THE WORLD MAN (NAMIJIN DUNIYA) COMPLETE NOVEL

Ɓangaren Namijin duniya ko yi yayi kamar besan da mutane a gurin ba hakan baƙaramun ƙara ɓatawa su Meemah da sukayi mutuwar tsaye rai yayi ba shiko ɗan gogan cigaba yayi da caring ɗin abarsa kamar wata matarsa saurin yin baya su Feenerh sukayi cikin tsananin ɓacin rai yayinda Meemah ma tabi bayansu zuciyarta na tafarfasa ta buga musu ƙofa da ƙarfi .
Mutsu-mutsu takeyi cike da tsananin ɓacin ran abinda yayimata a gaban mutane yayinda wasu hawaye suka shiga sintiri a kumatunta a zuciyarta tashiga tinanin wanne irin kallo mutanen nan zasu yimata ƙin sakinta yayi hakan yasa ta ƙara lafewa a ƙirjinsa wani ƙasaitaccen murmushi ya saki ganin yadda ta sakankance taƙara lafewa a jikinsa hakan yasa cike da mugunta ya hankaɗata ta faɗi ƙasa jikake ƙass ƙarar kashin ƙafarta yayi ƙara yayinda lokaci ɗaya ƙafar ta kaure da zugi ga tsamin da tayi cikin yanayi na jin zafi tace”ochhhhhh”.
murmushin mugunta a gadarance yace”matsamun da wannan ƙazamun jikin naki dayasha taɓawar ƴan bariki kin wani lefe jikin mutum kina yin pretending kamar wata ta Allah bayan kuma a zuci ba haka bane kina wani kakkare jiki kamar wata uwar mata mezan gani abu kamar kwan kurciya”.
yaƙarasa zancensa tare da ƙara shan mur kamar bashi yayi maganar ba ya wani ƙara haɗe rai ɗaga idonnan da zeyi sukayi ido huɗu da!!!!!!!!!
Sorry my fans kuyi haƙurin da rashin typing yafaru ne saboda wani uzuri daya tasomun me ƙarfi amma yanzu na dawo normal zamu fara wasa kullum insha Allahu zaku fara samu update sau ɗaya ko biyu a rana matsawar zaku bani haɗin kai ta hanyar suburbuɗamun comments and votes zaku sha mamaki domin yanzu zan tsoma hannu cikin labarin dan shimfiɗa mukayi yanzu zamu fara wasan.
Votes and Comments
Plz share to others
_*Daga Alƙalamu???? *MAN OF THE WORLD*
(NAMIJIN DUNIYA)
MALLAKIN
REAL EESHOW
BOOK 1
PAGES 2️⃣5️⃣➡️2️⃣6️⃣
Dasu Ahmad da sun daɗe suna kallon ikon Allah abinka da miskilin mutum se ya wani basar kamar besan abinda ke faruwa ba ya wuce ya zauna a kujerar office ɗinsa yashiga duba takardun dake aje akan table ɗinsa jawo system ɗinsa dake gefe guda yashiga operating juyawa su Adam sukayi cikin sauri ɗinta ɓangaren Inteesar ko kasa motsi tayi saboda tsananin azabar da ƙafar kemata lokaci ɗaya hawaye suka wankemata fuska cikin office ɗin ba abinda kakeji se shashekar kukanta ɓangaren Namijin duniya ko jin kukanta yike har cikin ransa ya rasa dalili a zahiri seka ɗauka wani mahimmin aiki yikeyi a system ɗinsa a cikin zuciyarsa ko jin wani irin abu yakeji dangane da kukan da takeyi .
Jiyayi duk be kyautaba abinda yayimata zuciyarsa ce tashiga rayamasa idan Rahamansa wani yayiwa haka zeji daɗi zuciyarsa ce tabashi amsa da”a’ah “.
wata zuciyar ce tace”to ita meyasa kake yimata haka?”.
wata zuciyar ce tace”ka rabu da ita ai rashin kunyarta ce ta jamata cigaba da aikinka kawai”.
yana cikin wannan zancen zucin yaji sallamar su Ahmad ba tare daya ɗago ya kallesu ba yace”wa’alakumus salam”.
yaƙarasa amsa musu tare da duba wani file dake gabansa kamar da gaske ya wani ƙara haɗe rai dan karsu yimasa magana ganin haka yasa suma basu bi takansa ba suka nufi inda Inteesar take cikin nuna basu ga duk abunda yafaru ba Adam yace”subahanallah Aishatu meya samu ƙafar taki haka naga ta kumbura Abdallah meyafaru da ita haka”.
ba tare daya ɗago daga danna system ɗin da yike ba kamar wanda yake wani abu me mahimmanci yace”ka tambayeta man nima yadda kaganta haka na ganta”.
saurin juyawa Adam yayi gun Inteesar cike da takaicin amsar rainin hankalin da abokinsu ya bashi karo na farko a rayuwarsu da sukaji tausayinta cikin tausayin halin da take ciki Adam yace”meyasameki Aishatu “.
cikin siriryar muryarta dake nuni da tasha kuka tace”gurɗewa nayi Sir”.
taƙarasa zancenta kuka na niyyar cin ƙarfinta yayinda takejin wata muguwar tsanarsa na ratsa zuciyarta ganin shi yajimata ciwo amma shi ko ajikinsa sosai tabasu tausayi cikin sigar lallashi Ahmad yace”sannu kinji bara na kira Hauwah ta temakamiki semu kaiki asibiti naga ƙafar ta kumbura sosai”.
cikin sanyin murya tace”toh Sir nagode”.
“bakomai”.
nan yashiga dialing number Hauwah bugu ɗaya ta ɗauka cikin girmamawa tace”salamu Alaikum”.
“wa’alaiki salam ki sameni a office ɗin Abdallah”.
“toh sir”.
nan ya kashe ko minti goma ba’ah yiba Hauwah tayi knocking buɗemata Adam yayi haɗe da cewa”temaka mata kisamun ita a mota mukaita asibiti naga ƙafar ƙara kumbura takeyi”.
yaƙarasa zancensa yana mata nuni da inda Inteesar ke yashe se lokacin ta lura da Inteesar daketa faman kuka cikin tashin hankali ta nufi gunta tana cewa”meya sameki Besty”.
kasa magana Inteesar tayi kuka ya kuɓucemata se nuni takemata da ƙafarta sosai Hauwah taji tausayin halin da aminiyarta take ciki tashiga ƙoƙarin temaka mata .
Kasa ɗagata tayi hakan yasa Ahmad nufar gurin yana cewa”bara na temaka miki”.
be ƙarasa zancensa ba yaji Namijin duniya ya bangajesa ransa a mugun ɓace yayinda yaketa faman huci yace”muharramarka ce da zaka taɓatamata jiki meye alaƙarka da ita ?”.
cikin tsananin ɓacin rai ya nufi gurin da Inteesar take yashe tana kuka wani guntun tsaki yayi sannan yasa lallausan hannunsa ya ɗauke ta cak kamar wata baby ya wuce fuuu baki sake suke kallonsa har ya ɓacewa ganinsu sauke numfashi gabaki ɗaya sukayi Adam ya kalli Ahamad suka saki wani shu’umin murmushi wanda su kaɗai sukasan ma’anarsa Ahmad ya kalli Hauwah gani yayi duk tashiga damuwa yace”ki kwantar da hankalinki ba abinda zemata nasan asibiti zekaita kya iya tafiya gida nasan shima idan sun dawo kaita zeyi”.
“toh Sir”.
nanta fice tabarsu ba abinda sukeyi se aikin murmushi.
Ɓangaren Namijin duniya ko yana fita ya nufi gurin haɗaɗiyar Bugatti ɗinsa sabuwa dal da ita kafin yaƙarasa securities ɗinsa sun buɗemasa motar back seat ya ajeta jin yadda take kukane yasashi sakin wani dogon tsuka ya juya ya nufi gurin driver security ɗin dake niyar shiga mazaunin driver ya dakatar da hannu yace”nizanja ku zauna ku”.
“okay sir”.
nan security ɗin ya matsa ya shiga harya fara tada motar sekuma ya kashe yayi tsaki ya fita ya zagaya inda take yasa lallausan hannunsa ya ɗauketa cak ya buɗe gefan me zaman banza yasata ya zaga yashiga mazaunin driver yaja motar da gudu ya cilla hancin motarsa titi shiru ne ya biyo a tsakaninsu kowanne da abinda yike saƙawa a cikin zuciyarsa ita tana tinanin itako meta tsarewa wannan mutumin dahar ya tsaneta haka shikuma yanajin duk beji daɗiba ganin yadda tayi ƙasa da kanta tana shashekar kuka ta wutsiyar ido ya saci kallonta gani yayi tana nan dai a yadda take sosai tabasa tausayi amma dake miskilin gaskene se ya nuna be damu da halin da take cikiba sema taɓe baki da yariƙa yi a haka har suka isa wani tanƙamemen na masu faɗa aji a ƙasa me suna A2 bakin tanƙamemen parking space ɗin hospital ɗin yayi parking tare da juyar da kansa ya kalleta tana nan a yadda take tsaki yayi ya buɗe mota ya zagaya inda take ya ɗauketa kamar wata baby yayinda ƴan hospital ɗin se bashi respect suke ya nufi wani room da ita yana shiga haɗaɗen room ɗin ya kwantar da ita akan wani haɗaɗen sick bed wanda inkana kai seka ɗauka na gidane gidanma wanda ya amsa sunansa gida mamakine ya kamata seta make gefe guda kuma wani mahaukacin tsoro ne ya dirarmata ganin irin aljannar duniyar gurin da take yana nan tsaye kanta sega wani Doctor yashigo bayan sun gaisa yayimasa bayani abinda ya sameta amma becemasa shiya jimata ba nan yashiga bata emergency care domin ƙafar ta kumbura sosai.
FEENER POV
Suna fitowa daka Office ɗin Namijin duniya Zuby ta dafe shafaffen ƙirjinta tare da kallon Feenerh cikin tsananin baƙin ciki tace!!!!!!!!!
Votes and Comments
Plz share to others
Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo._n ƴar Mutanen Gwarzo.*???? *MAN OF THE WORLD*
(NAMIJIN DUNIYA)
MALLAKIN
REAL EESHOW
BOOK 1
PAGES 2️⃣7️⃣➡️2️⃣8️⃣
"Gaskiya wannan tsinanniyar yarinyar anyi tambaɗaɗiya daka gani sede in gurin boka taje banda haka banga abinda Namijin duniya ze kalla a jikinta ba bare har yayi sha'awar aurenta muna ganinta saida kaji saida kaji ashe har shanu ma siyarwa take".
“aina faɗamiki dama ƴar iskar yarinyar nan ta wuce duk inda kike tinani domin ba Allah a tare da ita dakanan direct mu wuce gidan Ummah mu tafi gurin Boka”.
“aiko dai kema kince wani abu domin abunnan gagarumi ne”.
“eh mana hatsabibiya ce yarinyar ga kuɗin dana ciro zankai gidan adashi mutafi dasu kawai gobe na ciri wasu inkai”.
“toh muje ammafa yarinyar nan koda ansamu anɓan bareta daka jikinsa aciki wasa tunda ita yafara runguma kafinke amma dai nima zaki bani passentage ɗina daiko”.
“gaakiya baki da haƙuri Zuby kinsan dai ai zanbaki ungoni”.
“ai gaskiya ce najiɗin bani da haƙurin indai akan kuɗine gwara kibani haƙƙina”.
a zuciye Feenerh ta dankawa Zuby kuɗin tace”gashinan sarkin zalama”.
“naji ɗin kome zaki ce kice ɗin ina ganin kawai mu kira Ummah ta fito titi mu ɗauketa mu wuce kawai ina ganin tafiyar zata fimana sauri”.
“ok kirata da hanzari dan Allah”.
kamar yadda Zuby tace hakan sukayi suka kira Umman Zuby suna isa bakin layinsu suka ɗauketa suka tafi.