BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

BURINA COMPLETE HAUSA NOVEL

Kallansa take da tsananin mamaki, wannan wanne irin so yakewa wannan cikin?

Batace masa komai ba Takama hannun sa tana janshi, tace bazan ci komai ba, saina tabbatar kaima ka gama komai, saimuci abincin mu kwanta, Naga kagaji sosai

Binta yake da kallan luv, ashe Shima an damu dashi haka

Babu musu yatashi sukaje ciki yayi wanka, itace ta taimaka masa yashirya, sai shagwaba yake zuba mata
Falon suka dawo, suka fara cin abinci, shida kansa yadinga Bata harta qoshi
Sannan Shima yaci nasa

Dakanta ta tashi taje ta Bude fridge a kitchen, komai da komai akwai, hatta kayan fruit Ba’a bar komai ba

Ruwa da just tadauko musu tareda cup
Bayan sunsha ne,daddy yatashi da kansa yaje ya maida

Daukarta yayi cak suka koma kan doguwar kujera, tana kwance a Kirjinsa
Cikin rada yace baby kinsan me?
Kanta ta girgiza masa batare datayi maganaba

Yace lokacin da mukaje Germany natuna, kowa baya kula dan’uwansa

Sai yanzu ne Naga babban gangancin dana tafka wajan rashin kula dake

Dagowa tayi da kanta tana kallansa ta rufe masa baki da Hannunta

Cikin daria tace Dan Allah kabari
Karkasa natuno halinka nada daria tayimin yawa

Kallanta yake yana zuba mata murmushi yace menene halin nawa nada?

Kwaikwayon maganar sa tayi tace “idan kin gama zamu fita”

Sannan tasake cewa “karki batamin lokaci minti goma nabaki”

Daddy baisan lokacin da yasa daria ba

Yace kai baby banda sharri fa

Hararar wasa ta sakar masa tace bawani sharri

Haka sukai ta tuno abubuwan dasuka faru dasu abaya suna daria

Daga qarshe suka kira yan nigeria kowa da kowa suka gaisa sannan sukayi cikin daki suka kwanta

  ***      ***      ***

Amma gaskya Shahid babu abinda zance dakai saide nace Allah ubangiji yayi muku albarka gaba dayanku

Shahid yace amin baba

Qwallah ce ta cika idon baba hamani afili yace Allah yaji qanka ibrahima, Allah yamaka rahma

Shahid yace baba kayi shiru haka mana, umma dake gefe tace a a Shahid wannan abun farin ciki ai yafi karfin ayi shiru

Wayarta ta dauka ta kira layin dasu Amal suka kirasu dashi, tana shiga wayar na hannun daddy
Shine yafara dagawa saida suka gaisa sannan yabawa Amal wayar
Suna gaisuwa umma tace Amal din baba, yayanki fa yabiya mana umara nida shi da babanku dakuma shahida, ankusa gama komai cikin wani satin zamu tafi

Cikin farin ciki Amal tace wayyo Allah umma tah
Umma Dan Allah idan kunje nide haqorin makka nakeso, da turaren wuta irin na larabawa mai qamshi, da abaya

Umma ce ta dakatar da ita tace to shashasha, kede kullum bazaki girma ba, memakon kice abaki Shahid din ki sake yimasa godia kokuma abaki babanku kiyi masa murna a a Sai kika hau lissafi

Cikin shagwaba tace Kai umma to Naga Yaya Shahid din yayanane

Umma tace keni Sai anjima

Wayar umma ta kashe tabar Amal da waya a kunne

Daddy dayakejin duk abinda suke fada, baisan lokacin da yasa daria ba yace me haqorin makkah, a a kaga hajiya Amal

Fillon dake gefenta ta dauka tafara jifansa dashi

Yana kaucewa, haka sukai tayi dashi suna zagaye cikin falon

  ***      ***     ***

Atamfa ce ajikinta light blue Sai adon pink da baqi ajikin atamfar
Sosai dinkin ya karbi jikinta
Farar fatar ta tafuto Shar aciki

Fuskarta tasha makeup, tasaka pink din Jan baki a yan qananan lips dinta

Daurin datayi akanta ne yabawa gashin kanta damar zubowa agadon Bayanta

Yana tsaye cikin ash din suit, tana daura masa agogo qirar Gucci
Fuskarta babu alamar farin ciki
Takalmin sa ta dauko qirar Italy ta tsugunna Takama kafarsa ta Zura masa takalmin

Temako daya yayi Mata shine daga mata kafarsa

Sumar kansa ta taje masa, sai sheqi take, sannan tashiga fesa masa turare

Tana gamawa ta ajiye turaren tayi hanyar falo idanun ta nazubar da hawayen data Kasa riqewa
Cikin sauri ya fuzgota jikinsa
Babu Bata lokaci ya rungume ta tsam ajikinsa
Hawaye ne suka sakko asaman kyakkyawar fuskar sa, yayi sauri ya goge karta gani yasake kashe mata jiki

Kuka take sosai, harda sheshsheka, cikin sanyin murya yace kiyi hakuri baby
Insha Allah bazan wuce wata daya ba zanzo naganki tareda babynmu kinji?

Kuka take tasake qanqameshi, Shima kansa kuka zuci yake, Yama rasa wacce kalmar zaiyi amfani da ita wajan rarrashin ta

Kamota yayi suka futo falon, yace Dan Allah baby kiyimin alqawarin zaki kulamin da kanki da baby na, kidinga cin abinci sosai, karkibar babynmu da yunwa

Duk abinda kike buqata kifadawa doctor’s dinnan zasuyi miki, akwai me aiki dazata fara zuwa anjima
Ban yarda ki dauke ko tsinke ba
Duk abinda baiyi miki ba

Kawai kisanar Dani tawaya

Yana fadar haka wani irin kuka yazo masa kusa, wani qullulun baqin ciki ya tokare masa wuya

Cikin sauri yajuya yabar falon yana goge hawayen idonsa yafita harabar gidan yashiga Mota suka wuce airport

Kan kujera tafada tasaki wani irin kuka mai ciwo, sai yau taji ta tsani mulki a rayuwar ta

Gashi asadinsa anrabata da daddynta

Kuka take sosai, cikin sauri daya daga cikin doctor me kula da ita tafuto daga Dakin dayake kusa dana Amal ta janyo ta jikinta tana aikin rarrashin ta, cikin harshan turanci

  ***      ****       ***

Tunda daddy yatafi tazama wata irin shiru shiru, Bata magana sosai, kullum cikin tunanin sa take, abinda yake hanata shiga damuwa daya ne yanda zai Bata tsawon lokaci yakirata awaya suyi ta waya yana sakata daria

Saikuma video call a computer daya zama qa’ida kowanne dare, harta saba kullum yakira waya saita dage rigar ta ta nuna masa cikin yagani, banda ruwan pictures datakeyi tana tura masa

Gaba daya ta kumbura, cikin jikinta daya cika wata biyar yayi wani irin girma, abin har tsoro yake Bata, saboda ba haka take ganin na sauran mata masu ciki ba
Duk ranar Allah Sai doctor ta matsa mata kafarta saboda yanda suka kumbura

Haka doctor zata Sata agaba suyi ta zagaye gidan, saita gaji ne sannan zasu dawo ciki

Batta da aiki Sai shan fruit, kullum shine take wuni tanaci, batada damuwar komai banda rashin ganin mijinta

Idan ta zauna afalo anan take wuni, saboda cikin nauyin sa yafi karfin ta, wani lokacin tayi sallah a zaune, wataran kuma idan tanajin dama dama tayi yanda tasaba

Taqara wani irin kyau jikinta yayi bulbul ta murje, Taqara zama yar hutu kamar ka latsa jikinta jini yafuto

A bangaren daddy kuwa yafita zumudin San ganinta, so yake kawai Rana daya yayi Mata zuwan bazata, ayyukan gabansa yake burin yaga yayi sosai, yanda dazaran ya ware wajan babynsa babu me nemansa

Mrs Usman ce ✍????????BURINAH ????

(A Romantic love story)

Writing by Amnah El yaqoub

Bismillahir-rahmanirraheem

Second to the last

30

Fiancee banga perfume din danake using dashi ba Ina kika sakamin shi?

Dawowa tayi kusa dashi tace wallahi yana cikin kayana fiance, qamshin nakeso, shiyasa na sakashi cikin kayana Dan su dinga yin qamshin turaren
cikin rashin damuwa yace ok bari nayi amfani da wannan
Yasa hannu yadauki wani yana fesawa

Haka ya budawa jikinsa turare kamar sabon ango
Cikin dauria ta to she hancinta, tana turashi gaba

Da mamaki ya kalleta yace lafiya?
Cikin to she hanci tace bansan wannan qamshin turaren fice daga Dakin nan

Jikinsa ne yayi sanyi yazuba mata kyawawan idonsa yana Kallanta
Cikin sauri ya matso kusa da ita yace lafiya kike kuwa?
Jin qamshin akusa da ita ne yasa cikin azama ta tureshi tayi cikin toilet da gudu tana kwara Amai

Bin jikinsa yayi da kallo yana janyo rigar jikinsa yana shaqar qamshin turaren
Yarasa me taji dahar zaisa ta yin Amai

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47Next page

Leave a Reply

Back to top button