BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

“Gaskiya yakamata ka gyara halinka da d’abi unka ba abune me kyau ba kowa ya rik’a maka shaidar baka da mutunci babu wanda ka ragawa har akai ga matakin da kowa zai fara jin tsoronka sam wannan zalunci ne babba dan Allah ka gyara kaga ni d’innan dakake gani duk abinda kake ji dashi nafika ko ranan ma shammata na kayi banda haka bazakayi nasara akainaba sai dai ni bana shiga harkan wanda bai shiga nawaba dan haka kaga ko makarantar nan banda kawa sai A A”

“Nasani sam ban kyautaba kuma na miki alk’awari insha Allah daga yau nima babu ruwana da sabgar kowa”
” Allah yasa” ta fad’a atakaice tana wucewa department d’insa.

Yana tsaye har ta shige murya k’asa k’asa yace “tamin Allah yasa tasoni nidai tamin badan komai ba sai dan nutsuwa da ajinta Abba kayi suruka irin wacce kake so ‘yar wani wanin ma wanda yai suna aciki da wajen k’asar nan”
(Su Kamal d boy daga sannu sarkin fawa lol????????????)

Yau kam da wuri suka koma gida dake lacca d’aya ke garesu suna gamawa babu wani jinkiri Maryam ta nemi da A A ta rakata banki tana son bud’e sabon account, da mamaki AA take dubanta kafin tace “ke kuwa name sake duk yawan asusanku wanda ba ayi miki iyaka dasuba sai kin bud’a wani?”
Bazaki gane bane sam mama bata barina da k’udi ita zata bani kuma ita zata dawo ta rance na rasa abinda mama take da k’udi duk yawan kyauta irin na Baffan mu wallahi A A Saida mama ta kureshi” haka dai suka tafi tana bata bad habits d’in mamanta wanda abin yake masifar damunta ta kuma rasa dawa zata zanta taji sanyi saifa yanzun dataji ta aminta da ita.

Har sukaje suka bud’e account kud’ad’en da Maryam ta zuba a account d’in saida abin ya bata tsoro yayin da Maryam ta dinga mata dariya daganan tace Maryam ta rakata kasuwa zatayi siyayya sai da suka fara zuwa tasiyi kayan kwalliya da turarukanta dake Maryam mayyar turarece zai wuya ka kusance takaji bata k’amshi domin ita d’in ‘yar gayuce tagaban kwatance hakan yasa take da masifar farin jini Saidai halinta bai barinta shiga sabgar mutane domin bata da kirki ko kad’an.

Daga nan Kuma suka nufi wajen masu saida kayan abinci A A taga Maryam ta d’auki babban buhu na shinkafa da k’arami sannan ta d’auki taliya carton biyu haka makaroni da cous cous da semonvita irin buhunnan mai guda sha biyu shima guda biyu manja man gyad’a Maggi kanshi saida ta d’auki carton guda banda sauran spacies data d’iba ita dai A A kasa daurewa tayi tace “name sake nasandai abincin gidanku trela ake kawoshi me zakiyi da wannan abin da kike ta loda?”
“Ba damuwarki bane” cewar Maryam datakewa mai shinkafar maganan ko zasu samu motar da zai kwashe musu dukan kayan? dan adaidaita yayi musu kad’an.

“Akwai ‘yar k’ur k’ura wanda shi dama aikinsu Kennan d’iban kaya sukai maka duk inda kakeso’ ya fad’a yana kwalawa wani kira.

Tun tambayar da tayi mata tace ba damuwanta bane bata k’ara tofa nataba abinda ya Kuma d’aure mata kai shine ganin motar bai faka ko ina ba sai k’ofar gidansu da mugun mamaki ta rik’a kallon Maryam wacce ta d’auke kanta batare data bari sun had’a ido ba.

Suna tsaye har aka gama shiga da kayan abinci sannan ta sallami mai motar suka bi mai d’aukan kayan na k’arshe, shima ta sallame shi yayinda suna shiga suka tadda Umma da Abban Maryam da shima shigowarsa Kennan gidan aka fara shiga da kayan daya fara tunanin ko b’atan kai masu kai kayan sukayi amma yana ganin Maryam da Maryam sun shigo ya dingabinsu da kallo fuskarshi da alaman tambaya.

” Ku zauna mana Abba”
Maryam ta fad’a tana zaran buta tayi bayan gida, sam Maryam batada k’yamar mutane musamman inkana da tsabta dake it’s mutum ce mai tsananin tsabta da k’yamar k’azanta, tana fitowa tayi alwala tayi d’akin Umman su A A ganin haka yasa itama Maryam tayi alwalar tabita d’akin.

Tana fitowa tanemi waje ta zauna tana gaida Umma da Abban kafin ta kalli Umman tace “nifa yunwa nake ji Umma yau bross ko kari bai bari nayi agidaba wai ya makara a office”

Kallon mijin nata tayi yayin da yayi mata alamar data bata abinda suke dashi,shi kuma ya saka takalmansa yayi waje Umma Kuma ta nufi kicin ta kawowa Maryam wake da shinkafar da suka dafa da salak da tumatur da cocomber, ta aje mata ta koma domin kawo mata ruwa sai ga Abba ya shigo da ruwan roba da lemo harda dafaffen kwai tunda yasan me aka dafa agidan.

Sam bata wani nuna bak’unta ba taja abincin taci ta k’osh har tana santi ita kam Maryam zuba mata ido tayi tana kallonta batareda data iya cewa uffan ba saida ta gama ta wanko hannunta ta dawo tasha lemon da ruwa sannan tace.

“Abba wannan kayan abincin nakane kai na siyowa dan Allah Abba kada ka k’ara zuwa kayi dako insha Allah idan Baffana ya dawo zansa yabaka jari ka fara business kaima insha Allah Allah zai dafa maka”

Rasa bakin magana Abba da Umma sukayi suka rik’a kallon Maryam da tsabar mamaki dama Maryam taji sanda yake cewa saida yai dako ranan sannan ya samo musu abinda zasuci?

Sosai Abba ya gode mata sannan yayi mata fad’an abin yayi mugun yawa tace “Abba wannan ba komai bane akan idan da ace Baffana na fad’a wa shi ya doramu akan wannan tsarin nida ‘yan uwana” addu’ar da Abban Maryam ya rik’a yiwa Maryam da zuri arta harsaida yasata hawayen farin ciki itama.

Sai bayan la asar ta baro gidan ta kamo hanyar nasu gidan dake suna da tazara sosai sai yamma ta dawo maimakon Kuma ta shiga gida sai kawai ta shige gidansu MM wani class mate d’inta wanda har yau suna mutunci dashi kasancewar su unguwa d’aya.

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
???? BA JININA BACE????
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 22

Bata zauna ba data tadda jm bayanan nayi b’ata last page jm zance na manta nace mm, tana zuwa bakin get taji mai gadi yana cewa “gatanan yallab’ai” MD daya gama rud’a driver da bala i saboda kawai yace tun biyu saura su Maryam suka bar makaranta kuma alhalin ba ama turashi ba sai wajen biyar saura shine fa MD ya hana shi sakat da masifa sai da ya koma makarantar har sau biyu.

Sannan kuma Ammey ta tabbatar masa da cewa tun fitar da sukayi tare bata dawoba amma kar ya damu wannan ba komai bane a wajen su dan takan fi hakama awaje, sosai ransa ya b’aci da jin abinda Ammeyn ta fad’a masa ya fito Kennan cikin wannan halin mai gadi da ba shine driver ba da ya had’a ya hasu sakat yace ga Maryam d’in nann

Duk zubawa get d’in ido sukayi yayin da Maryam ta shigo hankalin ta kwance babu wani damuwa tattare da ita, tana tafe cikin nutsuwar da Koda yaushe ka ganta zaka ganta tattare da ita.

Ran MD ne yai mugun b’aci cikin bak’in ciki ya k’arasa inda take wato shi yana nan hankali tashe ita Kuma tana can yawon gantalin ta hankalin ta kwance’ wata irin fincika yayi Mata da mugun k’arfi har saida ta saki k’aran azaba, jakarta da wayarta sukayi nasu waje yayin tayi taga taga zata fad’i yayi saurin tareta ta fad’a jikinsa.

Wata irin ajiyar zuciya ya sauke jin ta cikin jikinshi take ya ji wani irin abu ya tsarga masa tundaga tsakiyar kansa har zuwa babbar yatsarsa ta k’afa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button