LIKITAN ZUCHIYAH COMPLETE HAUSA NOVEL

LIKITAN ZUCHIYAH COMPLETE HAUSA NOVEL

Hannunsa cikin nata haka suka shige gaba Yusuf na binsu a baya da murmushi akan fuskarsa dan Sosai suka birgesa. Har jin wani abu yayi aransa yadai yi addu’ar Allah ya kawo mai masoyiyarsa suma suyi rayuwa fiye da yanda ADAMS yake da NUFAISAT????…

Sun gaisar da mummy inda tanuna Farin cikinta sosai da bayyanar ADAMS ɗin..
Haka suka baro gidan zuciyar ADAMS cike da buqatar kasancewa da NUFAISAT.

Da misalin qarfe takwas na dare iyayan nasu suka tattauna kan batun komawar su NUFAISAT d’in.. Bayan sunyi abin daya dace ADAMS yaso aranar akawo maisu. Saidai dole yayi haƙuri ya barma gobe. Aiko da misalin qarfe goma sha biyu TAUDHAT ta koma d’akinta. NUFAISAT ko sanda takai hud’u saboda shirye shiryen da mummy da Zainab suka tsaya yi mata..

Da misalin qarfe tara na dare ne yake tare dasu a falan nasa bayan ya gama gaya musu iya abinda yasani akan dukan da y’an iskan nan suka masa..
Nan yake tsokanarsu wai daga d’akin wayake ne kafin b’acewarsa.
TAUDHAT tayi kicin kicin tace a ɗakinta yake.
NUFAISAT ɗaure fuska tayi dan tasan kwanan shi d’aya a ɗakinta bai cikace mata na biyun ba yayi tafiyar.
Dan haka saita ɗaure fuska batace komai ba.

Ganin hakan saiya kalli TAUDHAT ɗin yace.. “Tunda yanxu sabuwar rayuwa zamu fara. Aisaina fara daga kan uwar gida nasan hakan duk bazai zama da matsala bako.
Kunyarsa ce tasa TAUDHAT ɗin cewa. “La wasafa nakeyi. Dama ban gama shirya maka kaina ba. Dan haka har azuciyata na amince kayi ko kwana nawa ne aɗakin ƙawata..
Kallan qasan ido NUFAISAT tayi mata Jin tana san sashi nishaɗi da makirci irin yace ita ɗin nan me haƙuri. Sai kawai NUFAISAT ɗin tayi saurin cewa.. “Ai kinsan kece ƙarama dan haka naci girma nadai barshi ya fara yin kwana biyun aɗakinki dan nasan wannan ba wani abu bane.. Saidai zarcewane bazan iya jurewa ba. dan nayi missing abubuwa masu mahimmanci agaresa wanda duk baccin duniya idan zanyi idan banji shi ahannun damana yana yimin su ba bana samun wannan nutsuwar da kowace mace take samu idan ta rufe idanta dan san yin baccin…
Harara TAUDHAT ta galla mata batare da ADAMS ya ganta ba. Itako NUFAISAT saita ɗaga mata gira alamar zamu ɗora daga inda muka tsaya…

 "Toh yanxu dai kowaccenku ta barma ƴar uwarta ni ko. Shikenan ni zan yanke hukunci. Zan fara daga kanki NUFAISAT. Idan nayi kwana biyun na koma ga TAUDHAT ɗin..

Dan haka hira ta ƙare zanje na watsa ruwa…
Tashi TAUDHAT tayi cikin jin zafi aranta tace.. “Toh saida safe… Tana barin falan NUFAISAT ta gallama ADAMS hararar wasa tace.. “Ai daka bari ka kwana yau aɗakin TAUDHAT daba abin da zai hanani hukuntaka..
Murmushi ya sakar mata dasan kamota ta zille yace… “Aina gane yau kishi kike ji shiyasa nayi aiki da hankali..
Har takai ƙofa tajuyo da kallanta garesa tace. “Na baka minti biyar kacal kasameni a d’aki dan yau bani ba zuwa ɗakinka…
“Yau ranarki ce sai yanda kikayi dani.. Ya faɗi hakan da tashi ya shige room nasa. Itako murmushi tayi da ficcewa daga falan….

Na gaida y’an hannuna????????????????????????????????????????
[7/20, 10:05 AM] ®????◾◼▪official Auntyn Luv.: ☆´-☆´-
☆“˜•☆•
¸☆“☆ª☆_☾☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ☆´-☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾☆•
{Zoka Gyara Tunanina}
A true life story
April.. 2018

Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh’md Rufa’i Nalele..☆

© REAL HAUSA FULANI WRITER’S FORUM????
☆We the best ☆

https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&tn=H-R

” بسم الله الرحمن الرحيم
realhausafulaniwriters@gmail.com
☆page 22☆

Tana zuwa bed nata wanka tashiga bayan ta fito kayan bacci tasa na d’aukar hankali. Waƴanda suka fidda komai na tsarin halittarta.
Tana gama sawa tafeshe jikinta da turare me sanyin qamshi sannan tatsaya tana tunanin takoma garesa ne kodai takwanta a bed nata tunda ta gayamai bata ba zuwa ɗakin nasa yau.

Shiko ADAMS yana idar da wankansa bayan yasa kayan bacci sallar godiya ga Allah yayi daya dawo dashi cikin tunaninsa wanda ya sani. Sannan ya qara da rokwan Allahn daya bashi damar sanin wata rayuwa yayi tsawan wannan shekarun daya d’auka kuma a ina yayi.

Bayan ya shafa addu’arsa da d’aukinsa yake niyar tashi dan nufar matar tashi wacce take da mallakinsa a wannan dare. Saidai yana juyowa yayi ido huɗu da ita jingine ajikin ƙofarsa da alama ta ɗan jima tana kallansa..
Kallanta yake daga sama har qasa yana me sakar mata murmushi daga bisani ya ware mata hannunsa tazo da gudu tashige jikinsa tana cewa.. “Dana ɗauka zan iya jurewa har sai kazo garenin kamar yanda nace. Saidai ashe nayi qarya in iya dakatar da zumuɗina. Wannan yasa nazo ahankali dan naga me kakeyi wanda yasa ka shanyani da yawa haka..

“Sallar godiya ga Allah na tsaya yi. Sannan tunda kikazo nima bani ba zuwa ɗakin ki.
Murmushi tayi da ɗago da kallanta zuwa garesa tace.. “Yau jinake nafi kowace mace samun farin ciki da jin daɗin rayuwa.
Mijina! Kai haskene agareni. Yanxu na qara tabbatarwa. Saidai ka bini ahankali dan naga har wani zumuɗi kake..????
Ahankali ya hade bakinta da nashi yana bata wani kiss me tafiya da numfashin masoyi..
Bai barta haka ba dan aika mata da wasu sakwannni yake da hannuwansa wanda nan take tafara ɗauke wuta.
Ta lura so yake ya hana qafafuwanta tsayuwa waje ɗaya. Dan haka saita fara kici kicin kwatar kanta cikin mutuwar jiki..

Nan tacikin kunnanta ya fara raɗa mata magana wajen faɗin.. “Bazan iya binki ahankalin ba my luv… Yaudai sai kinyi min haƙuri. Dan bazan iya controlling kaina ba idan har nakai inda kike jin tsoro..
“Wannan salan ya bambanta da sauran salan da kake amfani dasu adai dai wannan lokacin. Wakema hakan. NUFAISAT ta fad’i hakan cikin wani hali..
Bai dena mata abinda yake ba ya bata amsa da cewa. “TAUDHAT dai bata taɓa rikitani na mance kaina wajen bata wani salo wanda banrigada na baki shi ba.
Karki ƙara tuhumata idan kikaga na canja miki dan ako yaushe so nake kwakwalwata tadinga bud’ewa dan na dinga baki salo me tsayawa arai..
“Fatan alkairi gareka masoyin asali. Zanso ka ɗaukeni dan kaga ina neman rasa nutsuwata…
ɗaukarta yayi kamar yanda ta buqata bai direta ako ina ba sai’a kan gadansa.
Sun samawa kansu nutsuwa da kwanciyar Hankalin da suka ɗauki lokaci me tsaho basu samu damar bawa juna ba..

Washe gari daga yanda suke breakfast kaɗai ya isa ya tabbatar maka suna tare da nishaɗi…

Haka dai NUFAISAT badan taso ba tabama TAUDHAT ADAMS ran girkinta.

Amman sanda tamai kuka..
Shiko ya shiga lallashinta yana me cewa tafito mishi da wani saban salo. Amsa dai ɗaya ce tabashi itace. Tayi missing d’in shi da yawa ne shiyasata yin kukan dan taso ace tajishi ko irin na wata biyu ɗinnan ne.. Da tsokana yake bata amsa da. To bara yaje gun TAUDHAT ya roqa musu hakan. Murmushi tayi da cewa. Wasafa take mai..

Eh da gaske daya tare da TAUDHAT yaji dad’inta sosai. Saidaifa NUFAISAT daban take agunsa…

Kwana biyar da dawowarsa Amminsa ta had’amai walima ta nuna Farin cikinta na bayyanarsa. Y’an uwa da abokan arziqi ba wanda bai halarci wannan walima ba. Koya yaji dad’in tawowarsa sosai da sosai.

A kwana na bakwai ne shida Yusuf sukaje can inda ake tsaran Ibrahim suka gano yana cikin mawuyacin hali…
Yana ganin Adams ya durqusa da kama qafarsa yana rokwansa kan yayafe masa yayi nadamar abinda ya aikata masa arayuwa Wallahi yayi nadama…
Kallansa ADAMS yayi da girgiza kai yace mai. “Sam banyi tunanin kaine mutumin da kake neman rayuwata ba. Kaje na yafe maka. Kuma bazan hanaka yin yanda kakeso da rayuwarka ba. Idan ma ka faɗin min hakan ne dan nasa asakeka kayima kanka. Dan ko baka roqeni ba zansa a sakeka. Sannan zan gaya maka har yanxu ina tare da masu tsaro. Dan naso nabarsu mahaifina yace bai aminta ba. Hakan yasa na ragesu.
Yanxu mutum uku ne suke tare dani. Nasan wannan karan bazasu tsorataka ba bare su baka wahala wajen cimma burinka akaina.
ADAMS na gama gayamai hakan ya tashi shida Yusuf suka barshi nan idansa na fidda hawaye.. Dan da gaske yayi nadamar abinda yayi masa. Sharrin shed’an ne kawai banda haka bega abinda Adams yayi masa ba arayuwa daya nufesa da wannan baqin halin. Sai yanxu ya gane d’aukaka ta Allah ce….
Su ADAMS na barin wajen aka ce an sallamesa.
Da mutuwar jiki Ibrahim d’in ya shege motar mahaifin nasa dan ADAMS ne ya kira mahaifin nasa ya gaya masa yazo ya ɗaukesa ko yasa azo a ɗaukesa dan’an sallamesa yau…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62Next page

Leave a Reply

Back to top button