BABU SO HAUSA NOVEL

BAJININA BACE COMPLETE HAUSA NOVEL

Tazo shiga d’akin suka gwabza karo da MD wanda yazo neman ta ta tsaya da Ammey wacce ya gama duba zai nemo mata magani, take tayi baya zata fad’i da sauri MD ya taro ta ya rik’e ta yana kallon yadda jikinta yake rawa

Suna had’a ido da shi ta fashe da wani irin kuka har da shashshek’a, ina ma ace Ammey ce maman ta ba wannan matar mai bak’ar zuciya ba, inama ace hannun agogo zai dawo baya data rok’i ubangiji ta fito a tsatson Ammey, sai dai Kash d’an Adam bashi da damar zab’a ma kansa rayuwa sai yadda ubangiji yayi da bawan sa,

“Allah kaza gatana Allah kazama gatana Allah kazama gatana” take ta maimaitawa cikin tashin hankali da wani irin fitinannen kuka, baisan lokacin da yajata jikinsa ya rungumeta da mugun k’arfi hannunsa na wata irin rawa ya d’ora abayan ta yana shafawa a hankali.

Jabbar Mama ta koma saman gado ta zauna tare da d’ora hannunta saman kanta tace “shi kenan na shiga uku taji komai wayyo Allah yau dubana ya cika innalillahi asiri na zai tonu”

Jiki na rawa ta ja waya ta kira haj. Zakiyya tun kafin ta d’aga tace “shi kenan k’awata yau taji komai dakanta ta kamani muna waya dake shikenan zata had’a ni da Baffa na shiga uku na lalace”

“Ke taya akayi kika san tajiki ba kince sun fita da Amina ba?”

“Wllh taji karkiga mugun kallon da take bina dashi dana ganta ma zan wayance bata saurare ni ba juyawa tayi da gudu ta fice”
Kinsan ya za ayi?”
“A’a”

“Zuwa zakiyi kiji idan kin tabbatar da taji abinda muka tattauna sai kibi duk hanyar da zakini nuna mata cewar kunnenta bai juyo mata daidai ba” daga haka suka yi sallama ta mik’e tayi d’akin Maryam.

Tana d’aga labulan tayi wani irin baya cikin girgizar zuciya batasan sanda ta kurma wani mugun ihu tace” jama’a kukawo min d’auki kwarto zai lalata min ‘ya”

A firgice duka suka juyo suka kafeta da ido yanayin sa ba karamin firgita ta yayi ba tayi saurin k’asa da kanta jikinta yana wani irin masifaffen rawa,bata san sanda ya k’arasa kusa da itaba yace adaidai kunnen ta yace “ajiyar ki tananan acikin lambun na bar miki”

A firgice ta d’ago tana kallonsa kafin tayi wani luuuuuu ta zube awajen tsabar tashin hankalin jin abinda yace mata

Plss manage

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الرحيم

☀️ FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION ☀️

FCWA

Home of qualities and trusted writers of the nation

https://free.facebook.com/111719967001810/photos/a.111720050335135/116072649899875/?type=3&source=45&refid=17

???? BA JININA BACE ????
2021

    NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

PAGE 44

Da sauri Maryam ta nufeta, yay saurin tareta yana kallon cikin idonta da kallon kar ki soma.

“Mama nace fa” ta fada a raunane “maman naki ban lamunta ba kibar ta zata tashi ga Ammeyn ki cen ciwon zuciyar ta ya tashi” da sauri ta kafe shi da ido gabanta yana wani irin dokawa tace “ba yanzun muka dawo daga unguwa ba?”
“Eh kinsan al’amarin ubangiji babu yadda baya juyawa bawa kuna shigowa bayan shigewar ki ciki ta yanke jiki ta fad’i, yanzun ma magani zan amso mata na gama dubata.

A hankali ta juya ta kafe mama da wani irin kallon tuhuma da tsoro tace “kece ko?”
Mama da tun da ta fad’i take wani irin kukan zuci mai azabar radadi tayi saurin girgiza kai, alamun babu ruwanta.

Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tare da kwafa ganin yaja hannunta sun fice,.
“Sai naga bayanka wallahi Muhammad tunda kayi sanadin rusamin shirina saikayi nadamar yin hakan dan haka nice ajalinka wallahi saikayi nadamar shiga rayuwana da kayi” ta mik’e tashige d’aki tana sakin kukan bak’in ciki.

Yanayin da taga Ammey yasa ta k’arasa da sauri ta rungumeta tareda fashewa da kuka tace “Ammeyna me ya sameki daga dawowar mu?
Kodai akanki ne naji mama na waya?”

Kafeta da ido Ammey tayi batare da tace mata komai ba yayin da zuciyar ta yake mata wani irin fitinannen suka, batasan lokacin da ta fashe da wani irin kuka ba mai mugun cin rai.

Ita ma maryam fashewa tayi da kuka tare da k’ara k’ank’ame Ammey tana fad’in “sannu Ammey yana miki zafi ko zai daina kinji dan Allah ki bar kukan nan haka yana Kona min rai.

Wani mugun kukanne ya kuma taho mata tayi saurin toshe bakinta da hannun ta tana jin wani mugun tausayin Maryam yana kamata, ta sani rayuwar Maryam yana cikin gagarumin matsala, tasan Sailuba tasan wacece ita muguwa ce azzalumar matar da batasan Allah ba babu d’igon tsoron Allah a tareda ita makira ce ta ajin k’arshe bata da imani ko k’ank’ani.

“Maryam kiyi hak’uri da rayuwa ki gyara d’abi’unki duk da kasancewar naga sauyi mai yawan gaske atare da ke, amma ina so kisani rayuwa bashi da tabbas, idan yau mune gobe ba mu bane, dan Allah zan rok’eki duk halin da kika tsinci kanki, ki kasance mai yawan godewa Allah, ki kare Martaba da kimar ki na d’iya mace k””””””””’ya isa dan Allah ya isa Ammey ki daina min irin wannan zantukan masu kama da wasiyya, daga kinyi d’an zazzab’i sai ki kama wasiyya kamar mai shirin barin duniya yanzu yanzu, insha Allah sai kinga jikoki na” ta fad’a cikin matsanan cin rawan jiki ga kukan da take ya kasa tsayawa tsabar tashin hankalin da kalaman Ammey suka saka ta a ciki.

Wani irin murmushi tayi mai ciwo sannan hawayen ta basu bar zuba ba, sannan bata fasa yiwa Maryam nasiha ba akan rayuwa da zaman takwar mutane tare da fad’a mata yau da gobe kai ranan dai babu wani jin dad’i a wannan gida.

Acan k’auye kuwa bayan Baffa ya isa ba k’aramin farin ciki Inna tayi da ganin tilon d’an nata ba, sai dai shi kad’an sa ta ganshi babu maryam kamar yadda yadda ta buk’ata, hakan bai wani bata mamaki ba tunda tafi kowa sanin halin Sailuba “kai wannan yarinya Allah dai ya shirya, Allah kanaji kuma kana gani na fita hakkinta na bata tarbiyya gwargwadon iyawa ta Allah karka kamani da laifin gurbacewar halinta dan alfarmar fiyayyen haltta (S A W).

Nan falon ta tayi masa shimfida ya zauna takawo masa ruwan randa mai sanyi da fura wacce taji lafiyayyan nonon shanu zuryan, kasan cewar tasan da zuwan sa.

Sai da suka gama gaisawa sannan ya soma furar kasancewar yana sonta sosai yana sha suna d’an tab’a hirar duniya da Inna wanda duk rabin sa nasiha ne da shawarwari cikin hikima.

Bayan ya kammala ne ta dubeshi tace “kaje kasamu kawun Muhammadu dan a tsaida daidai lokacin da za a d’aura auren Maryama da shi Muhammadun dan insha Allahu jibinnan za’ayi babu jinkir tawa”

Da sauri Baffa ya dubeta yace “jibi kuma Inna?”
K
“Ko ban isa zartar da hukunci akan jika ta bane?”
“A haba Inna kin isa har kinyi yawa”
“To katashi kaje ka dawo kazo ka amshi naka iv da zaka rabawa ‘yan uwa da abokan arzik’i, saboda nasan shiriri tarka shiyasa nasa aka buga har kai, sannan magana tagaba Baffa koda wasa Sailuba kar tasan jibi daurin auren Maryama domin na fahimci ita d’in fitina ce arayuwar Maryama, kai wannan yarinya Allah dai ya ganar da ita”

Daga Baffa ya fita zuwa gurin yan uwan marigayi aminin shi Hassan

MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الرحيم

☀️ FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION ☀️

FCWA

Home of qualities and trusted writers of the nation

https://free.facebook.com/111719967001810/photos/a.111720050335135/116072649899875/?type=3&source=45&refid=17

???? BA JININA BACE ????
2021

    NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

PAGE 44

Da sauri Maryam ta nufeta, yay saurin tareta yana kallon cikin idonta da kallon kar ki soma.

“Mama nace fa” ta fada a raunane “maman naki ban lamunta ba kibar ta zata tashi ga Ammeyn ki cen ciwon zuciyar ta ya tashi” da sauri ta kafe shi da ido gabanta yana wani irin dokawa tace “ba yanzun muka dawo daga unguwa ba?”
“Eh kinsan al’amarin ubangiji babu yadda baya juyawa bawa kuna shigowa bayan shigewar ki ciki ta yanke jiki ta fad’i, yanzun ma magani zan amso mata na gama dubata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button