BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Ita kam Maryam wani irin takaicin jinta ajikinsa ne ya kamata batasan sanda hawaye ya sulalo mata ba saboda bak’in ciki kwace jikinta tayi daga nasa tace murya k’asa k’asa “ban yafe ba d’an iska kawai aidama Halima tace duk wanda yake irin aikinka to manemin mata ne anje neman na bariki ba asamuba shine akazo latsa k’anwa dan abin kunya tur” ta fad’a tare da fashewa da kuka.

Tunda ta juya tabar shi nan tsaye yake cikin suyar ran kalamanta tunda yake babu wanda ya tab’a fad’a masa maganar daya k’untata masa irin yau ba,amma sosai abin ya rik’a sukar k’irjinsa temakon da Allah yayi masa cikin rad’a tayi masa duk wannan wulak’ancin da cin fuskar.

Sai dai hakan baisaka yajanye alk’awarin da yayiwa Baffa da Ammey ba yayi musu alk’awarin zai ja Maryam ajikinsa yanda zasuyi sabon da duk abinda zaisa ta bazata tab’a Musa masaba ta hakane Ammey take ganin zasu samu hanyar gyarawa Maryam zama.

Bayan an idar da sallar issha suna d’akinta ita da Nassar tana tayashi assignment d’in da yazo dashi saiga sallamar shi abakin k’ofar ba k’aramin fad’uwar gaba ta tsinci kanta aciki ba d’azu bayan tagama masa fitsaran ta dawo d’akin tace sam saitaga bata kyauta masa ba kome ya mata ya kamata yaci darajan shi na d’an uwanta JININTA.

Bata samu damar amsa masa ba sai Nassar ne ya amsa masa ya k’araso gefen da take ya zauna daf da ita tanaji Nassar yana gaidashi takasa had’a ido dashi bare wani gaisuwa ya had’asu.

“Nine d’an iska mai bin mata ko?”
Ya tambaye ta cikin wani irin murya mai kashe jiki wanda hakan yasata jin wani irin babu dad’i “kayi hak’uri bross dan Allah” maganar ya kwace mata batare data shiryawa hakan ba.

Sosai ya kafeta da idonsa wanda sukayi wani irin kyalli saboda kwallan daya cikasu, tunda yake babu wanda ya tab’a gasa masa bak’ar magana irin nata.

Jin shirun yayi yawa yasa ta d’ago idanunta dake duk’e kan littafin Nassar daya jima da ficewa daga d’akin,ba k’aramin fad’uwa gabanta yayiba ganin kwallan daya ciki idanunsa sai dai bai basu damar zubowaba saboda nayasan taga logonsa amma maganar gaskiya yaji zafin maganar ta ainun wanda dama dan yaji zafin tayi masa.

Rasa yadda zatayi masa wani maganar tayi sai kawai ta fashe masa da kuka wanda zan iya kiransa da kukan shagwab’a, take ya k’arasa zaman durshen agabanta tareda kamo hannunta yace “haba k’anwarta me kuma nayi miki banfa yi miki ko mai ba” ya k’arasa maganar cikin rawar murya domin har ga Allah jiyai kukan yana mugun tab’a masa zuciya.

“Kayi hak’uri” ta k’ara fad’a masa cikin muryan kuka “nayi” yafad’a mata da sauri cikin rawan murya sannan ya d’an dubeta yace “k’anwata na miki wani tambaya mana amma ina son dan Allah ki fadamin gaskiya tsakaninki da Allah”

“To” kawai tace masa tana faman goge hawayen da suke zubo mata har lokacin “to ki daina kukan haka mana dan Allah kinji” yafad’a yana share mata hawayen data rasa dalilin k’in tsayawarsu.

“Wai me yasa kika tsaneni ne?”
Yayi mata tambayar dayafi komai ci masa rai tun ranan data furta masa ta tsanesa har yau baidaina jin amsa kuwwar abin cikin kunnen saba sosai abin ya tab’a shi.

“Ai nima baka sona nida mama ka tsanemu kafi son Nassar da Ammey kanawa mama rashin kunya agabana baka dukan Nassar agaban Ammey amma ni kamar jaka haka kake jubgata ko dan kaga Nassar d’an d’akinku shiyasa ni kake nuna min ‘yan ubanci” ta fad’a cikin zubowar sabon hawaye, maganar ta na k’arshe ya mugun bashi tausayi har baisan sanda yasa hannu yajata jikinsa ba kamar jira take kuwa ta fad’a tareda sakin kuka irin mai cin rannan.

Dagajin yanda take kukan yasan akwai abinda yake damunta wanda ta barshi aranta takasa fad’uwa kowa, saida yabari ta d’an yi kukan da d’an yawa kafin ya soma d’an bubbuga bayanta har saida yasamu tayi shru da k’yar.

“Me yasaka ki kuka?” ya tambaye ta cikin sanyin murya, “ku kullum Ammeynku tana tareda ku tana kulawa daku duk abinda kukeso tanayi muku bata yawan fita unguwa bare tabarku cikin kad’aici, amma ni kullum mamana tana gidan k’awarta haj. Zakiyya danayi magana sai tabani k’udi ko tace bari ta had’a min wani d’an party bathday d’ina kuwa ko manta date d’in batayi dan Allah bross k’udi ne yake maganin ko wane matsala?”

Ta K’are maganan da tambayar abinda yake matuk’ar damun ranta,
“A a” yabata amsa cikin tausaya mata domin shima ya fahimci wannan abun yafara damunta hakan kuma ba k’aramin dad’i yayi masa a rai ba ko babu komai tunkafin ya fara tunanin hanyar da zaibi dan shan kanta ta yadda zajata jikinsa su kulle har akai ga maganar da ake son k’ullawa wacce babu wanda yasani dagashi sai Baffa sai kuma Ammey da Baffan yake jin tana da hak’k’i akan tasan komai.

“Amma Maryam bamune muka tsaneki ba kece Kika tsanemu bakya mutantamu da Ammeynmu ko kad’an har zaginta fa kikeyi taya kike tunanin zamu mutuntaki bayan bakya mutanta mana mahaifiyar mu?”

K’are maganar dayi mata tambayar wanda nan take ta gano kuskurenta amma Kuma sai tace “ai mama tace kada nasake nayi sabo da ‘yan uba dan muddun nace zan dinga mu amalantar ku to babu abinda zaisa baku kashe niba tunda Kuna ganin agabanku Baffa yake nuna yafi k’aunata akan ku, kuma tace Ammey muguwace tun ina jaririya taso kashe mata ni kuma tace Ammey ce take asiri take had’a ta fad’a da Baffa shiyasa kullum yake mata fad’a baya bata k’udi saidai inya ajiye ta turani d’akin sa na d’ebo mata mai yawa amma baya isarta saita had’a danawa.

Tsabar tashin hankalin jin wannan mugun zantukan baisan sanda ya zube ak’asan wajen yace “maman?”
Yafad’a gamida zaro ido har saida yanayin sa ya mugun tsoratata.

Pls manage data taku har kullum

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
????BA JININA BACE????
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Wannan shafin nakune gaba d’aya kuyi yadda kuke so

MUHAMMAD KAREEM

HAYATU BABA ZUBAIRU (YAYA HAYAT)
ITS ABBAS
Allah yabar kauna

Page 23

Jikinta take ya hau rawa tace “wa lla hi haka tace min, shi yasa kaga nima bana son Ammeynku.

Kasa magana yayi da hannunta da ya kama ya rik’e gam cikin nashi, idanunsa kuwa kad’awa su kayi suka yi wani irin ja,
Me wannan matar take nufi?
Takasa kula da amanar data dauka, Kuma tana son raba hanta da jini wannan ba adalci bane, zalunci ne babba, ke baki kula da yarinya ba, sai ma d’ora ta da kikayi akan wata turba mara b’ullewa.

“Zaki abota dani?”
Ta tsinci muryarsa cikin wani irin yanayi batasan lokacin data d’ago kai ta dubeshi ba sai dai bata iya tace masa komai ba ganin yadda ya kafeta da runannun idanunsa

“Uhm?”
Ya k’ara tambayar ta again babu amsa sai faman murza idanunta take da d’aya hannun da bai rik’e ba.

“Kema Ammey mamanki ce, ta tsinci muryar shi yana rad’a mata a kunne daga yau zamu rik’a shiga d’akin ta muna hira tare dake, kuma kema duk abinda kike so ki tambaye ta zata baki, kuma tama fi sonki damu idan kina musu ki gwada”.

Ya fad’a yana cigaba da murza hannunta dake cikin nasa.
“Mama bazata barni ba ta tsaneku” ta fad’i abinda tasan kullum maman tana tusashi agabanta, wanda tasan hakanne har cikin ranta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button