BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Plss manage

Daga taku MAMAN ISLAM CE

بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
???? BA JININA BACE????

2021
NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 29

Wanka tayi ta tayi alwala dake lokacin an fara kiran Azhar dan haka tana gabatar da sallar ta shirya tareda daukar bag d’in ta ta fito babu kowa a falon sai Ammey.

“Ina zaki haka?” Ammey ta tambaya tana kallon fuskar ta dayake cike da damuwa’ kamar bazata tanka mataba sai kuma tace “shopping” kamar maijin tsoro tayi maganar”
“Zonan” Ammey ta kirata kallon Ammeyn tayi kamar tayi mata gardama sai kuma ta karasa kusa da Ammeyn ta zauna ta d’an jingina jikinta dana Ammeyn,abinda bata tab’a yiba iya tsawon shekarun datayi a hannun haj. Sailuba batama samu anbar ta taje inda take ba bare ta rab’etan.

Wata irin ajiyar zuciya Maryam ta sauke mai k’arfin gaske lokacin da ta kwantar da kanta jikin mahaifiyar ta ita kanta Ammeyn sai dataji wani iri aranta bata san sanda wasu irin hawaye suka zubo mata ba tayi saurin gogewa dan kar tagani.

Duk inda uwa take ko a ina ne ko a wane hali take ta fita daban hakanne ya kasancewa Maryam jitai wani irin nutsuwa na shigarta tareda wani d’an Karen sanyi da ya dirar mata lokaci guda alamun zazzab’i keson kamata.

Haka nan batasan dalil ba kawai taji ta kama hawayen da batasan ko na menene ba tun iya hawayen ne har tafara shashshek’a, a rud’e Ammey ta d’ago fuskar ta tana kallon yadda take shashshek’a kallon lips d’inta tayi yadda suke rawa sosai batasan sanda ta k’ara k’ank’ame ta ba tana d’an buga bayanta kad’an kad’an batare da tace komai ba domin tasan tabbas itama idan tayi magana nata kukanne zai fasu.

Sai da suka shafe ak’alla mintuna uku kafin Ammey ta d’ago ta ta fara share mata hawayen “me yake damunki?”
Ta tambaye ta ahankali kamar tana jin tsoron wani yajita tace “Ammey jikin yafi na Mama dad’in kwanciya kuma ga d’umi,dan Allah Ammey nima ki rik’a rungumeni kamar yadda kike wa Nassar”

“Naji amma sai kin fad’a min abinda yake damun ki kwanakin nan, na lura kina da damuwa keep ki fad’a min koda ahawaran da zan baki” kallon Ammeyn ta dingayi babu k’ak’k’autawa yayin data ta dinga jin wani abu mai sanyin gaske yana ratsa ta, tunda take da maman ta bata tab’a tambayar ta damuwanta ba sai dai idan taganta a damuwan ta d’ebi manyan kud’ad’e ta bata tace taje ta kore damuwan ta.

” Ina jinki’yar albarka maza ki fad’amin ki d’auka cewar kina fad’awa mahaifiyar ki ne kima sa aranki cewa ni mahaifiyar kine zan miki maganin duk wani damuwaki a duniya,wanda kuma yafi k’arfi na zan fad’a wa ubangiji na”

Ammey ta fad’a tana saurin goge hawayen daya zubo mata dan kar ta gani Muhammad dayake tsaye bakin k’ofar tun sanda Ammey ta kira Maryam ya saki wani boyayyar ajiyar zuciya aransa yana fatan Allah ya karya ak’adarin haj. Sailuba.

“Ba komai” ta fad’a a hankali “kwai baby command fad’a min kinsan babu kyau d’a ya rik’a wa mamansa k’arya” batasan sanda ta rushe da kukaba tace “Ammey k’udi sune maganin ko wane matsala?”
Ta tambaye ta abinda yafi komai damunta a rayuwarta
” Injiwa?
Duk wanda ya fad’a miki wannan k’arya yake ko waye yana yaudarar kine kawai, amma akwai abinda k’udi bai isa yayi maka shi ba da yawa ma a duniya dan haka duk wanda ya fad’a miki hakan yayi karya ya fad’i son ransa ne kawai”

Ta fad’a tana shafa kanta nan “Mama ce koya ta ganni a cikin damuwa sai ta d’ebi manyan kud’ad’e ta bani tace zasuyi min maganin ko wace irin matsala a duniya” duk da cewa tasan zata iya jin abinda yafi haka daga d’iyar tata ma amma hakan sai yayi masifar d’aga mata hankali tace

“Tana iya miki kyautar nawa lokaci guda?” Ta tambaye ta cikin tsantsar tashin hankali “har dubu d’ari biyar cash tana bani tace muje mu kama waje muyi d’an kwarya kwaryan walima wai na jikina ma su mori arzik’in ubana”

“Kina yi?”
Ammey ta k’ara jefo mata wani tambayan “da inayi amma yanzun tara k’udin nakeyi da sukayi yawa na sai gida kuma da wasu kusan 7 million a d’akina har sani fa take na d’ebo mata k’udin Baffa kinsan baya k’irga wa yake ajiyewa”

“Innalillahi wainnailahi raji un” shine abinda Ammeyn ta fad’a cikin tashin hankali “Allah sarki Nanne da Anty shamsiyya yau ga abinda kuke fad’a min yana shirin faruwa tayi maganar cikin zubowar wasu zafafan hawaye.

Da sauri ta share hawayen tace”kin yarda dani zaki iya bani ajiyar duk abinda kika mallaka?” Ta tambaye ta cikin rawan murya
” Eh Ammey me zai hana ta bata amsa yayin da wani irin sanyi yake kwaranya aranta
“Yayanku fa?” ta k’ara tambayar ta
“Tab’ni bazan bashi ba mugu ne gashi masifaffen tsiya ta fad’a tana hararan gefe.

Murmushi Ammey tayi shi kanshi Muhammad dake bakin k’ofar maganar ta ya bashi dariya dan haka ya d’an murmusa yana shafar k’irjinshi a hankali kamar wanda wajen yake masa ciwo

“Kece baki gane halinsa ba amma yana da kirki sosai kuma zai kula daku sosai koda ace yau babu Baffa baku da sama dashi SHINE GATANKU”

Tab’e baki tayi ta mik’e tana cewa “anjima zan kawo miki A T M d’ina Mama bata san dashi ba saboda shegen kashe k’udin ta idan ta sani duk saita rance kuma ba biyana take ba, tunda kince kin yarda dashi sai ki bashi zan had’a shi kuma da na siyi gida ta hanyar sa wallahi ya cinye kwandala ta bazai yi ciwon kai ba biyana zaki”

Duk yadda yaso dauerwa saida ya fashe da dariyan maganta domin ta bashi dariya sosai wallahi, ita kanta Ammeyn murmushi take kafin tace “yanzun to ina zaki naga ko abinci baki ciba”

Eh banjin yunwa zanje shopping, ina Nassar ya rakani?”
“Za daiki siyan kayan zakin da kika saba maza muje yau nima na fanshi hajiyan tunda bata nan muje na baki da kaina tunda ta gama shagwab’a ki”
Sai taji ta kasa yi mata musu tana zuba mata abincin kafin ta fara bata MD ya shigo wajen da sallama Ammey ta d’ago ta dubeshi ganinsa da kayan gida tace “yau kuma ina uniform d’in?”

“Banje office ba yau?” Ya fad’a yana zama facing d’in Maryam datai wani kicin kicin da rai, murmushi ya saki lokacin da ya juyo da hannun Ammey santar bakin sa ya amshe abincin da ta d’ebo zata kaima Maryam baki, bata san sanda ta b’alla masa wata shegiyar harara ba ta juya ta kalli Ammey a marairaice tace Ammey”

“K’yale shi baby in yasa tsiya yanzun zan korashi amshi maza kici ki k’oshi kinji yarinyar kirki ta fad’a tana bata, sosai taci abincin, tunda take zata iya runtsawa cewar bata tab’a samun farin ciki irin na yau a rayuwarta ba sai taji Ammey ta bala in kwanta mata arai.

tana gamawa tasa tusio ta goge bakinta ta zari mukullin motar ta”sai na dawo Ammey”
“Baki ba Ammeyn ta fad’a tana mik’ewa ta k’arasa kusa da ita kanta ta dafa tayi mata addu’a sosai kafin tace “Allah ya tsaremin ke ki kula da kanki ki kare mutuncin ki domin shine Martaba ki”

Wani irin sanyi Maryam taji aranta ta rungumeta ta tace “na gode sosai Ammey dan Allah ki rik’a min haka please”
“Kullum nake miki haka amma ba kusa da kusa ba amma ko yaushe kece farkon wacce nake fara yiwa addu’a kafin nida kaninki da sauran makusanta na”
“Allah Ammey?” Maryam ta tambaya ciki farin ciki tare dajin yadda matar tak e k’ara bin dukan jikinta, dama haka halin Ammeyn yake amma mama tace muguwa ce.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button