BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

Nan da nan Dakin yayi hankali, kitchen taje ta gyara ko’ina, sannan tadawo falo nanma ta gyara, Gaba daya gidan qamshi ne ke tashi, daban daban

Saida tagama gyara ko’ina sannan tashiga kitchen tahada kunun Aya dayaji kayan qamshi, tadauko kwakwa da madara tahada Lemon kwakwa, tayi shinkafa fara dataji Karas aciki, sai kuma miyar ja da naman kaji

Takai komai dining ta jerasu, sannan tashiga dakinta tayi wanka, tana futowa daga wanka Ana Kiran sallar magrib, tayi sallah, sannan taje gaban madubi tafara tsarawa kanta kwalliya

Gashin kanta ta taje tayi fakin, ta Bude kayan data gama shirya wa dazu, wanda maisah ta ware mata, ta janyo wata Riga da wando tasaka, ta kalli kanta a madubi, tace Ina Bata yiba, tacire ta, tadauko wata Riga ja, iyakarta gwiwa, taduba takalmanta ta dauko wani baqi me shegen tsini tasaka, ta bude jikinta da humra
Sannan tafuto falon ta zauna tana kallo
Aranta tace yanzu duk wannan shirin idan bai zoba Yaya zanyi?
Yatashi a banza kenan fa ko?
Wayarta ta duba gaba daya batada number sa, afili tace kinyi sakaci kinyi sakaci Amal, ya Allah Kasa yadawo gida yau
Har wajan karfe tara shiru Bai zoba
Nanfa hankalin ta yafara tashi, ta tashi tsaye tana zagaye cikin falon da Wayarta ahannunta

Tara da kwata nayi, taji alamun shigowa gidan, saurarawa tayi, saikuma taji alamun rufe gate
Ta window ta leqa, ta ganshi tare da wasu mutane, da alama magana suke, saida suka gama tattaunawa sannan taga dayan yabude musu gate din sun fice, shikuma ya juyo yanufo cikin gidan da yar qaramar jaka ahannunsa

Gabanta ne yake faduwa, me zatayi yanzu? Karfa yamata kwarjini, cikin ranta tace Amal daure daure Amal kada komai ya lalace
Matsawa tayi Dasauri tabar wajan, Takoma tsakiyar falon tana zagayawa alamun tanada damuwa

Yana turo kansa cikin falon wani irin qamshi yadaki hancinsa, baisan lokacin daya lumshe idonsa ba

Tana dago kanta ta ganshi tasaki murmushi tatafi Dagudu ta rungume shi, tana cewa Yaya daddy oyoyo, nayi missing dinka
Tana riqe dashi tadago kanta ta kalleshi tace tsoro nakeji ni kadai tun jiya bangankaba, inata jiranka

Kasa magana yayi, Gaba daya ta cika shi da mamaki, saide wata irin nannauyar Ajiyar zuciya dayake saukewa

Itama Sarai taga yanayin daya shiga, Dan haka takama hannun sa ta riqe tace muje kayi wanka Kaci abinci

Kamar dolo haka yake binta, saida takai shi har dakinsa, sannan ta karbi jakar hannun sa ta ajiye

Babbar rigar sa takama zata fara cirewa tace masa, daga hannun mana Yaya daddy

Shide kawai binta yake da kallo, me yarinyar nan take shirya wa?

Tana cire masa rigar ta nuna masa toilet tace to bissmillah ko
Tajuya tafi ce daga Dakin
Bayanta yabi da kallo yanda hips dinta yake juyawa acikin rigar
Tana rufe masa kofar ta jingina da Jikin kofar Gabanta yana faduwa, Amal Ina kika samo wannan qwarin gwiwa? Saida tatabbtar yashiga wanka sannan Takoma Dakin, Akan gadon taga ya zubar da kayan daya cire, tayi sauri ta dauka ta ajiye shi, sannan taduba cikin kayansa zata dauko masa wani kayan, taga kaya birjik aciki, wani wajan iya manyan kaya ne kawai, wani wajan suit wani wajan kuma qanana, rasa wanda zata dauka tayi aciki, sai ruwan ido take, idan tadau wannan saita maida ta dauko masa wani, daga karshe de ta dauko masa wando three quarter kalar Ja, sai rigar ta dauko masa baqa, ta ajiye Akan, jakar daya shigo da ita dauke zata saka masa Akan bedside drawer, Garin dauka mirfin jakar ya bude, daloli tagani aciki masu yawa, ta jinjina Kai, ita tunda take Bata taba ganin kudi hakaba, mayarwa tayi ta rufe, ta ajiye jakar sannan tafi ce zuwa falo
Saida yabata lokaci yana wanka sannan yafuto, da kayan data ajiye masa yayi tozali, baisan lokacin dayasa murmushi ba, wannan yarinyar? Hmm

Kayan yadauka yasaka sannan yafara feshe jikinsa ta turare, turo Dakin Amal tayi tadawo, tana addu’ah aranta Allah yasa de yasaka kayan, aikuwa saitaga yasaka din
Jingina tayi da kofar Dakin ta zuba masa ido tana murmushi
Sannan tace Amma Yaya daddy wannan kayan sunyi ma kyau sosai
Tatako ahankali zuwa gabansa takamo hannun sa, hannun yabi da kallo yakasa magana, tace muje nabaka abinci, hannun su sarqe da juna suka sauka qasa sunyi kyau kamar kasacesu ka gudu
Har dining din takaishi, memakon ta zauna akujerar datake fuskantarsa, a a saita zauna akujerar gefensa, harda qara matso da kujerar, tafara zuba masa abincin, sai Kallanta yake yanda take komai nata cikin nutsuwa, gabansa ta ajiye abincin, sannan ta tsiyaya masa kunun a yar, tazuba masa ido tana kallansa

Abincin yafara ci cikin nutsuwa, yana ci acikin ransa yana masha Allah

Yanaci dazaran yadago kansa saisu hada ido itadashi, kamar wasa taji yace “meyasa bazakici abincin ba?”
Tace no banjin yunwa yanzu saide zuwa jimawa
Bakinta yake kalla yanda take motsa shi, Dan qanqani dashi
Dayawa yaci abincin, yature sauran, dasaurin ta ta janyo flate din tace haba Yaya daddy dubafa saura Dan kadan ka cinye, please daure ka qarasa kaji?
Tafadi hakan da sigar rarrashi
Jiya yi wani Abu ya tsirgo masa tun daga kansa har zuwa tafin kafarsa
Babu musu yadauki spoon din zai qarasa abincin, tayi sauri ta dora Hannunta Akan nasa tace barshi nabaka,
Debo abincin tayi ta nufi bakinsa dashi , tanaji jikinta yana taba nasa, saida ta qara matso wa jikinsa da niyya take goga masa nashanunta ajikinsa
Ahankali yabude bakinsa tazuba masa abincin, tana cewa yauuuwa, Bakinta dab danashi kamar zatai kissing dinsa
Haka ta dinga bashi yana ci, harya qare, sannan yadauki kunun ayar ya shanye duka na cup din data zuba masa, ya kalleta da wani irin yanayi atare dashi muryar ashaqe yace to naqoshi

Cikin shagwaba tace Kai Yaya Dan Allah, ba kasha wannan dinbafa, ta nuna masa Lemon kwakwar, yace “Aina koshi”

Tace a a gaskya, tsaya kaji, sau daya kawai zakasha, ta tsiyayo Lemon kwakwar takai masa bakinsa
Kadan yadansha, ta kalleshi tace Yaya daddy da dadi ko?

Jijjiga kansa yayi, alamun eh
Aikuwa tabashi yakafa Kai saida ya shanye tass
Sannan yace naqoshi

Kallanta yayi yace kamar naji Ana buga gate Dan leqa ta window
Zuciyar ta daya tatafi wajan windon

Batasan wayo yayi Mataba
Yana ganin tashinta ya kalli wandon jikinsa, kamar zaiyi kuka yace nashiga uku, meyake shirin faruwa da nine?

Aguje yatashi yayi sama, yana tsoron karta juyo taga halin dayake ciki, yana zuwa Dakin yashige toilet

Amal kuwa tana waigowa zata fada masa babu kowa, taga bayanan, da mamaki tabishi Dakin sa, tana shiga Dakin taji Motsin ruwa a toilet

Bakinta ta rufe da hannunta saboda Kar dariyar datake ta futo fili, tace waya fada Maka barno gabas take, tajuya takai kwanukan abincin kitchen ta wuce daki ta shirya ta kwanta bacci

  ***      ***      ***

Washe gari tunda tayi sallar asuba Bata koma bacci ba, Bayan tayi karatun alqur’ani da kazimi Tafita ta gyara gidan, gida yadau qamshi kamar ba gobe, kitchen ta nufa tahada musu breakfast, madara ta dama tayi musu kunun madara da kwakwa, sai fruit salad, da wainar semolina
Daki tashiga tayi wanka, tasaka Riga da sket qanana, sket din iyakarsa gwiwa, sai rigar yar qarama daga sama kana iya hango kirjinta, daga qasa kuma bata gama rufe mata cibiyarta ba, Ana ganin shafaffan cikinta
Gashin kanta tasaki ko daure shi batayiba taje falo tana jiran futowar daddy
Shiru shiru har goma ta wuce bai futo ba, Dan haka ta tashi taje Dakin, ganinsa tayi yana kwance yana bacci, tsayawa tayi tana kallan tsantsar kyau irin na daddy, cikin ranta tace ya Allah Kasa mutumin nan ya Soni kamar ba gobe

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47Next page

Leave a Reply

Back to top button