BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Wata shegiyar dariya ta saki tace “zaka gani zaka kuma tabbatar muzuba nidakai shege ka fasa” daga haka tayi waje hankali a tashe.

Sosai maganganun ta suka tsaye masa rai sai dai kamar yadda yake tsaye wajen yiwa Maryam Adda a ya zama dole ya k’ara zage damtse.

Maryam kuwa tana shiga d’akin Ammey ta rufeta da fad’a akan maganganun da taji tana sakarwa haj. Sailuba tace mata koba komai matsayin uwa take awajen ta dan haka ta rik’a sanin irin maganan da zata fad’a Mata.

“Nifa Ammey indai akan kune babu abinda zaki fad’a min na fahimta matar da bata da lokacina sai na gantali kullum tana tafe a hanya ita ba kasuwanci ba ba komaiba, ai wallahi duk laifin Baffa ne da yasake mata haka dayawa shiyasa take iskancin ta son Rai”

“Ungo nan Ammey ta yiwa Maryam tace “idan har da gaske kina ganin mutunci na kamar yadda kika fad’a to kada ki sake kinji ko?”

“Naji Ammey, ina Baffa shi nazo nema”
“Lafiya kike neman Baffa?”
Bata b’oyewa Ammeyn komai ba ta fad’a mata tana son bawa baban k’awarta jarine ya fara sana a, sosai hakan yayiwa Ammeyn dad’i arai taji dad’i ya kasance yarta tana da zuciyar tausayi dan haka Ammeyn ce da kanta ta bawa Maryam dubu d’ari tace “gashi idan Kuma bai isaba kimin magana sai na k’ara miki?”

Rungumeta maryam tayi tace “na gode Sosai Ammey na Allah yaja da rai ta sumbaci Ammeyn tayi waje da sauri tana fad’in saina dawo”

Sosai Ammey ke jin dad’in yadda yarinyar ta soma sakewa da ita ta rage wannan d’an banzan yawon dayake sanyata fargaba da damuwa musamman idan haj. Sailuba ta dawo taga bata nan ko zata kwana basata tuhumeta taji inda taje ba.

Tana fita suka gabza wani uban karo da MD ai kuwa taji zafi sosai shima haka duk suka dafe wajen suna kallon juna kafin Maryam ta galla masa harara ta wuce tana sosa goshinta.

Da sauri yasha gabanta ya tsaya yana d’an diddira k’afa irin na shagwab’a yace”ni Allah Allah Allah sai ki bigeni kuma ki wuce babu hak’uri ni sai na rama” yadda yayi maganar dole abin yabata dariya batasan sanda ta saki murmushi ba tace “sorry”
Daga haka ta wuce kuma shan gabanta yayi yace “ina kuma zaki?”

“Gidan su Maryam ta bashi amsa dan har ga Allah sauri take ta tsai da baban Maryam yau baifita nema ba dan haka yakamata taje akan kari
“Wanda kike siyayyar nan awajensa?”
Ta tsinci muryarsa tana shirin fita “Eh shi”
Ta bashi amsa tana ficewa da sauri ya bita ya rik’o hannunta yana kallon ta tace “dan Allah yaya sauri nake sai batamin lokaci kake”

“Muje mana naganshi idan ya cancanta da amanar da kika bashi saiya cigaba da kula da su idan Kuma ba haka ba sai na amso ko?”
Sanin cewa sunyi maganar da Ammey yasa bata musa masa ba suka jera suka shiga motar yaja suka bar gidan.

Maman Islam ce

بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
???? BA JININA BACE????
2021

            NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 35

Saida tasa kashi suka biya wani spermaket ta d’an musu siyayya, dan Allah yasani hakanan Allah yasaka mata tausayin iyayen Maryam, saboda yak’i nin su da kamewar su hakanan sun iya babun su, dan malam Abdullah mutum ne jajir tacce tsayayye, akan iyakansa bai yarda da zubar da daraja da kimar gidansa ba, haka kuma baya daukar raini ko kad’an dan haka hatta iyalinsa suna shakkar sa saboda sam bai yarda da wulakanta kai ko zubda mutunci ba.

Yadda suke shiga cikin lungunan unguwar yasha mamakin yadda Maryam tasan wajen dan koshi dayake namiji bai tab’a yowa ta area dinba sosai ya rink’a binta da kallo yana mamakin ta.

Sai yanzu yake gane asalin halinta mai kyau ne irin na mahaifiyar ta wancen halin na aro ne wanda aka d’ora ta akai bisa wani dalilin mara tushe da makama.

Ita duk wannan kallon dayake binta dashi sam bata kulaba dan hankalin ta yana kan wayar ta suna chat da Halima sai yanzun ta d’ago dan taga ko sunkai inda ta kwantato masan ai batasan sanda tasaki kara ba ta maida hankalin ta kanshi ganin suna shirin taka wani k’aton dutse, shima da sauri ya taka burkin da sai daya janyo hankalin wasu daga cikin masu wucewa dake cikin unguwa be.

Harara ta galla masa kamar idanunta zasu fad’o tace “to kasheni ka huta tunda ka gaji da ganin rayuwata”

Murmushi ya d’an saki kafin ya d’an shafi fuskar ta yace “ina son ki princess dan Allah ki soni my happiness” hararan ta kuma masa kafin ta d’auke kanta yasa hannu ya kuma juyo da fuskar nata saitin sa ya kafeta da ido,

.”dan Allah ki kalle ni nasan zaki yadda da abinda nake fad’a miki har zuciyana ne” bata musa masan ba ta d’an kalleshi na kamar 1 mint take taji ta fara d’an tsuma tsuma tasoma k’ok’arin kwace fuskar ta amma ya hanata damar hakan da sauri ta runtse idonta dan bazata juri kallon wannan fitinannun idanun nasa ba.

Murya na rawa tace ni kaina ya k’age ka sakar min fuskana, kuma ka daina yimin wannan kallon mayun” murmushi ya d’an saki kafin yace “indai akanki ne baby ki kirani lasan ma ba maye ba da da yadda zanyi na tsaga jikina na sakaki da tuni na jima da yin hakan na huta’ dan Allah baby karki gujeni, idan kika gujemin hakan yana nufin abubuwa da yawa ciki harda rayuwana”

Yanayin da yayi maganar yasa dole ta kara bud’e idanunta akanshi yadda taga idanunsa sun koma ba k’aramin tsoratata abin yayi ba sunyi wani irin mugun ja ga wani kyalli kyalli alamun ruwan hawaye ne suka kwanta masa aciki, wani irin tausayin sa ne ya kamata tace

“Zaka iya aurata koda ace bana sonka?
Sosai maganar ta ya dakeshi, zaka iya aurata koda ace bana sonka?
ya sake maimata tambayar a zuciyar sa kenan akwai wanda take so Kennan tunda bata son shi?
Wani irin ajiyar zuciya ya sauke kafin yace

“Baby wa kike so?
“Babu”
Ta bashi amsa atakaice sannan ta d’ora da fad’in ba kaine kakori muhseen ba yaron dayake masifar Sona kamar zaiyi hauka tundaga ranan yake masifar tsorona bama kaiba ko a hanya ya ganni wallahi canja hanya yake”

Sosai maganar ta ya masa zafi a zuciya amma sai ya daure tunda shine mai nema dole ya sauke duk wani zafin ransa gefe ya nemi masalaha
“Kina son muhseen d’in?
Ta tambaye ta cikin tsantsar zafin rai dana zuciya.

“Ni babu wanda na tab’a jin ina so arayuwata shima muhseen d’in saboda nacinsa da rashin zuciyar sa yasa na tausaya masa na fara kulashi” baisan sanda ya wani fisgeta ta fad’a jikinsa ba ya wani k’ank’ame ta atare suka sauke wata irin ajiyar zuciya kafin yasoma magana cikin sanyin da shi kansa baisan zai riskeshi a wannan lokacin ba yace

“Na amince baby zan aureki koda ace bakya sona nasan dole wata rana zanyi nasara zan mallake ki KE DA ZUCIYAR KI”
“Ya jima yana zubar mata da sak’onnin da suka cunkushe masa zuciya suka hanashi sukuni, bai tab’a sanin da akwai rayuwa irin wannan ba rayiwar da zaka kasa katab’us ka kasa sukuni ba sai da ya had’u da jarrabar SO wanda ya hanashi sakat yake sanyashi kasa baci cikin dare ya kasa runtsawa tsawon dare ya zubda hawaye ba adadi duk asanadin SO”

Tun bata fahimtar maganganun sa har ta fara fahimta sanadin da jikinta yayi sanyi bata san da cewa akwai ranan da MD zai iya kallon idanunta ya furta mata tsadaddun kalamai irin wannan ba musaman idan tayi tunanin yadda suke da shi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button