ne..

Farincikin ta a ranar baya misaltuwa dan kasa bacci tayi har gari ya gama wayewa tayi abin da zata yi,wani hali da ba nata ba sai tayi sa a yau wato cancaɗa kwaliyya na zamani irin na yan mata masu ilimi da wayewa,shigar mutunci tayi ta dohuwar Asmaa abaya plain black mai kyau da tsada,tayi rolling veil din abayar ta saka loafas mai taushi ta fito kamar wata wacce bata taba zaman damuwa da kadaici ba…

Bata tsaya duba fifi ba dan ta san an zo an dauke ta zuwa dinning table,haka da fara’ar ta ta sauko ai kuwa ta fara hango su suna breakfast din su cikin walwala,ɗage kafadun ta tayi alamar abin bai dame ta ba ta karasa saukowa kasar..

Da zuwar ta ta sa hannu ta ja daya daga cikin kujerun dinning din ta zauna tana mai gaida su(cikin jama’u)..

Mamaki Ammy tayi ganin walwala a fuskar ta yayin da Hajja kuwa ta tsaya tunanin hala wa ya kirawo ta zuwa breakfast din tunda sun ga alamar ita din mai son kadaicewa ne ita kadai ko me ya faru yau ta zo tayi joining din su..

Shi kuma Khalid kallon ta yayi yana yaba kwalliyarta har ya furta mata..
“You look beautiful “wani dadi ne ya mamaye zuciyar Hamida amma tsabar rike aji irin nata sai ta dan murmusa kawai ta ce
“Nagode brother”.daga haka ta kalli fifi tana mata faffadar murmushi itama ta maida mata da martani..

Abinci suka ci cikin jin dadi da walwala as family har suka kammala babu tashin hankali bayan yar hirar da aka rinka yi da fifi ba a sako ta ciki ita kam ko a jikin ta dan damuwar su yanzu ta maida shi gefen hagun ta ta dabbaƙa damuwar Khalid a gefen damar ta dan ganin bata yi sake ta rasa shi ba…

Sallamar ta fifi tayi akan zasu tafi yawon bude ido tare da Khalid har ta mata tayin tafiya amma ta ce a’a su tafi sai dai kar su manta su dau hotuna da dama dan in sun dawo ta kalla..

Allah sarki fifi sai ta dawo ta rungume yar uwarta tana mata sai sun dawo ita kam ban da murmushi babu abin da take mata,bayan tafiyar su ma bata koma dinning din ta zauna ba sai ta sallami su Ammy akan zata tafi kallon gidan tare da ma’aikatan gidan,basu hana ta ba suka kirawo wata amintacciyar ma’aikaciyar gidan suka umarce ta da ta raka Hamida su zagaya gidan..

Daga haka ta masu godiya suka fita,barin su Ammy da Hajja tayi cikin mamakin dalilin walwalar ta na yau amma da yake bata wani yi jiki da su ba sai suka share kawai suka cigaba da sabgogin su…

MamuhMamuhgee

9

Sannu a hankali yar aikin nan ta rinƙa zagaye gidan nan da Hamida tana nuna mata sashe sashen dake cikin gidan ko wanne kuma sai ta mata bayanin mammalakin sashen, dan akalla mai aikin wanda aka fi sani da mama hasiya ta jima tare da su a cikin gidan zata kai sama da shekaru ashirin da shida zuwa da bakwai tana aiki a gidan kuma bata zamba da cin amana wannan ya daukaka darajar ta a idanun yan gidan ya sa aka yarda da ita har in abu na sirri ya taso ana iya yi a gaban ta dan an san sirrin nan zai kasance a killace..

Wani sashe suka zo mai bala’in kyau da tsari wanda bata taba ganin irin sa ba sai ta ja ta tsaya ahankli ta kalli matar ta ce
“Mama hasiya nan kuma sashen na waye ne?amsa ta bata kai tsaye ta ce
“Wannan sashen shine sashen ɗan uwan ku Khalid kuma tun yarintar sa har kawo girman sa a nan sashen yayi sa”..

Gyaɗa kai Hamida tayi tana tunanin ta shiga ne ko a’a, wani tunani tayi sai tayi shiru ta kyale ta dai cigaba da ƙare ma sashen kallo.

Muryar matar ne ya fargar da ita a inda take tambayar ta ko tana son a bude mata sashen ne ta shiga..

Tace “A’a mama hasiya,bana bukatar ganin yanayin sashen a yanzu,amma watarana nice aciki. cikin ranta tace ba iya gani zan yi ba har shiga cikin sa zan yi in zauna na har abada dani da khalid.
“da fara’a a fuskar ta ta ida maganar wanda ya so ya ɗan ɗaurewa mama hasiya kai ganin kamar jefa magana Hamidar tayi cikin magana amma lura da tayi da yanayin Hamidar na ba mai son hayaniya bane sai bata daukaka maganar ba ta basar..

Daga haka suka cigaba da bin sauran sashe sashe na gidan suna dubawa suna ƴar hira kaɗan kaɗan wanda a cikin hirar ne Hamida ke ƙaruwa sosai dan kusan a 100% ta san kusan 60% na halayyar ƴan gidan musamman inda ta fi buƙatar sani wato fannin labarin rayuwar Khalid dan shine ta fi bukata sama da komai..

Suna zuwa wani sashen kuma sai Hamida ta ja ta tsaya tana kallon mama hasiya tambayoyi cike taf a bakin ta da zuciyar ta amma bata furta ba tayi shiru..

Fuskantar hakan sai mama hasiya tayi murmushi dan ita kan ta tana da ɗiya mace mai hali kusan na Hamidar wato halin kau da kai ga abin da ba’a saka ta ciki ba kuma bata tambaya in har ba abin ya zame mata abin dole bane da zata sami ƙaruwa ba,dan haka sai ta hau yiwa Hamidar bayanin wannan sashen da mamallakin sa.

“Wannan shine sashen babban ɗan gidan nan kuma jigo jagorar gidan nan,magaji kuma masanin sirrin cikin gidan nan wato marshall MUHAMMAD SAHEEB kuma a halin yanzu baya ƙasar yana can South Africa inda ya fi yawan zama dan business din sa da kusan komai na rayuwar sa sun fi ƙarfi a can ɗin,amma duk lokacin da ya kawo ziyara nan ƙasar toh a nan sashen yake zama”!!

gyaɗa kai kawai Hamida tayi dan ko ba a faɗa mata ba ta san wannan shine old eldest son ɗin Ammy da daddyn su ke basu labarin sa,lallai wannan tsohon shine wai har yanzu yana zaune awata ƙasar gaskiya su Ammy sun mai sake da yawa..

Ko da mama hasiya ta kuma yi mata tayin shiga wannan sashen sai ta ce a’a bata so,a zuciyar ta kuwa faɗi take ita me zata shiga ta gani a sashen tsoho sama da tarikicen kaya irin tasu ta tsoffi,sashen yaro mai zamani ma wato Khalid an mata tayin sa bata karɓa ba sai na wannan da ta san da ta shiga zata fito da babbar story da zata faɗawa fifi in ta dawo su yi dariya dan ta san fifi ta fi ta wauta tana iya cewa zata zo sashen da kan ta dan ganin me ke ciki ko dan ta sha dariyar mai dalili..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70Next page

Leave a Reply

Back to top button