BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Wani fitinannen kallo Nanne ta kafe Amina dashi yayin da ziciyarta yake wani irin tasa tace

Taku ce maman Islam
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
????BA JINANA BACE????

2021
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 13

“Yanzun shi Baffan ne ya d’auke ‘yar yabawa kishiyarki akan me shi ya haifa Miki yar ko su sukayi Miki rainon da nak’udar wallahi bazai sab’uba bindiga a ruwa” sosai Nanne ta hau fad’a ta inda suka shiga bata nan suke fitaba sosai ranta yai azabar b’aci ganin fad’an bazai fisshe taba ta finciki hannun Amina tana fad’in”zo muje gidan dole su baki yarki haka akeyin kyauta da abun wani mugunta”

Tana bud’e labulan suka gabza karo da malam dayagama jin komai tayi saurin ja baya tana had’e rai danma kar ya dakatar da ita dan daga kallon irin kallon dayake binta dashi tasan cewa yagama jin komai ” muje ciki ko?”

Shine kawai abinda malam yace yana rab’a gefenta ya wuce had’e rai ta k’ara yi tana hararan bayan sa sai dai babu ikon musu dashi dan tun farko basu sabar Masa da hakan ba.

Waje ya samu ya zauna saman kujera mazaunin mutum d’aya yayin da Amina ta zauna agabansa ta sunkuyar dakanta k’asa ita Kuma Nanne ta zauna gefen gado fuskar nan babu alamun annuri ta masifar cin magani dan ma kar malam yace zai hanata zuwa d’aukar ma ‘yarta mataki.

Gane take takenta ne yasa malam sakin murmushi yace “Zahra kenan Zahra’u manya Zahra’u sarkin rikici dan Allah Zahra in kin girma kisan kin girma inbanda abinki ina ruwanki da harkar yara ‘yar nanfa tasace yana da iko akanta dan me Zaki goyi bayan rashin gaskiya to ban amince Miki zuwa ki zubar min da kima a inda nake da Martaba da daraja dan haka na kashe wannan maganar ke Kuma” ya fad’a yana nuna Amina karna sake hanin kinsa k’afa kin baro d’akin ki akan wani dalili mara tushe ‘ya dai tasace Kuma yayi abinda yake so da ita ace danme kar naji kar na gani kinji ko” sosai malam ya rik’a yi musu nasiha har zuwa sanda yai shiru Nanne ta sauke ajiyar zuciyata tace “nifa malam bawai ina goyon bayan Amina bane saboda anbama kishiyarta yarta ba domin da ace suna zaune lafiyane to da hakan mu kanmu saiyafi Mana dad’i amma kishiyarta muguwar makirace datasan kan kissa ta mugunta” nan Nanne ta rik’a bawa malam irin labarin da shamsiyya ta fad’a mata da irin bautuwar da Amina take a siyasance a hannun Sailuba.

Ajiyar zuciya malam ya sauke yace “karku damu domin komai na Allah ne Kuma duk abinda yake damuwa hukuncin Allah ne dan haka kusa aranku duk abinda zai samu mamana daga Allah ne domin babu wani abu dayake samun bawa face da sanin Allah”

Sosai nanma ya kwantar musu da hankali sannan yayima Amina nasiha da hak’uri a duk halin data tsinci kanta hak’ik’a Allah baya barci, yace Nanne taje ta rakata Kennan Baffa yayi sallama’ bayan sun gaisa da malam kafin yace komai malam ya soma bashi hak’uri abisa shirmen Amina har Saida kunya ya kama Baffa ya dinga sunne Kai yana dad’a bawa malam sannan yace adad’a bawa Amina hak’uri domin ansan anyi mata ba daidai ba amma yayi hakanne dan samun had’in kansu.
Malam yace babu komai Allah yabada wasu masu albarka.

Tunda suka dawo gida Amina tayi masifar d’auke kanta daga garesu ta daina kulasu duk wani aikin gidan ta ajeshi tsakanin ta dasu sai ido hatta kicin na falonta take shiga, sosai hakan yake sosa ran Baffa shi da kanshi yasan cewa basu kyauta mata ba sun nuna son ransu kuma zata na ganin cewa dan Sailuba ‘yar uwarsa ce shiyasa ta nuna son Kai acikin al’amarin.

Da k’yar yasamu yasha kanta suka koma dai dai haka ma mama kamar yadda ta rad’a wa sailuba suka koma daidai amma Kuma bata Kara yarda tayi mata wannan uwar bautar ba.

Wata irin sangartacciyar rayuwa aka koya Maryam wani irin mugun gata ake gwada mata wanda babu wanda ta ragawa rashin kunya wa kowa sai anyi magana Sailuba tace ai yarinyace haka rayuwa taci gaba da tafiya an mugun tab’ara Maryam duk girman mutum bai wuce ta zageshiba.

Koda Nanne ta kula da yadda Amina ta watsar da Maryam da al amuranta fad’a ta Mata tace yau idan akace Maryam ta lalace kafin kowa yaji ciwon haka kece zakiji domin kece kika san zafinta ita adirenta ta ganta dan haka ita hakan bazai tab’a damunta ba domin batasan ciwontaba haka Nanne tayi ta mata maganganu tare da nuna mata illar kawar da kanta da tayi daga kan Maryam.

To Kuma duk yadda taso Jan yarta ajiki tareda nusar da ita hakan ya faskara see domin Sailuba ta wuce tunanin mai tunani akan komai musamman ta fannin makirci ta kware fiye da zaton me karatu.

Haka rayuwarta yacigaba a tab’arb’are babu kwab’a babu harara duk abinda take so shi ake mata a ta gefe guda kuma tun bayan da ta Kuma haifar yara maza guda biyu duk basu zo da raiba bata sake Koda b’atan wataba sosai abin ya dameta ga matsalar Maryam da Allah yayita da fitinar tsiya ga shegen rashin kunya ga d’an banzan tsokana abin ya masifar damunta amma sai takema yarta addu ar Allah ya shirya.

A b’angaren Sailuba kuwa tunda taga daga Kan wannan yara anja kusan shekara bakwai Amina bata k’ara Koda b’atan wataba hakan ba k’aramin faranta ranta yayiba dan haka ta watsar da duk wani nema da take akanta ta maida dukan wani asirinta akan iya Baffa shi kad’ai riba biyu ga Baffan ta ga Kuma Maryam data b’atar da duk wata hanya da zata gane cewa Amina ce mahaifiyar ta.

Lokacin da MD ya dawo ya tarar da irin tab’arb’are war da rayuwar Maryam yayi ga fitsara ga raini wa kowa ba k’aramin tashi hankalinsa yayiba ya dinga bin Ammey yana fad’an bata kyautaba databar rayiwar Maryam awajen wacce batasan ciwon haihuwaba amma sam Ammey tak,’i kula hakan tama daina sauraron say domin tasan cewa kotayi magana babu abinda hakan zai haifar sai fitina Kuma tun wataran da taga abin yana yawa tayi ma yarinyar fad’a ta zageta ta kuwa kamata ta zane ai kuwa ranar taga ruwan bala I a wajen Baffa dan rufe ido yayi ya tujareta har da mata iyaka da yarta abin ya k’ona mata rai sosai har Saida tayi zazzab’i saboda bak’in ciki shi kanshi Baffa da yaga kamar bai kyautaba yasa ya dinga rarrashin ta daga baya.

Da farko MD yaso jan Maryam ajiki amma Sailuba bata bada damar hakan ba domin da kanta ta dinga tusa tsanar Muhammad a zuciyar Maryam har taji duk duniya babu wanda ta tsani ta bud’a ido ta gani irinsa.

Tun yana daurewa halayyar tata har abin yafi k’arfinsa domin halin yarinyar ya wuce tunanin mai tunani, hakan yasa yai masifar tsanar wannan mugun halin nata yarinyar da ya ginu da tunanin yadda zai jata jikinsa ya gwada mata Koda gutsuren k’aunar da mahaifinta yake nuna masa amma ina makircin uwar rik’onta bazai bari hakan ya faruba.

Sanda Maryam ta cika shekara goma dai dai Amina ta Kuma haifo yaronta katon gaske sak Maryam har yaso yafi Maryam fari da manyan idanu, wannan haihuwa ba k’aramin gigita tunanin haj. Sailuba yayiba domin ta rigada tagama sawa ranta cewa Amina tagama haihuwa ita da k’ara haihuwa har abada, kamar yadda sabon bokan da suka sake ya fad’a Mata.

Tun kafin suna take tunanin hanyar dazata b’ullowa wannan yaron dan bata tab’a jin abinda ta tsana sama da wannan yaron ba duk iya yanda taso had a makircin ta akan yaron idanun Baffa ya rufe abinda ya k’ara d’aga hankalin Sailuba yadda atake Baffa yayiwa Amina kyautar wani kat’on gidansa na G R A sannan Kuma yaron wanda yayima hud’uba da Abdul Nassar yabashi companyns na takalma company data gama cin buri akai tagama tsara duk yadda zata yi ace anbarwa Maryam shine yau ake bama wani banza da uwar banzan lallai Baffa ya tarowa kansa

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button