BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL
Kamar wasa taji, alamar yana kuka
Dasauri tace Yaya kuka kake?
Cikin shashshekar kuka yace Amal Yaya zanyi da soyaiyarki?
Innalillahi karde zancan su umma da gasken ne
Cikin kuka nace nashiga uku yaya
Yace Amal, Babu yanda zanyi, dole in hakura dake
Tunda baba yariga yayanke hukunci
baba yayimin komai Amal, BURINAH inso abinda yake so Koda kuwa ba shine ra’ayina ba
Yaya kayafemin kula Yaya sham danayi
Insha Allah bazan sakeba Yaya nayi laifi
Amma Yaya wallahi banasan wannan mutumin
Banasan sa Yaya
Please Yaya kadawo baba yayi mana aure
Hawayen idonsa yagoge yace bazai iyuba Amal, bazai iyuba, karmu maida mahaifinmu mutumin banza
Wayar sa yakashe yana goge hawaye
Kamar wasa okasha yaji kuka, yana juyawa yaga Shahid yana goge hawaye
Subhanallah, Shahid meyake faruwa?
Kamar jira yake a tambayeshi nan yaci gaba da kuka haiqan, yana cewa shikkenan narasata okasha
Okasha narasa Amal, yarinyar nan da soyaiyarta na rayu acikin zuciya ta
Jikin okasha yayi sanyi,ya janyo shi jikinsa yana rarrashinsa
*** *** ***
Ungo wannan karbi Kisha, umma menene wannan din? Bansaniba yarme tsinannan surutu
Bata qara maganaba takarbi maganin ta shanye
Umma zanje gidansu rumaisa, bazaki ba, kije nan gidan hauwa’u tana neman ki
Babu yanda ta iya haka zura hijabin ta tatafi, tunda bikin nan ya matso ake dirka mata wannan magungunan, tarasa na menene
Ko duk Dan wannan gunkin sukeyi oho
Tana zuwa gidan anty hauwan ma, magani tahada mata tasha, wani kuma tabata su aleda Wai tanasha kullum idan ankaita bauchin
Koba bauchi ba
Zasuga bauchi
*** *** ***
Alhaji kaide kadage Akan auren nan, wallahi kuwa hajia, aure kamar anyi angama insha Allah
Yatsina fuska tayi, tayi shiru batare data qara cewa komai ba
Ina agogon nan nawa?
Wai agogon daka siyo a Qatar kaida president?
Eh shi bani shi,
Tana kawo masa yasaka, yagyara Zaman babbar rigar sa, ya kalleta yace Toni ke kin zauna ko yau bazan samu afesa min turaren ba?
Batace komai ba ta tashi tana cika tana batsewa, tafesa masa, yace yauwa kokefa
Angama saka akwatunan acikin motar?
Eh angama alhaji
Tosh mu muntafi saimun dawo, shi daddy yacemin yana jiran
Jabir, jirgin su zai sauka nanda 20 minutes
So zasu biyo mu daga baya
To alhaji Allah yakaiku lafiya, Allah yatsare Amin hajia
Yana fita suka shiga motoci shida tawagar yan daurin aure, basu zarce ko Inaba Sai jigawa state
*** *** ***
Jb, Babu inda zani, Akan wannan qanqanuwar yarinyar zanje indebowa kaina gajia, wallahi bazaniba
Jirgin ku yasauka da niyya nace masa Kai nake jira
Haba daddy, Abba nefa, meyasa zakai masa qarya? To Jb ya zanyi? Wai kasan yarinyar dayake shirin aura min ne? Yaushe ma Salman ta rasu?
Yarinyar fa batafi shahida ba, haba me zan tsinta ajikin ta?
Daria Jb yasaka
Yace a a fa daddy karka zo kana qaramar murya daga baya
Kai yarinyar fa nakasashiya ce, wallahi batada lafiya, liqamin ita ake so ayi
Kafin Jabir yayi magana wayar daddy tadau qara
Gabansa ne yafadi dayaga sunan Abba baro baro ajikin screen din wayar
Ahankali ya amsa, acan kuwa Abba yanata Fama da jama’ah Ana jiran ango yazo a daura aure tunda yace zasuzo daga baya
Abba yace Ina kuka tsaya ne, har yanzu shiru babu ku
Sumar kansa yashafa yace Abba Mota ce ta lalace mana ahanya
A a Mota ta lalace muku bazaku tsaida wata ku taho ba, yanzu Yaya kukeso ayi?
Abba kawai a daura
Abba yanajin haka yashaidawa mutane ango Mota ta lalace musu
Dan haka a daura aure
Babu Bata lokaci aka daura auren
Amal da karaam, Akan sadaki nera dubu Dari biyu, lakadan ba ajalan ba
Comments ????
Mrs Usman ce ✍????BURINAH ????
(A Romantic love story)
Writing by Amnah El yaqoub
Bismillahir-rahmanirraheem
10
Agida kuwa anata hidimar biki, yan’uwa daga Niger sunzo, sai kuma maqota da yan’unguwa dasuka yiwa umma Kara suka zazzo
Nikuwa muna daki nida rumaisa Sai qawaynmu yan islamiya dasuka zo mana
Ajima kadan in goge hawaye, naqiyin wata kwalliya, mutane kowa Sai magana yake in tashi in shirya, na zauna Ina kuka kamar Wanda akamin dole, maisah ce mai kareni da cewa kukan rabuwa da umma ne, dahaka take rufe musu bakinsu
Da mutane suka ragu maisah tace Amal banga angon namu ba, ai yakamata ace yazo kun gaisa ko
Idanuna jajir nace maisah basai yanaso ba zaki ganshi
Shimafa bayaso, ninarasa dalilin baba nayin wannan aure, tunda babu Wanda Yake so kawai a rabu damu,
A a Amal duk abinda babba yahango yaro bazai hangoba, kede kiyi biyayya da hakuri Dan Allah Amal
Nace to maisah ta
A kofar gida kuwa, Ana gama daurin aure aka shigo da kayan lefen akwatuna dozin biyu
Baba yace ai alhaji ku koma da wasu kawai, kayan sunyi yawa, Abba yace haba Malam Muda muke cewa sunyi kadan, Dan Allah kadena wannan maganar adauki kayanta abata, haka aka shiga dasu gida, jama’ah kowa yagani, yana tofa albarkacin bakinsa
Abinci kuwa Sai kawo shi ake baqi kowa yaci yakoshi babu laifi anyi musu karba ta mutunci
Bayan azahar aka fara shirin tafiya bauchi tare da amarya, baba hamani yace shi bazai jeba, tunda akwai yan’uwa dazasuje su Gano inda take, hannun ta yakama da kansa yace alhaji ga amanar Amal nan, batada kowa ku kadai tasani, alhaji bazamu lamunci aciwa Amal mutunci ba, ko waye tsaf zan hawo Mota inzo in dauki yata mu tafi
Abba yace haba Malam, ai Amal kamar ya take awajena, batada banbanci itada daddy, insha Allah baza’a samu ko wacce irin matsala ba
Haka iyayenta sukai mata fada, aka daukesu Sai bauchi, hannun ta yana cikin na rumaisa
*** *** ***
Shahid Ana Kiran wayarka fa
Yana daga kwance yace inaji okasha, wannan Yarinyar ce, kabarta idan tagaji zata dena ai
Haka wayar taita ringing, karshe ma Sai ya kashe wayarsa baki daya
Shahid wannan tunanin fa babu inda zai kaika, ni a ganina tunda yarinyar nan anriga anyi auren ta, kawai ka hakura, ga wata anan yarinyar nan tana Mutuwar sanka, meyasa bazaka amince ba
Kallan okasha yayi da kyau, okasha? Kalau kake kuwa? Ni in auri wa? Yarinyar da batada aiki Sai tallar jikinta a titi
Tana ganin hakan shine wayewa, tayaya zan auri sauran kallan wasu
Hmm ajiyar zuciya nazy yasauke, daya gama Jin duk kalaman su, yace Lalle Shahid kana da aiki agabanka, to yanzu a Ina kake tunanin zaka samu irin yarinyar dakake so?
Kullum cikin hijab
Bafa zaka samu ba
Zan samu nazy, Amal, Amal dina haka take, dahaka nayi Mata tarbiya tun tana qarama
Amal Amal Amal, kaide komai Amal, to yanzu de matar wani ce, tunda tariga da Tafita daga hannunku
Lover boy kadau qaddararka kawai
*** *** ***
Kema de shahida da tsinannan naci kike, kin kira yaqi yayi picking, kinsake kira yakashe wayarsa, Amma ahakan zaki debi jiki kibishi gidansu, wallahi ni DANA SANI ma daban fada miki inda gidan yakeba
Sunkuyo wa tayi daidai fuskar jamcy, tace inde naci yana bada soyaiya, to naci na zai bani soyaiyar sa
Tamiqe ta dauki jambaki ta shafa, Dan qaramin mayafi ta dauka tayi rolling, sosai tayi kyau, doguwar face dinta ta tsaru
Jakarta ta dauka, tace Shahid na shahida ne, Babu me shiga tsakanin mu
Jamcy batasan lokacin datasa daria ba, ta kwanta, tace Allah yadawo dake lafiya, ban fara shirya karbar dizgi awajan da namiji ba
Tana fita Bata zarce ko Inaba, sai gidansu Shahid
Nocking tayi, suka Bata damar shiga
Dukansu suna falo
Shahid yana ganinta ya lumshe idonsa, shikam yagamu data kansa, matar datake bin namiji har gida Wai ita ake kira ya aura