BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

bayan ta idar da sallar ne tayi zikiri da sauri ta tashi ta cire rigan ta hau shafe shafe kafin tagama har an kira Isha kasancewar lokacin magriba ya kwace mata sosai.

Sai da ta gabatar da sallar tayi karatun alqur ani mai girma kafin ta shirya cikin wasu riga da wando masu masifar kyau da daukar hankali farare kar, sai wani bluen rubutu da aka yi agaban rigar ONLY FOR YOU shine abinda aka rubuta, wandon kuma da kad’an ya wuce gwaiwar ta kayan sunyi masifar yi mata kyau ta taje dogon gashin kanta tayi parking d’inshi takawo wani bluen Vandana ta sakawa kanta ba d’an k’aramin kyau tayi ba haka nan ta hauyiwa kanta salfie da wayarta.

Tana cikin d’aukan kanta a hotunan MD da Nassar suka shigo d’akin tana ganin MD tayi masifar d’aure fuska, saboda abinda yayi mata d’azu, murmushi ya saki yana shafar gefen face d’inshi.

K’arasowa yayi kusa da ita ganin haka yasa ta maida kanta kasa tana wani cin magani, kafeta yayi da ido yanajin kamar ya had’iye ta tsabar masifar kyuan da tayi masa,
Hannu yasa ya d’ago habanta ya manna mata kiss a goshi kafin amshe wayan ya d’an rab’a ta da jikinsa kad’an ya soma d’aukar su hotuna.

Nassar yace “wow gaskiya bross kunyi kyau sosai kamar wasu masoya” da sauri ya dafe bakinsa saboda kallon dayaga MD yana masa fuskansa d’auke da wani irin murmushi.

“Nima ayi dani Nassar ya fad’a yana shiga tsakiyar su haka suka kasance ashiriri ce yayin da halin na Maryam ya motsa dan bata kula MD ba saboda abinda yayi mata.

Suna haka wayan Muhammad yai k’ara yana ganin layin Baffa na nageria yai saurin d’agawa”Allah ya temaki Baffa na” cewar MD yana sakin wani k’awataccen murmushi, duk shiru Nassar da Maryam sukayi jin MD ya ambaci Baffa

“Kuzo ka d’auke ni ina airport” shine abinda Baffa yace wa MD ya katse kiran “yeee” MD yafad’a da d’an tsallensa,duk suka kafeshi da ido kafin Nassar yace
“Baffa ne ya dawo?”
Hannu ya mik’a masa suka tafa “dad’i na dakai gane wa” inji MD yana murmushi “zo muje mu d’auko shi” yafad’a yana kama hannun yaron
“Nima zani” ya tsinkayo muryanta d’an juyowa yayi ya kalli kayan dake jikin ta sai kuma ya d’an girgiza mata kansa “gaskiya bazamu iya jiran har ki canja kaya ba yafad’a yana d’aure fuska”

“Dan Allah after kawai zan d’ora akai” ta fad’a cikin marairaicewa

” Minti biyu ya fad’a suna ficewa rik’e da hannun Nassar.

Taku ce MAMAN Islam
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
????BA JININA BACE
2021

             NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 26

Jikin mota ta same su sai zance Nassar yake zuba masa yayin da shi kuma hankalinsa yake kan phone d’insa yanata faman latsawa.

Kamshinta ne yasa shi saurin d’agowa ya kafeta da ido yayin da zuciyar sa ya hau wani irin bugawa har d’an rawa rawa jikinsa ya soma abinda bai tab’a faruwa dashi ba.

“Muje” ta fad’a cikin fad’uwar gaba saboda shegen kallon dataga ya kafeta dashi, aranta tana bitar kalaman Mama anya ba wani abun ta hangoba kuwa?

Take raya hakan aranta sanda take shiga cikin motar, “my princess dan Allah kintaho da wayarki ki aramin?”

Cewar Abdul Nassar da ya zuroda kansa ta b’angaren datake,
“Kayi me dashi?” ta tambaye shi batare da ta d’ago ta kalleshi ba
“Boy zan kira anty dan Allah”

Kafin tace mai wani abu wayan yayi k’ara hakanan taji gabanta ya fad’i ganin no ba suna da mamaki aranta tace waye Kuma yake kirana ?

“Ki daga mana” take tsinkayo muryansa,
Dagawar tayi ba tareda ta k’ara kallonshi ba kafin tayi magana taji ance
” Amincin Allah yatabbata agareki yake saurauniyar kyawawa” wani irin murmushi ne ya sub’uce mata, zuwa yanzun ta fara sabawa da halin d boy wanda yabi ya mak’ak’ale mata ga d’anbanzan iya kalami me sanyaya Rai”

“Tareda kai ma aboc………..wani irin burki da MD ya take ne yasaka tayi wani tsalle ta gwaru da murgin motar wayar Kuma bata fad’i ko ina ba sai saman cinyarsa.

Hannu yasa ya d’auke wayar ya zurata acikin aljihun sa ya ya zagayo a zuciye yace “zoki ki fice min a mota” da mamaki ta tsaya kallonsa domin bataga abinda tayi masaba da zaiyi irin wannan fusatar haka lokaci guda “zoki fita nace malama” ya fad’a cikin wani irin buga tsawa, ai batasan lokacin data fito cikin wani irin rawar jiki ba, tana kallonsa ya koma yaja motar sa da wani irin matsiyacin gudu ya bud’e ta da qura, agogon hannunta ta duba tara saura batasan lokacin data fashe da wani irin kuka ba ta daga kai tana kallon sama yadda wani irin hadari ya murtuke bak’i k’irjinta ta dafe dayake wani fitinannen bugu tace “na shiga uku ni mero, me kuma nayiwa wannan mugun mutumin da zai ajeni anan” ta fad’a afili cikin muryan kuka yayin da aka wani irin kece da ruwa mai mugun k’arfi ga Maryam da mugun tsoron hadari bare ya sauketa a wannan wajen da babu kowa sannan babu gida kusa, jitai wani irin tsanar shi ya dawo mata sabuwa dal, tafara takawa a hankali yayin da take kuka sosai jikinta na wani irin rawa.

Nassar kuwa ganin yadda bross d’in nasu yake wani irin tuk’in ganganci yasaka yai tsuru abayan mota yayin da tausayin Maryam ya cika ransa domin baiga abinda tayi masaba zai ajeta wajen da babu kowa sam bai kula da hadarin ba sai zuban ruwa yaji wanda yasa MD ta ka burkin dole.

Fashewa da kuka Nassar yayi da mugun k’arfi kafin yace fili “shikenan Addana ta mutu” yafad’a yana kuka sosai kafeshi MD yayi sosai kafin yajawo yaron jikinsa yana cewa “kai me kace?”

Memakon ya amsa masa sai cewa yayi”me tamaka bross zaka ajeta inda babu kowa ita kad’ai idan wani mugun abin yasameta fa?
Gashi kuma tana tsoron ruwan sama sosai idan ana ruwa babu inda take fita”

Sosai gabansa ya fad’i da maganganu yaron har baisan sanda ya tada motar batareda ya Kuma cewa komai ba ya figeta yana maijin haushin kansa akan abinda yay mata duk da cewa har lokacin zuciyar sa masifar zafi yake masa na yadda yaji tana magana da wani wanda yarasa me yasashi jin hakan?

Ita ko Maryam fara takawa tayi a hankali cikin wani irin tsoro jin yadda wajen yai tsit babu komai sai k’aran zubar ruwa yayin da zuciyar ta yake wani irin bugun dayasa jikinta rawa sosai tayi nisa da inda ya ajeta sosai tana tafi tana share ruwan dayake feso mata afuska wanda yake wanke hawayen dayake tafaman zubo mata babu ka’k’k’autawa.

Yana cikin tuk’in kiran Baffa ya k’ara shigowa faking yayi a gefe kafin ya d’aga “karka zo naga garin da hadari na hau tixi” abinda Baffa ya fad’a kenan ya kashe wayar batare da yace komaiba, saboda kar Baffa ya gane halin da yake ciki.

Sanda yazo inda ya sauketa ta ya rage gudu sosai zuciyar sa ya buga dan ganin bata wajen yayin da Nassar ya kuma fashewa da kuka dan a tunaninasa wani abun ne yasamu ‘yar uwarsa.

“Dalla malam ka karka damemu ka rufe mana baki d’if ya d’in ke bakinsa saboda yadda yaga bross d’in yai wani irin canza kama fuskar nan tayi wani irin ja yayinda ya soma zargin kansa akan abinda yayi mata sam baiga kyautawar saba ko kad’an.

A hankali ya cigaba da jan motar yana d’an duddubawa ko zai ganta Maryam wacce taci kuka ta k’oshi ga d’an banzan dukan da ruwa yake mata wanda yasa wani mugun zazzab’i ya saukar mata lokaci guda ta sami gefen hanya ta zauna tana ta faman shashshek’a.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button