A SANADIN GROUP COMPLETE HAUSA NOVEL

A SANADIN GROUP COMPLETE HAUSA NOVEL

Motsin su Hanif ne ya tasheta daga nanauyan barcin da ya d’auketa duro wa tayi daga kan gadon,ta nufi Palo aguje,a Palo ta tarar da Hindatu tana shiryasu,Taufiqa na tsaye da uniform d’inta a hannu Dan ta dage Hindatu bazata sa mata ba sai dai Momy ta sama ta,gaisheta suka fara yi,ta amsa tana k’arbar Uniform d’in daga hanun Taufiqa,sa mata Uniform d’in tayi,Hindatu ta nufi kitchen ta dauko flask din shayi da chips din data soya tazo ta zuzzuba musu,ta d’auko lunch box d’insu daga kitchen tazo ta ajiye,manal ganin sun fara cin abincin ne yasa tacewa Hindatu ta kai su school in sun gama cin abincin,to tace mata,ta kalli su Hanif tace mai zata dafa Musu Kafin su dawo,Taufiqa ce tayi saurin cewa cous cous,Saleem yace shi dai fried rice,murmushi tayi tace duk zata dafa musu suyi karatu da kyau,Hindatu tayiwa magana tace mata tazo ta k’arba musu choclate,Hindatu na barin d’akin ta shiga band’aki tayi wankan tsarki tayi alwala ta tayar da sallah,tana sallama ta ta mik’e Dan tunda ta tayar da sallah,kira ke ta shigowa wayar ta kuma San Yusuf ke kiranta,sai da ta fara kallon agogon d’akin Kafin ta d’aga,k’arfe 7:30 lokacin,

Tana d’aga wayar yace “Madam ina kuma kika ajiye wayar ake ta kiranki baki d’auka ba”?

“ina can palo ina shirya su Hanif shi yasa bansan ka kira ba”

Hira suka cigaba da yi, sai da suka kwashi awa d’aya suna hira Kafin ya mata sallama,tana ajiye wayar kiran titi ya shigo wayar,lumshe idonta tayi Kafin ta d’aga Dan taji dadin yanda yasa ma mata nutsuwa jiya,kamar da jiya,hirar banza suka ringa yi Wanda hakan yaringa yiwa manal dadi,Dan sai zuciyarta zata rayya mata fa abinda take yi haramun ne,sai wata zuciyar ta k’awata mata dadi da nutsuwar da take ji.

Ahaka Manal ta jefa kanta a masifa bata ma jin ita matar aurece ballantana ya kai ta ga tunanin nauyin zunubin da take aikatawa amatsayinta na matar aure,abinda ta canza ta kuma gyara shine ita take yiwa yara home work, Yusuf kuwa ta kan tura mishi tex message ta watsapp,ko tayi squeezing time ta kira shi,yanda bazai k’ara tunanin wani Abu ba,shek’a ayarta kawai take da Titi ta waya da chatting,sai su raba dare suna waya, hotuna kuwa kullum da style d’in da suke wa juna,Idan Ana gobe Yusuf zai dawo clearing komai na wayarta take yi,tayi mutting groups,idan kuwa ya dawo tayi ta bashi kulawa kamar ta had’iyeshi nan kuwa Allah Allah take Monday tayi ya koma Dan tama fi samun nutsuwa da titi akan mijin aurenta na sunna wa’iyyazubullahi.

Sai da Manal ta samu wata biyar a cikin irin wanan masifar inda shak”uwar da suka yi da Titi ya wuce tunanin mutum Dan kud’in da take kashe masa ba kadan bane,kati kuwa kullum sai ta tura mishi, duk sati sai ta tura mishi dubu goma,yan kudad’enta awajen titi yake karewa,acikin wanan halin Ton G ya matsa mata yace yana so su had’u face to face bai kamata ace a iya waya zasu ringa biyawa junansu bukata ba,Dan shi mafarkinsa da burinsa a rayuwa bai wuce yaganta azahiri,ya sadu da ita,Dan yasan a fili, sai abun yafi haka,Manal tunda ya bijiro mata da zancen yanaso yazo su had’u ta Dan fara jin tsoro,dan ita agaskiya duk abinda take yi a iya waya takeso su tsaya baza ta iya aikata zina da aurenta ba,duk da babu banbanci kamar zinar ma suke yi,amma ba kamar a zahiri ba,hanya hanya ta fara mishi,shi kuwa ton g ya sako ta agaba ya matsa mata yace ko dai bata sanshi ne shi yasa take haka.

Watarana daddare bayan sun gama watsewar da suka saba yi awaya tana daga kwance tana sauke ajiyar zuciya,Ton G ya fashe mata da kuka, hankali a tashe ta fara tambayarsa mai yasa yake kuka,cikin kuka yafara ce mata in bai had’u da ita asatinan ba zai iya rasa ransa Dan shi kadai yasan mai yake ji akanta,kalamai ya ringa mata yana kashe mata jiki da dadin baki,Manal kuwa ganin ya dage yana kuka ne yasa tace to ya kwantar da hankalinsa zata yi tunani zuwa gobe zata gaya mishi yanda za ayi,da haka suka yi sallama , Manal ta dafe kanta Dan har ga Allah tasan fa abinda take yi haramun ne,amma me shaidan ya Riga ya sata agaba,ya za’ayi abinda bata tab’a yi ba tana buduruwa tazo tayi a lokacin da take da aure,da yaranta,ya yaranta zasuyi if they get to find out what she is doing,tayiwa mijinta adalci kuwa?Yusuf bashida buduruwa tasani,bazai tab’a cin amanarta ba,Rabin abinda take yi tasan Yusuf bazai tab’a yin hakan ba,to meyesa ita ta biyewa San zuciyarta take cin amanar mijinta,take cin amanar yayanta,?

Readers Ku tayata bata amsa nima na tafi tunani????????????
[10/14, 6:56 PM] Sadnaf: ???? S????N????DIN GROUP

Written by

???????? SADNAF????

PURE MOMENT OF LIFE WRITERS

_We don't just entertain and educate we touch the heart of the readers_  *P.M.L*

#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
#IG PML WRITERS
#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
#http://maryamsbello.blogspot.com

A short novel based on true life story

This page is all
Yours the great,talented,famous and fantabulous writer Zuwairat Ummu maryam keep d fire burning may the sky be your limit dear more greece to our shining elbow????❤????????????????

Page 25_30

A ranar Manal kwana tayi bata yi barci ba,Dan bata tunanin zata iya aikata zina da aurenta.

Sai da tayi wanka tayi sallah barci yayi awon gaba da ita, ba ita ta tashi ba sai goma na safe,Palo ta fito sai da ta tabbatar da hindatu ta gama komai ta koma ciki,wayarta ta d’auko ta ga Miss call guda goma shidda na titi hud’u na Yusuf,number Yusuf ta fara kira,yana d’agawa yace zai kirata yana wani Abu,yana kashewa tafara k’ok’arin kiran Titi Dan har ta saba suna gama waya da Yusuf sai ta kirashi,da sauri ta katse wayar da ta tuna yanda suka yi dashi jiya daddare akan zata gaya mishi yanda zaayi ayau,kiran waya daya shigo ne ya katse mata tunanin da take,Tit ne dai yake kiranta kasa d’aga wayar tayi Dan bata san mai zata ce masa ba dan har ga Allah bazata iya zina da aurenta da yayanta ba,ganin kiran ya k’ara shigowa ne yasa ta d’aure ta d’aga “haba hot milk mai yasa kike min haka ko dai kin daina sona ne” titi yace a shagwab’e,lumshe ido Manal tayi Dan indai Titi zai mata wanan shagwab’ar to ya gama tafiya da imaninta,Titi karuwa jin da yayi manal tayi shiru ne yasa yace ” Hot Milk kin yi shiru,ni nasan bakya sona jiya banyi barci ba dan ina fargabar amsar da zaki bani,Hot milk pls ki amince nazo kano naganki mu jiyar da junanmu dadi a zahiri,I promise you sai kinfi ni jin dadin had’uwarmu Dan wlh dak’yar in baki rabu da mijinki akaina ba,Dan daga ranar da muka had’u dake azahiri wlh kallon mace zaki koma yiwa Mijinki”

Tunda ya fara magana titi tafara hararo irin dadin da take ji in suna iskancinsu ta waya ina ga sun had’u a zahiri,Titi bai yi karya ba Dan tasan indai suka had’u batasan wane irin dadi kuma zata ji ba,bud’e baki tayi da zumar tayi magana,hirar da suka yi da Yusuf ya fad’o mata gabanta ya yanke ya fad’i

Kwanaki da Yusuf ya dawo bayan sun gama farantawa junansu rai,tana kwance akan k’irjinsa Dan wani sa’in sukan raba dare suna hira kawai,tsaki yayi ta d’ago tana kallonsa tace mishi Lafiya yake tsaki,girgiza kai yayi ya cije lebb’enshi alamar abinda yake San fad’in na k’ona mishi rai,ganin ya mik’e ya zauna ne yasa tasan maganar ba k’arama bace hannayenta ya rik’e yana kallonta take ita kuwa gabanta ya hau fad’uwa Dan ta d’auka ko wani Abu ya gani a wayarta,magana ya fara yi cikin tsananin takaici take idonsa ya chanja kala zuwa ja cewa yayi

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25Next page

Leave a Reply

Back to top button