BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Yau kam da wuri suka koma gida dake lacca d’aya ke garesu suna gamawa babu wani jinkiri Maryam ta nemi da A A ta rakata banki tana son bud’e sabon account, da mamaki AA take dubanta kafin tace “ke kuwa name sake duk yawan asusanku wanda ba ayi miki iyaka dasuba sai kin bud’a wani?”
Bazaki gane bane sam mama bata barina da k’udi ita zata bani kuma ita zata dawo ta rance na rasa abinda mama take da k’udi duk yawan kyauta irin na Baffan mu wallahi A A Saida mama ta kureshi” haka dai suka tafi tana bata bad habits d’in mamanta wanda abin yake masifar damunta ta kuma rasa dawa zata zanta taji sanyi saifa yanzun dataji ta aminta da ita.

Har sukaje suka bud’e account kud’ad’en da Maryam ta zuba a account d’in saida abin ya bata tsoro yayin da Maryam ta dinga mata dariya daganan tace Maryam ta rakata kasuwa zatayi siyayya sai da suka fara zuwa tasiyi kayan kwalliya da turarukanta dake Maryam mayyar turarece zai wuya ka kusance takaji bata k’amshi domin ita d’in ‘yar gayuce tagaban kwatance hakan yasa take da masifar farin jini Saidai halinta bai barinta shiga sabgar mutane domin bata da kirki ko kad’an.

Daga nan Kuma suka nufi wajen masu saida kayan abinci A A taga Maryam ta d’auki babban buhu na shinkafa da k’arami sannan ta d’auki taliya carton biyu haka makaroni da cous cous da semonvita irin buhunnan mai guda sha biyu shima guda biyu manja man gyad’a Maggi kanshi saida ta d’auki carton guda banda sauran spacies data d’iba ita dai A A kasa daurewa tayi tace “name sake nasandai abincin gidanku trela ake kawoshi me zakiyi da wannan abin da kike ta loda?”
“Ba damuwarki bane” cewar Maryam datakewa mai shinkafar maganan ko zasu samu motar da zai kwashe musu dukan kayan? dan adaidaita yayi musu kad’an.

“Akwai ‘yar k’ur k’ura wanda shi dama aikinsu Kennan d’iban kaya sukai maka duk inda kakeso’ ya fad’a yana kwalawa wani kira.

Tun tambayar da tayi mata tace ba damuwanta bane bata k’ara tofa nataba abinda ya Kuma d’aure mata kai shine ganin motar bai faka ko ina ba sai k’ofar gidansu da mugun mamaki ta rik’a kallon Maryam wacce ta d’auke kanta batare data bari sun had’a ido ba.

Suna tsaye har aka gama shiga da kayan abinci sannan ta sallami mai motar suka bi mai d’aukan kayan na k’arshe, shima ta sallame shi yayinda suna shiga suka tadda Umma da Abban Maryam da shima shigowarsa Kennan gidan aka fara shiga da kayan daya fara tunanin ko b’atan kai masu kai kayan sukayi amma yana ganin Maryam da Maryam sun shigo ya dingabinsu da kallo fuskarshi da alaman tambaya.

” Ku zauna mana Abba”
Maryam ta fad’a tana zaran buta tayi bayan gida, sam Maryam batada k’yamar mutane musamman inkana da tsabta dake it’s mutum ce mai tsananin tsabta da k’yamar k’azanta, tana fitowa tayi alwala tayi d’akin Umman su A A ganin haka yasa itama Maryam tayi alwalar tabita d’akin.

Tana fitowa tanemi waje ta zauna tana gaida Umma da Abban kafin ta kalli Umman tace “nifa yunwa nake ji Umma yau bross ko kari bai bari nayi agidaba wai ya makara a office”

Kallon mijin nata tayi yayin da yayi mata alamar data bata abinda suke dashi,shi kuma ya saka takalmansa yayi waje Umma Kuma ta nufi kicin ta kawowa Maryam wake da shinkafar da suka dafa da salak da tumatur da cocomber, ta aje mata ta koma domin kawo mata ruwa sai ga Abba ya shigo da ruwan roba da lemo harda dafaffen kwai tunda yasan me aka dafa agidan.

Sam bata wani nuna bak’unta ba taja abincin taci ta k’osh har tana santi ita kam Maryam zuba mata ido tayi tana kallonta batareda data iya cewa uffan ba saida ta gama ta wanko hannunta ta dawo tasha lemon da ruwa sannan tace.

“Abba wannan kayan abincin nakane kai na siyowa dan Allah Abba kada ka k’ara zuwa kayi dako insha Allah idan Baffana ya dawo zansa yabaka jari ka fara business kaima insha Allah Allah zai dafa maka”

Rasa bakin magana Abba da Umma sukayi suka rik’a kallon Maryam da tsabar mamaki dama Maryam taji sanda yake cewa saida yai dako ranan sannan ya samo musu abinda zasuci?

Sosai Abba ya gode mata sannan yayi mata fad’an abin yayi mugun yawa tace “Abba wannan ba komai bane akan idan da ace Baffana na fad’a wa shi ya doramu akan wannan tsarin nida ‘yan uwana” addu’ar da Abban Maryam ya rik’a yiwa Maryam da zuri arta harsaida yasata hawayen farin ciki itama.

Sai bayan la asar ta baro gidan ta kamo hanyar nasu gidan dake suna da tazara sosai sai yamma ta dawo maimakon Kuma ta shiga gida sai kawai ta shige gidansu MM wani class mate d’inta wanda har yau suna mutunci dashi kasancewar su unguwa d’aya.

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
????BA JINJINA BACE????

2021
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 20

Suna fita wajen ta fauce hannunta daga nashi ta nufi motar ta bud’e har ta shiga ta zauna bai k’araso ba daga inda take tana hangoshi yana magana da wani.

Wayarta dake k’ara ta zaro Maryam ce ta d’anyi murmushi tareda d’agawa “ya akayine besty?”
“Yau Kuma yada makara beaty malamin nan fa kinsan bashi da kirki kuma gashi saura 10 min mushiga kuma kinsan Koda 1min ya rigaki bazai bari ki ahigaba” cikin damuwa tace “ganinan besty”
“Wai kina ina need?”
“Zan fad’a Miki idan na shigo”
“To kiyi sauri dan Allah”
“Insaha Allah”

Tana kashe wayar yana k’arasowa yana duba agogon hannunsa ta wani kalleshi tayi kicin kicin da rai, murmushi ya d’an yi batare da yace komaiba ya tada motar lokacin da suka isa tuni malamin ya fara da kusan 10 yana faking tace ” maidani gida”

Kallonta yai da son k’arin bayani tayi masifar had’e rai tace “to meye amfanin barina tunda anriga an shiga kuma malamin baya barin kowa ya shiga muddun ya riga ka shiga” ta fad’a tareda zubowar hawaye sai da ya d’an kalleta na kusan 7 second kafin yama hannunta har department d’in nasu yayi sallama abakin hall d’in wanda ya lek’o ne yasa MD rik’e baki yace “kana ruwa yaro dama Kaine kake furgita mana kanne haka?”

Shima da mamakin yace “MD kana duniya gaskiya bamuda kirki zumunci yayi karanci me yafaru kake cewa ina firgita muku k’anne?” Maryam MD ya nuno masa “na d’an biya da ita office amsar wani muhimmin sak’o ina ajeta ta fashe min da kuka wai na maidata gida kariga ka shiga” dariya m Bash yayi yace
“Yarran ne koya sukaga wallenka sai su rainaka” ya fad’a yana dosar inda Maryam take yayin da MD ya biyoshi yana magana a waya.

Da sauri Maryam ta d’an russuna tace “good morning sir” ga mamakinta taji yace morning dear how fa maza wuce aji karki k’ara biyewa wannan yayanki ya makarar dake” ya fad’a bayan ya tambayi ya take batareda ya bari ta bashi amsa ba da alama yadda yai maganar akwai sanayya tsakaninsu da yayannata.

Da sauri ta doshi ajin inda ta hango Maryam tana ta faman lek’e ta window ta d’an kai mata dundu tace “me kike nema haka kamar zaki tsinka wuya tsabar lek’e?”
Ajiyar zuciya Maryam ta saki tace “ya akai yabarki kika shigo?”
“Uhm bross nefa ya makarar dani yana direni nasa masa kuka””””” nan ta kwashe yadda sukayi ta fad’a mata.

Bayan sun fito a lacca ne Maryam ta d’an dubi k’awar tata tace “besty yau ni naga masifa da tashin hankali ganin ido na,kai soja bala I ne wallahi besty”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button