BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
???? BA JININA BACE????

2021

            NA

HASSANA ABDUL AZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 30

Rungumeta ta k’ara yi tace “na tafi Ammey na”
“Sai kin dawo’yar albarka”
“Nima zan rakaki zaki siyamin chocolate?”
Yayi mata yadda Nassar yake mata, batasan sanda ta saki murmushi ba ta fice a daga wajen cin abincin, binta yayi shima domin yi mata rakiya.

Tayi zaton shi zai jasu, sai kawai taga ya bud’e wajen mai zaman banza ya k’ame abinsa, tura baki tayi tana d’an hararansa ta gefen ido, sarai ya ganta sai ya mai da kansa gefe yana d’an murmushi hakanan yanzu komai tayi burge shi take.

Sai da ta zauna ta sakarwa mai gadi k’aton hon wannan ba sabon abu ba ne awajenea sam indai zatayi tuk’i batayin na nutsuwa tun lokacin data ke a matsayin Maryam ba yanzun da ta zama mero ba lol????????????

Shi kanshi Muhammad sai da yai mamakin ganin yadda ta wani figi motar da masifar gudu bai san sanda ya juyo yana kallonta ba “ke baki da hankali ne?”
Ya fad’a lokacin dayaga ta kusa fad’awa wani d’an rami dake tsakiyar titin data hau tayi wani irin kaucewa ramin
“Princess tsaya” ya da sauri yana dafe kan sa da duka hannayensa.

Babu musu ta nemi waje ta faka dama da biyu ta keyi dan ya amsa banda son banza tana tare dashi d’in zata zauna ta jashi????????????

Canjin wajen zama sukayi ya amshi tuk’in yana fad’in”naga alamun ke kin shirya mutuwa ni kam gaskiya bana so na mutu banyi aure ba”
Ya fad’a cikin barkwanci.

Murmushi kawai tayi bata tanka masa ba, sai ma wayar ta data d’auko ta bud’e data tana chat da friend d’inta tana duba no d boy babu shi kwata kwata a jerin contact d’in ta da gaske yake ya goge.

D’an kallonsa tayi sai akayi sa a shiama ya wago yana kallonta ta gira ya dage mata alamun ya dai?
D’auke kai tayi tana tuna hargagin sa na d’azu akan mama wani lokacin bata cika ganin lafim su ba domin halin mama sai mai hak’uri.

Kusan sau uku tana kamashi yana kallonta kuma duk sanda zasu had’a ido sai yamata alaman yadai?
Sai kawai ta hak’ura bata k’ara kallonsa ba har suka isa sper market d’in da yawanci anan suke siyayya duka ‘yan gidansu.

Bayan ya samu waje ya faka ya bud’e ya fito sannan ya zagayo ya bud’e mata bayan tagama gyara mayafinta ta fito a hankali ya Mai da motar ya rufe ya kama hannunta suka fara jerawa cikin wajen.

Duk inda suka gifta sai idanu sun bisu saboda masifar kyawunsu da kuma yadda sukayi macin d’in da mutane sukayi da juna.

Sunzo shiga shi Kuma d boy sun zo fita shi da abokansa ya gansu sai da gabansa ya fad’i ganin ta tare da wannan gwaskan yayan nata ya wani kafesu da ido har suka k’araso inda suke, sai lokacin ma Maryam ta kula da d boy ta d’an saci kallon MD wanda gaba d’aya hankalin sa yake kan wayar sa.

Sai da tagawa d boy hannu ne shi kuma kamar wanda akace ya d’ago sai kawai yabi hannunta da kallo lokacin shima d boy ya d’ago mata tare da wani irin mumushin farin cikin ganin da yayi, kafesu yayi da wani fitinannen kallo zuciyar sa ya hau wani fat fat fat ko ko kad’an bai damuwa da labarin mutane amma ko cikin miliyan sai ya fidda d’an jakin mutumin can, kuma ko da ace shi bai son Maryam wallahi datayi mu ‘amala da wancen gwamm ace masa ta mutu ne shi zai fi masa sauk’i.

Sam bata kulla da kallon da yakafe d boy da shi ba amma shi d boy yana ankarewa take jikin sa ya hau rawa ta ina zai manta da wannan basumuden mutumin wanda babu abinda ya ajiye sai mugunta tsantsar ta, kafin Maryam tayi wani motsi d boy ya b’acewa ganinta, ta d’ago kai da zummar yiwa MD magana yadda taga yayi kicin kicin da rai sai da gabanta ya fad’i ta d’auke kai aranta tana tunanin anya wannan bashi da aljanu?

Duk abubuwan data siya shine ya biya k’udin, suka fito daga wajen har lokacin babu annuri atare da shi dan haka taja bakin ta ta tsuke bata k’ara kallon inda yake ba.

Mai makon ya wuce gida kai tsaye taga ya d’auki wani hanya daban amma dake haushin sa take ji bata dube shi ba bare tayi masa tambayar inda zai kaita, har suka isa wani d’an madaidaicin gida mai kyau ya faka motar a k’ofar gidan ya fita ya kwankwasa aka bud’e masa wanda m Bash ya ganine yasashi hangame baki

“Amma dai b’atan hanya kayi ko MD” m Bash ya fad’a yana d’an rik’e baki, harara MD ya zafga masa yace “aini gwanda ni na kawo maka ziyaran kai yaushe rabonka da inda nake? Kuma yanzun ma ba wajenka nazo ba wajen madam nazo tana dai ciki ko?”

” Hum tana ciki mana ina zata bayan gani yawo ai sai ku manyan gwaraye”

Harara ya galla masa batare da yace masa koma mota, har lokacin bata saki ranta ba hannunta kawai ya kama batare da yace mata komai ba ya nufo gidan.

Ido ta d’an waro lokacin da suka tunkaro gidan, yayin da shi kuma ya sakar mata murmushi,itama murmushin tayi masa ta d’an rusuna ta gaida shi kafin ‘ yace ta wuce ciki,

Kallo MD ya bita dashi har ta shige kafin ya maida hankalin sa kan m Bash da yafe shi da ido’
” Muje man munafiki ka wani zubamin ido kamar zaka cinye ni” murmushi m Bash yayi kafin yace “SON TA KAKE KO?”
“Na fad’a maka”
“Sai ka fad’amin gashi nan ina ganin sa acikin idanunka”

” Hum abokina ban san sanda yarinyar nan tayi tsalle ta daki zuciya naba lokaci guda sonta yamin wani irin kamu wanda har ya fara tab’a wasu daga cikin al’amurana na yau da gone”
“Ka fad’a Mata?”
“Ban fad’a mataba”
“Me yasa?”
” Inajin tsoron kar tace bata sona duk da nasan cewa idan nace ina sonta ko bata so sai an bani ita”

“To kajarraba Mana”
Ta yaya bazan iya ba ina matuk’ar jin tsoron kada tace a a” ya fad’a cikin tsananin damuwa sosai

Sosai m Bash yaji yana jin tausayin abokin nasa dafa kafad’ar sa yayi yace “abokina kada ka bari ya huce” daga haka yaja hannunsa zuwa cikin gidan.

Har Hajara matar m Bash ta tarb’eta duk da cewa bata santa ba amma ta cika mata gabanta da kayan makulashe suna d’an tab’a hira sama sama dake Maryam bata da bak’unta sam.

Kusa da ita MD ya zauna yana kallonta tare da tunanin ta yadda zai fara taranta da maganar musamman idan ya tuna irin kallon da take masa.

Ji ta ta takura da kallon daya takura masa dashi d’agowa tayi ta d’an kalleshi kafin ta kauda kanta tana hararan gefe

Taku ce MAMAN Islam
بسم الله الرحمن الر حيم
______________________

FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION

FCWA

{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*____________
???? BA JININA BACE????

2021

          NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Page 31

Kayan da Hajara ta aje mata ya kalla yaga babu abinda ta tab’a, sai ya d’an dubeta yaga yadda take ta faman hararan gefe ta wani turo baki gaba baisan sanda ya saki murmushi ba, yasa hannu ya d’ago hab’an ya kafeta da wani shegen kallo.

Ganin haka yasa m Bash ya janye matarsa suka bar musu falon, kasa daurewa kallon nasa tayi sai kawai tayi saurin rufe idanunta.

“Waye shi?”
Ta tsinci muryarsa yana mata tambayar da bata san inda ya dosa ba kallonsa take da alaman tambaya a fuskar ta itama?.

“Wanda ya d’auke miki hankali a sper maket?”
Yanzu kam kallon shi take da madaukakin mamaki, yadda yai bala in d’auke mata kai har kawo zuwansu nan batayi tunanin zai kula da hakan ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button