A SANADIN GROUP COMPLETE HAUSA NOVEL

A SANADIN GROUP COMPLETE HAUSA NOVEL

A short novel based on true life story

Page 35_40

Yusuf sai da ya farfasawa Ton g jiki,da dorinar hannunsa Ton G sabida wahala ma kasa kuka yayi gwallo ido kawai yake yana wani zillo,wurgi Yusuf yayi da dorinar,ya cakumo wuyan Ton G,yasa k'afa ya taka mishi gabansa,wani wahalallen ihu Ton G yayi,yana "kayi min rai zaka kasheni"Yusuf da ji yake kamar ya kashe  Ton G k'ara shak'o wuyansa yayi yace "ai kashenka zanyi Dan banga amfanin rayuwarka ba tunda matan mutane kake bi,as small as you are," wani irin takaici ne ya rufe Yusuf,yakai kallonsa bakin k'ofa yana kallon Manal data rakub'e sai kuka take yi kamar ranta zai fita,"Manal kinyi mugun asara arayuwarki ki rasa Wanda zaki nema sai kanin kaninki,yanzu wanan Affan bai girmeshi ya fishi cikar ido ba,wanan ramamen da mai yafini Manal? Da yaranki da komai,dawane idon zaki kalli yarana in suka girma suka ji abinda kike aikatawa,I gave you all my trust,not even in my dream na tab'a kowawa zaki ci amanata, tunda na aureki ko hanun wata mace ban tab'a rik'ewa ba,duk 'yan matan da ke sona  suke kawo min Kansu,zagi da rashin mutunci ke rabani dasu, idan ni namiji zan iya killace kaina ma kame kaina daga kowace mace,duk da inada damar da zanyi duk iskancin Dana ga dama,banyi ba sai ke da kike mace,Manal ki ringa d'aukar hoton jikinki kina turawa yaron da da anyi miki auren wuri zaki iya zuciya ki haifeshi,kiyi wa kanki video kina tura mishi kinsan mutane nawa ne suka ga jikinki,kinsan mutane nawa ne suka ga tsaraicinki? Kinsan irin wanan yaron sune ke watsa irin shirmen a social media?Manal how can I Eva forgive you,Manal taya ya zan iya cigaba da zama dake duniya tagama gane min sirrin danake ganin a lullub'e yake,nikadai nake gani,bakayi exposing kanka  bama ana had'a maka sharri da computer ballantana akai ga kayi exposing kanka,mutane basa ajiye Abun alheri,sun fi ajiye abun sharri,duk ranar da kayi wani abun ayita yad'aka"

“Innalillahi wa inna ilahi rajiun na shiga uku na lalace ???? S????N????DIN Group na janyowa kaina Masifa wayyo Allahna zuciyata Tijjani mai ya shigo dakai rayuwata,Hajja Kaltume mai ya shigo dake rayuwata,kinsa na ha’inci mijina kinsa na tonawa kaina asiri,mai zancewa ‘yayana insuka girma suka ga hotona na yawo a media wayyo shaidan baka min adalci ba daka ci galaba akaina,kaicona dama hanun agogo ya koma baya, dama mafarki nake yi”

Manal tace cikin matsanacin kuka tana birgima,Ton G kuwa zare ido kawai yake yi Dan irin shak’ar da Yusuf yayi mishi ya fara jiyo kamshin lahira,Yusuf dawo da kallonsa yayi kan Ton G, yace ” Dan ubanka mai ya had’aka da matata?ya akayi kuka had’u?mai kazo yi gidana”?

Ton G cikin tsananin tsoro da firgita yafara kuka yana “baba Dan Allah kayi min rai wlh ban tab’a iskanci da matarka ba sharrin shaidan ne,” wani Mugun Naushi Yusuf ya kai wa bakinsa sai ga hokaransa guda biyu a kasa,ihun wahala Ton G yayi ya zube akasa,Yusuf ya k’ara shak’o wuyansa Dan Zuciyarsa wani irn zafi take yi kamar ruwan zafi aka kwara masa, Dan Ji yake kamar ya kashe Ton G,”ka amsa min tambayata kafin na kasheka wlh yanda nakeji zan iya luma maka wuka idan ka d’auka wasa nake ina z zuwa,cika shi yayi ya d’auko wata sharbebiyar wuka,Ton G yana ganin wukar yace ” Kulli nafsee zaikatul mauti shikenan na zama margayi Hajja kaltume Ashe mutuwa ce take kirana

“Yanzu nan kafara amsa min tambayoyina,kana yimin karya zan luma maka wukar nan and I mean it,I want nothing but the truth,kaji mai nace ko” ? Yusuf yace a tsawace yana ajiye wukar a gefensa”

Da sauri Ton G ya girgiza masa kai yana kallon wukar dake kyalli a gefensa,

Yusif“Ya akayi kuka had’u da matata”

Ton g“Alhaji Dan girman Allah ina gaya maka gaskiya bazaka kasheni ba”

Yusuf “Indai ka gayamin gaskiya bazan kasheka ba”

Ton G“Hajiya Kaltume ce ta had’amu”

Yusuf” wacece Hajiya Kaltume”?

Ton G “wata Hajiya ce da take had’a matan aure da samari”

Yusuf” ya akayi ka had’u da ita Hajiya Kaltumen”?

Ton G” wani abokina ne ya had’ani da ita “

Yusuf“interesting inaso kamin takaitaccen bayanin wanan hark’ar taku ta Neman matan mutane”

Ton Gwani abokina ne ya had’ani da Hajja Kaltume a lokacin banida ko sisi buga buga nakeyi,ban tab’a zina ba sai ta dalilinta Dan kud’i take kashewa yara irinmu,su biya mata bukatar ta,to da haka muka maida abun Sana’a Matayen da mazajensu basa iya biya musu bukatunsu,kud’i suke kashe mana sai mu biya musu bukatarsu”

Yusuf” dakyau shekararka nawa kenan kana Neman matan aure suna biyanka? Daka lokacin da ka fara wanan. Sana’ar matan aure nawa ka Neman”?

Ton G shekarata biyu kenan, ,matan aure uku kawai na nema na tab’a aikata zina dasu,wlh Alhaji sauran duk ta waya muke had’uwa kamar dai yanda muka had’u da matarka”

Yusuf” ita Manal tana kashe maka kud’i ne”?

Ton G eee tana kashe min Kud’i tana turamin kud’i ta account tana kuma saka min kati

Yusuf“da kyau kace kai take kashewa kud’ina, yanzu videos da hotuna da take tura maka dawa dawa kake turawa su gani”?

Ton G ‘Alhaji wlh ban tab’a” ganin Yusuf ya d’auko wukar dake gefensa ne yasa yayi sauri yace zan” fad’a maka gaskiya wlh Alhaji karka kasheni”

Yusuf ina jinka ka kara gingin yimin karya zan Luma maka wukarnan,banida asara iyayenka basu da asara tsaya ma tukuna kana da iyaye kuwa”?

Da sauri ton g ya girgiza kansa yace “bansan kowa nawa ba ahanun wata mata na girma ta ce tsinta ta akayi “

“No wonder Ashe shege ne kai” ina jinka dawa dawa ka turawa hoton Manal da Video”?

Ton g “a group nake turawa abokanai na masu irin hark’ar”

“Inalillahi wa innalilahi rajiun na shiga uku na wayyo Allahna Allah ya isa tsakanina dakai wayyo Allahna Allah ya tsine maka albarka” Manal tace tana nufarsu da gudu,da k’afa Yusuf ya maidata ta zube akasa

Yusuf ” ina jinka dama haka kukeyi kenan idan matan sun turo muku video ko photo turawa junanku kukeyi”

Ton g eee grp ne damu SEX NIGHT CLUB duk Wanda buduruwarsa ta tura mishi hoto ko video sai ya tura grp d’in,agani, Idan ta had’u zamu yaba muce ayimana hanyarta muma mu d’ana”

Yusuf da kyau Ku nawa ne a grp d’in”?

Ton gmu shidda ne a grp d’in

Yusuf “bani wayarka nagani”

Ton g cikin rawar jiki ya zaro wayar jikinsa na rawa Dan gani yake yana masa gardama zai Luma masa wukar,hodan daya fad’o daga Aljihunsa Yusuf yabi da kallo adaidai lokacin daya ke k’arbar
Wayar daga Hanunsa,d’aukar hodar yayi yace mishi “wanan fa”

Ton G cije lebb’e yayi yace ” hod’a ce da muke badawa matan da suka k’i bamu had’in kai su fita daga hayyacinsu,mu samu biyan bukatarmu”

Yusuf kenan Manal kazo ka badawa Hodan nan sabida kasamu biyan bukatarka,meyesa kataho da hoda ba ita ta nemi kazo ka biya mata bukatarta ba”?

Kuka Ton G ya fashe dashi yace, Wlh Alhaji ba ita bace,Hajiya Kaltume ce ta zugani tace nazo na d’ana ta k’arfi da yaji,Dan matarka tana da taurin kai ta bata wahala kafin ta yarda afara had’ata da ni,Dan Kullum cikin mata nasiha take,to amma dayake Hajiya Kaltumen,Wanda zata dulmiyar take nema,ahaka nida ita muka sako matarka agaba har muka yi nassara akanta,ta yarda muringa muamalla ta waya,amma tace bazata yarda mu had’u ba shekaranjiya Hajiya Kaltume ta sa koni agaba tace ince mata sai na zo mun had’u matarka tak’i ak’arshe tace ta tuba tayimin wa’azi tace nima nadaina,abinda mu keyi bai dace ba,Dana gayawa Hajiya Kaltume shine tace mata nace mata na tuba amma Dan Allah zanzo muhad’u mu gaisa,kawai,shine tace inazo sai na samu hodan nan na bad’a mata hodan sai na samu biyan bukatata ta Dan Allah Alhaji kayi hakuri nayi nadama,

Yusuf bai ce komai ba illa girgiza kai da yayi ya zauna sosai,ya bud’e wayar ton g,ganin da password akai ne yasa ya mik’awa Ton G wayar yace ya cire masa password d’in,jiki na rawa Ton G ya cire masa password d’in,Yusuf Watsapp d’insa ya shiga yakuwa Bud’e grp d’in Sex Nigt club scrolling yayi sama sosai,ahankali yafara bin chatting d’insu yana karantawa yana kallon videos d’in matan da suke turawa,da hirar batsar da suke yi,wani video ya kuna da wani Bad boy ya turo bud’ewa yayi yafara kallo,Video ne na yanda yake sx da wata mata,bai gama gani ba yayi sauri ya rufe videon yana a uziyya, cigaba yayi da karantawa yana bud’e video yana kallo, yana ganin iskanci akeyi sai yayi sauri ya rufe,ahaka yazo kan videos da hotunan da Ton G yake turawa grp d’in,d’aya bayan d’aya yafara bud’ewa yana gani,wani irin bakin ciki,da tafasa zuciyar Yusuf ke yi daya ga yanda suke comment akanta,suna suma ya musu hanya su d’ana videos d’in da ma bai gani awayar Manal ba ya gani a group d’in da alama Manal ma goge wasu take yi,ahankali ya koma ya bud’e grp d’in Dan yaga participant d’in yaga su shidda ne,fitowa yayi daga watsapp ya shiga gallery hotunan da videos d’in da Manal ta tura mishi gabad’aya ya goge daga wayar ya d’ago cikin tsananin b’acin rai ya kalli Manal da take juya kai hawaye na amballiya a fuskarta,” Na mugun tsanarki Manal,na tsani in bud’e ido naganki,ba iya wanan zalb’en ne yaga jikinki ba harda wasu biyar nama San suma su biyar d’in sun broadcasting dinshi, ayau zaki barmin gidana Manal Dan ina cigaba da ganinki agabana I can do something stupid, “

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25Next page

Leave a Reply

Back to top button