BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

Idanunsa ya zuba mata, yana takowa ahankali har zuwa kusa da ita

Qamshin turaren dataji akusa da itane yasa Tajuyo Dasauri

Mamakin ta ne yakasa boyuwa
Cikin wata irin murna taqarasa wajansa ta sauri, tuni ya rungume ta bakinsa yaqi rufuwa kamar gonar auduga

Yaya daddy!!!
Dama Kaine? Wayyo I miss you wallahi, takai wa bakinsa wani irin kiss me tsayawa arai

Fuskarta yakama da hannayensa guda biyu, yace baby nah
Dafatan de Kuna lafiya keda babynmu? Dukan wasa takaiwa Kirjinsa tace shine kaqi dawowa har munyi wata uku Bama tare

Yace Tuba nake baby nah, kema kinsan dole ce Tasa hakan, idan a kaga wannan Watan nafita, wani Watan ma haka, wasu bazasu duba abinda yake kawo ni ba zasu fara yimana mummunan zato

Yanzu ba gashi nazo ba, cikin shagwaba tace Allah yaya daddy bazaka tafi kasake bari naba
Bazan juri rashin ganinka ba

Kallanta yake cike da qauna, ko waye yace Mata Shima zai iya qara sati daya batare da itaba?
Afili yace Mata aike da nigeria saikin haihu yaro yana gudu zamu tafi

Turo baki tayi cike da shagwaba
Sake janyo ta yayi jikinsa yakai hannun sa kan cikinta ya tsugunna dede inda cikin yake yace Yarona, yauga babanka yazo dafatan zaka barshi yagaisa dakai sosai

Cikin daria tajanye jikinta, daga nasa, takama babbar rigar sa tacire masa sannan tajashi ciki tace muje kayi wanka ka shirya

Ledar daya shigo da ita ya nuna mata yace gashi inji momy, kallan Ledar tayi tace to

Saida takaishi har toilet inda daqyar yabarta tafuto sannan ta dauko masa kayan dazaisaka tafuto falon

Ledar ta janyo taduba, magani ne aciki na mata, Murmushi tasaki lokacin data karanta rubutun dake Jikin takardar Ana cewa Asha da nono Koda madara

Afili tace momy kenan, wato yanzu anbamu dama muyi komai kenan,tunda gashi harda gudunmawa, Amma da antashi anraba mutum da mijinsa

Takardar ta yage daga jiki saboda kada daddy yagani, taje kitchen tasaka acikin dozbin sannan tadebo madara dayawa a cup

Ta ajiye, sannan taje Dakinta takawowa daddy abinci, aqasa ta ajiye sannan ta Bude maganin tazuba acikin madarar tafara Sha

Aranta tana cewa gara tasha Dan tasan wannan mutumin yanda yayi hakurin nan na Tsawon lokaci yau bazasu wanye lafiya ba

Tana cikin Shane yafuto Shima cikin qananun kayan shan iska, abincin ya zuba da kansa yana cewa ai gara dakika kawo abincin nan Dan banci abincin kirki ba nataho Ina murna zanzo naganki

Kafin tayi magana yakarbi kofin Hannunta yace muga me kike Shane haka?
Kokarin karba take, Amma yarigata karbewa yadebo yakai bakinsa yasha

Miqo mata yayi yace ungo babu ma dadi, Hararar wasa tayi masa tace to maganin mutuwa ne

Daria yasa yace shikkenan kinga saimu mutu tare

Abincin tadiba tabashi aspoon sannan ya karba yafara ci

Yana gamawa yajata kan kujera suka kwanta, rigar jikinta ya yaye yana shafa cikin yace baby wannan yarinyar tahana na rungume ki yanda ya kamata
Gashi cikin Naga yayi girma sosai, ko yan biyu zaki Haifa?
Amal zuciyar ta daya tace bawani yan biyu, ai kasan inacin abinci dayawa inajin shiyasa yakesa Yaron ciki yazama qato

Shima abinka da besan komai Akan wani masu ciki ba, bai taba ganiba, sai Akan salma, Dan haka yace eh kuma gaskya kina cin abinci sosai, inajin shiyasa Yaron yake da girma, Amma kinga salma lokacin dazata haihu ma cikin bekai hakaba, inaga Dan Bata kaiki cin abincin bane

Cikin kwanciyar hankali Amal tace emana, Allah yaji qanta, yace amin baby

Gashin kanta yafara shafawa yace inyi miki kitso? Tace kaidin ne ka iya kitso? Yace bazai nakoya Akan matata ba
Yacire ribbon din kanta yana shafa gashin nata sunata firar su cikin farin ciki

Amal tace Yaya daddy namanta ban fada maba, dazu Yaya Shahid yakirani yace wai anty shahida nada ciki har watansa biyu

Cikin fari ciki yace alhmdlh, Amma nayi musu murna, Allah yasaukeki lafiya, tace amin, kuma maisah ma haka

Cikinta yashafa yace a a masha Allah kice Yaron da zamu Haifa zaiga qanne dayawa

Daria Tasa tace emana

Suna manne da juna babu abinda yake rabasu Sai sallah, suna idar wa zasu koma suci gaba da firar su

Suna idar da sallar isha’i, ya zauna tana zaune Akan cinyarsa suna fira suna kallo, wayarsa yadauka yakira su Abba dasu Shahid suka gaggaisa sannan yabawa Amal wayar suna gaisawa yazubawa Kirjinta ido

Yawani qara cika sosai, ahankali yakai kansa wajan yana kissing tareda lasar su

Cikin sauri ta yiwa su Shahid sallama ta kashe wayar

Dubansa tayi tace Yaya daddy waya nakefa, shiru yayi Mata yana ci gaba da abinda yake

Kansa tafara dagowa daga jikinta Amma yaqi Bata damar hakan

Daga qarshe itama tayi shiru tana karbar saqon, Idanunsa dasukai ja yadago yana dubanta dashi yace muje daki?

Kanta ta daga masa, Dan Bata iya bashi amsaba, daukan ta yayi cimak Sai cikin dakinsu, inda yahade bakinsu waje daya yashiga nuna mata yanda yayi missing dinta, sosai tabashi hadin Kai, Awannan dare haka suka kwana cikin farin ciki da annushuwa

Tunda yazo kuma kula da ita da duk wani Abu datake so yadawo hannunsa, sosai yake Bata kulawar data dace, yana Mutuwar tausaya mata yanda yaga tana riqiniya da wannan cikin, kuma Koda wasa Bata hanashi haqqinsa idan ya nema, saide shida kansa ne zai nuna mata bayaso, wani lokacin kuma tayi masa yan dabarunsu na mata

Hatta matsa mata kafafu baya bari doctor suyi Mata da kansa yake zama tana zaune Akan kujera shikuma yana qasa yanayi mata, aikin doctors kawai suyi Mata awo dakuma duba lafiyar ta da sauran su

Yawo kuwa haka zai jata suje wajajan dasuke kusa, hakan baifi motsa jiki ne agareta ba

Watansu daya a Malaysia suna shan soyaiyar su, sannan sukayi shirin dawowa nigeria

Ganin yanda cikinta yakeda mutuqar girma ne yasa sukabi jirgin yamma, suka iso cikin dare

Amma duk da hakanma jama’ar de suna nan danqam, haka suka tafi government house shida tawagarsa, inda babu Bata lokaci kafafen Yada labarai suka fara watsawa duniya cewa maigirma govnor yayi saukar sirri daga Malaysia zuwa nigeria shida mai dakinsa

   ***      ***     ***

After 3 month’s

Babu abinda ya sauya daga kulawar da Amal take samu daga wajan daddy
Yanzu abinma yafi nada, kulawa take samu sosai baga Abba ba, baga momy ba, bare kuma shi kansa uwa uba

Cikinta ya tsufa sosai haihuwa yau ko gobe suna nan sun tanadi komai saide fatan Allah yaraba lafiya
Yayinda cikin shahida yacika wata shida, na maisah kuma biyar

(Facebook fan’s, kuyi hakuri jiya ban samu damar yimuku posting ba, nasan kun jira kinji shiru, na danyi busy ne, dafatan zakumin uzuri ???????????????? Ina yinku sosai kamar yanda shahida takeyin Shahid ????????????)

Mrs Usman ce ✍????????BURINAH ????

(A Romantic love story)

Writing by Amnah El yaqoub

Bismillahir-rahmanirraheem

Dedicated to readers of this book BURINAH

Last page

31

Zaune suke a main falo itada momy, labarai suke kalla, Amal na kallo Tana shan just
Abba ne yashigo da sallama cikin murmushi momy tace alhaji sannu da zuwa
Amal tafara kokarin tashi ta nayi masa sannu da zuwa
Abba cikin tausaya wa yace a a Ina zakije ne Amal?
Tace Abba Lemon nan nakesan qarowa

A a kuma banda abinki menene amfanin ma’aikata, momy tace bari nadauko miki yata, nafada miki kidena kokarin tashi, kede kawai kiyi Zaman ki, kifadi abinda kike buqata
Cikin kunya Amal tace to ai momy zan iya daukowa, ki barshi
Momy tace a a yi Zaman ki

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47Next page

Leave a Reply

Back to top button