BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

“Ai bazata sani ba saboda kinga kullum bata zaman, gida Kinga kafin ta dawo munyi hiranmu, bawai ki rik’a shigowa d’aki, ke kad’ai ba, Kinga tunani sai ya miki yawa”

Ya fad’a yana kallon ta, tabbas abinda ta fad’a gaskiya ne, tunani yana damun sosai wani lokacin har sha daya mama tana kaiwa agidan hajiya zakiyya.

Shi kam zama ya gyara tareda zuba tagumi ya kafeta da idanunsa, yayin da tausayin ta ya game mai jiki,yana mai jin haushin kansa, na yadda tun farko bai jata a jikin sa ba bare har yasan damuwar ta.

“Zaki iya abota dani inzama amininki wanda zaki dinga fad’awa dukkan wani damuwar ki wanda zai dinga magance miki duk wani matsalar ki da yardan ubangiji?”.

Ya sake mata tabayan shi na farko,
“Idan mama tagan mu tare akwai matsala” ta fad’a masa haka, matsayin ta na wacce tafi kowa kusanci da mama dan haka tafi kowa sanin halinta.

“Karki damu Baffa bazai bata damar raba masa kanmu ba, kinsan burin ko wanne ubane ya ga kan yaransa ya had’u” ya fad’a yana d’ago hab’ar ta yana kallon, cikin idonta.

“Shi kenan na amince ta fad’a cikin sanyin murya”
Ihun murna ya saki tareda rungumeta”na gode my happiness na gode my Lovely sis dan Allah daga yau ki daina wannan had’e min ran baya min dad’i”

Ya fad’a mata a hankali “to” tace masa daga haka ta maida hankalinta kan aikin da suke da Nassar, tayata yayi suka gama aikin, daga haka ya rik’a janta da hira.

Waahegari motar ta ya iso, motar da Baffa yace bata gift idan taci jarrabawa, tun tana maganar motan har sai datayi fushi ta daina maganan bata san cewa mak’alewar motar daga MD bane shi ya hana saboda rawan kanta, yanzun ma sai yana yi yana sa mata ido sosai.

Washe gari kuwa tun kafin ya fito tuni ta shirya ta bar gidan a sabuwar motan ta sai da ya fito yaga Abdul Nassar yana shiga cikin motar da yake kaishi makaranta.

“Kai ina Adda?” Nassar ya tambaye shi “tab’Adda yanzun ai ta jima a schl, kasan cewa tayi bari tayi sauri ta tafi kar ka fito ka hanata kace Kai zaka kaita”.

Murmushi MD yayi Yana shafin sumar kanshi daya sha gyara, daga haka ya juya ya shiga motarsa security d’insa yaja shi suka wuce.

Uhm su o o anyi abun kai yaushe rabon duniya tunda bross ya dawo ya hanata sakat hatta motar mama da take hawa sai da ya hana ta k’arfin bala i, dan haka yau take jinta cikin wani irin farin ciki.

Tunda ta doshi cikin makarantar ido ya koma kanta domin motar tayi mugun d’aukar hankalin mutane, da yawan su basuyi mamakin ganin wacce ta fito daga motar ba domin ansan tafi k’arfin, wacce ta ninninka wannan ma, dan da yawa wasu suna mamakin yadda bata da motar kanta sai dai akawo ta.

Maryam kuwa da gudu tazo ta rungumeta tace “eye had’uwa ta iso kenan” ta fad’a tare da k’arasawa tana shafa motar, wani k’awata taccen murmushi Maryam ta saki tace “humm kinga wannan bross d’in namu sai a hankali, nasan wallahi shiya hana akawo min motar amma Baffa yafi shekara da biyan k’udinta”

Itama murmushin tasaki “ina ganin akwai wani abu tsakaninki da bross d’in nan”
“Kamar ya?
“Kamar yadda na gani bross sonki yake Maryam”
Manyan ta bata amsa
“Humm baki da hankali kin tab’a ganin inda akayi aure uba daya shifa d’an Ammey ne”

“Ammey shekarunta baikai ta haifi kamar bross dinku ba ki dai k’ara bincike”
“Humm kawai tace batare data d’auki abin serious ba.

Haka dai abubuwa suka cigaba da faruwa cikin k’aramin lokaci Maryam tayi wani mugun sabo da ‘yan gidansu batare da sanin maman taba wacce ta mik’a dukkan yarda da imaninta wajen malaman tsubbu da ‘yan bori dan haka bata da masaniyar cewa tufkar da take yi ta cikin gida ya gama warewa tas.

Wata rana kamar yadda akasaba “Zakiyya takaiwa Sailuba ziyara akan yadda suka kasa fahimtar jina ta waya,
“Nifa nagaji da wahala so nake na watsata tabi duniya ta lalace ta zama k’asaitacciyar karuwa bana buk’atar akai ga d’aura wannan auren”

“Humm Sailuba kenan wani lokacin kwwnyar ki atoshe yake wallahi, banda ke da abinki idanmma zatayi auren taya zamu bari tayi auren hutu?”

“Ni auren ne ma bana son tayi kwata kwata, so nake rayuwar ta ya wulak’anta fiye da duk wani wulak’antacce a duniya.

Tofa

Muje zuwa

Daga taku maman islam
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
????BA JININA BACE????
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Shafinki ne wannan’yar laleta SA’ADATU USMAN MUSA (ISLAM)
Allah ya rayamin ke tareda dukkan yayan musulmi badaya
Almustapha Usman Musa shalele na kenan kuma nagaban goshi Allah ya tsaremin ku.

Page 24

“Kina bani ciwon kai Sailuba nifa komai da kike gani da mugun shiri nakeyin sa, Kuma bana bawa na kusa dani damar gane akwai wani abu a cikin raina dan haka zai wuya kiga idan nayi, abu ayarda ni d’in ce nayi saboda babu fuskan da za a gane hakan, ke kuwa gajan hak’urin ki kawai ya isa tonaki, Kinga alhajina da kike ganinsa bansa me shi da sauk’i ba saboda mugun taurin Kai da Allah ya d’ora Masa, shi yasa kuma kikaga bana masa ta dad’i, domin naci bak’ar wuya kan nasame shi, sannan Kuma kina ganin har yau tak’i amincewa ta saurari Deedah shegiya mai kafirin wayon tsiya na rasa dalilin da yasa bata Sona”

Ta K’are dogon sharhin ta da k’orafin yadda Maryam take masifar d’auke mata kai ‘yar dariya haj. Sailuba tayi kafin tace” ashe kin manta da cewa nonon wannan shegiyar ‘yaalaman tasha, kai wannan mata ta zame min annoba a rayuwata nasa ta yadda zanyi maganin tsinanniya”

“Hum ai irin su idan dubunsu ya tashi cika saikin ji kamar kiyi musu kuka wallahi” cewar haj. Zakiyya cikin ya tsina fuska
Sun jima suna k’ulle k’ullensu.

Tana tunkaro gidan ta tuna da yadda bross ya rik’a kwala mata kira tanaji ta d’iba da gudu dan kar ya hanata fita, tunda suka sam d’an hutun nan ya wani sa mata ido yanzun ta lura aikin ma ba sosai yake zuwa ba sai jifa jifa damma yanzun Allah yasa ko ba kowa zata shiga d’akin Ammey suyi ta hira yadda Ammeyn take mata ne yasa ta jinjinawa k’aryar mamanta da tace Ammey muguwace ko kad’an bataga hakan ba saima wani irin mugun shak’uwa daya soma shiga tsakaninsu da Ammeyn ganin yadda take mata.

Sam ta manta da yadda ya rik’a kiranta ta gudu kanta tsaye ta shigo gidan har da yar wakar ta, daman tun fitar ta yake dakon dawowar ta.

Tana shigowa taji anyi ram da ita ya damk’e ta a bazata taji an rik’o ta sai abin yabata tsoro ta bud’e baki zatayi masa ihu yayi saurin toshe bakin da hannunsa yace “wa na kama?”
Sam ta manta da abinda ya farun dan haka ta hau rarraba ido tana neman hanyar gudu, gane hakan da yayi ne yasa yaja hannun ta zuwa Pat d’in shi.

Dan” Allah bross kayi hak’uri banjika bafa”
“To in bakiji ba taya kikasan mai ya faru wato bakijin magana ko my happiness?” ya fad’a yana kallon yadda tayi tsuruvtsuru shi wallahi dariyama take bashi, yadda duk ta koma kamar wadda ta aikata wani babban abu tun ranan da suka shirya yake kiranta da wannan sunan hakama Nassar ya daina kiranta da Adda ya koma my happiness.

Shiru tayi ba tare da ta tanka ba dan in bata ga dama ba itama wani lokacin muguwar muskila ce sai kayi ta magana tak’i tankaka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button