Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Not edited.

Mai gadin ya girgixa kai yace “Toh ku yi hakuri gobe sai ku je ku dawo, amma ku tabbatar kun taho da wayar da xa ku yi communicating da ita” xai rufe gate Yakumbo tayi saurin saka kafarta daya ciki tace “Don girman Allah kayi hakuri ka bar mu mu shiga, wllh mun kashe kudin mota yayi dubu daya, kuma ni na biya, ka ji tausayina d’an nan” kamar xata rushe masa da kuka ta kai karshe, ya tsaya kallonsu da mamaki, can yace “Toh shkkn, amma har ni nasan sai kun janyo min fada wllh, amma bakomai akwai Allah, ku shigo” Yakumbo ta durkusa har kasa tana masa godiya suka shiga cikin makeken compound din gidan, uwa idonta xai fito yyi magana ta dinga bin gidan da kallo da motocin dake parking lot, Abuu ko idan da sabo ta saba shiga gidaje haka kai yara masu aiki, don haka ita ke biye da mai gadin yakumbo kuwa nata kalle kalle, bbu abinda khadijah tayi ma kallo biyu a compound din, don bbu bakonta a ciki. Karkashin wani artificial tree mai gadin ya nuna masu su jira sa, ya isa main entrance din shiga gidan, ya kusa minti biyar tsaye bakin kofar bayan ya danna bell aka bude kofar, Mai aikin gidan ce warce baxata wuce shekara ashirin da bakwai ba tana sanye da apron da hularsa alamar daga kitchen take, ganin warce ta fito yayi murmushi yace “Kyauta mun tashi lafiya?” Tace “Lafiya lau Usman, Ashe kai ne ma, ya aka yi?” Ya d’an sosa kai yace “Hajiya ce tayi bak’i ina fatan dai ta tashi bacci?” Kyauta tayi kasa da murya tace “Gata can parlor xaune ma” Muryar Hajiyar gidan suka ji tace “Waye kyauta?” Kyauta ta yi saurin barin bakin kofar tace “Hajiya, Usman mai gadi ne wai kin yi baki” Hajiyar dake gyara farcenta da nail cutter ta kalli agogo tace “Baki kuma?” Kyauta tace “Eh Hajiya” tace “Toh su shigo, amma ni bani da wasu baki da nake expecting da safen nan, da akwai ai da na gaya masa” Usman da ya ji abinda ta fada ya nufi gun da yakumbo suke yace “Allah ku daina karya bashi da amfani a rayuwa, yanxu gashi tace ita bata da wasu baki da take expecting da safen nan ku kuma har da ce min kun yi waya” yakumbo ta yi kasa da murya tace “Mu dai don Allah tunda har muka samu muka shigo gidan nan ka rufa mana asiri mu karasa idan ma ta kore mu shi kenan sai mu fita haka Allah yayi” ya nuna masu kofar shiga ya koma can bakin gate yana mamakin wasu ‘yan Adam. Da yake a bude kyauta ta bar masu kofar, da sallama Yakumbo ta kutsa kai cikin parlorn tana dudduke kai ga wani daddadan kamshi dake tashi ta ko wani angle… Abuu na biye da ita a baya, Sai da duk suka shiga khadijah ta tura kofar a hankali ta rufe sannan ta bi bayansu, Hajiya Fatima matar gidan ta dinga kallonsu da mamaki har suka xauna kasan lallausan carpet din tsakar makeken parlorn, sanyin Ac yasa yakumbo ta fara rawan Dari, Hajiya tace “Sannun ku da xuwa” Yakumbo tayi saurin cewa “Yauwa ina kwana shugaba?” Ba Hajiyar kadai bace xaune parlorn ita da wata ce wanda ga dukkan alama kanwarta ce tsabar kamanninsu, matar xa kuma ta yi shekaru talatin da ‘yan kai a duniya, Hajiya ta kalli kanwarta kamar yanda ita ma take kallonta, Amsa gaisuwar yakumbo Hajiyar tayi tace “Daga ina?” Yakumbo tayi gyaran murya kafin Abuu tace komai tace “Dama Hajiya da daddewa mun ji kina neman mai taimakon ki, shine ga yarinyata ganin irin haxakarta da hanxari yasa nace in rako Abuu dillaliya mu kawo maki” Hajiyar tace “Ayya ai kam ina da mai aiki bayin Allah gata can ita ta bude kofar ma….” Yakumbo ta katse ta tace “Ayya wannan d’an share share da goge goge xata ke maki Hajiya, wancan naga ai babba ce, ni ko baxa ki biya kudi mai yawa ba ki dauketa Hajiya don wllh daga waje me nisa muke ga uban kudin mota da muka kashe, ki taimaka fisabillilahi Hajiya” Abuu ta kara da cewa “Ki taimaka Hajiya wllh takanas saboda ke muka kawo yarinyar” Hajiya da tayi shiru tana kallonsu tace “Toh wacece mai aikin?” Da sauri Yakumbo ta nuna khadijah dake kallo so engrossed a katon plazma dake parlorn tana murmushi, Yakumbo ko lura da hakan ba ta yi ba, sai kallon Hajiya take ta kara jin abinda xata ce kan khadijah xuciyarta na bugawa, Hajiyar na duban khadijah tace “Ke ya sunan ki?” Inaa khadijah ana can duniyar kallo wannan karan har da dariyarta don film din ya mata dadi, yakumbo ta hadiye abu da kyar ganin irin kallon da Hajiyar ke mata, ta wani mitsileta a boye da sauri khadijah ta dawo, a fusace Abuu tace “Ba ke ake ma magana ba” khadijah ta kalli Hajiyar dake kallonta har lkcn tayi kasa da murya tace “Sorry ma’am, pardon?” Daga Hajiyar har kanwarta dake xaune kusa da ita bude ido suka yi suna kallonta sosai, Khadijah tayi kasa da manyan idanuwanta tace “I am sorry” Mikewa Yakumbo tayi jin fitsari ya taho mata, shi kenan khadijah ta cuce ta sai da ta buga masu turancin, ta nufi kofa da sauri tana cewa “Bari in d’an xaga Hajiya ku yi hakuri” Abuu ma sai kallon khadijah take baki sake jin fa kamar wani yare ta yi maimakon Hausa, Hajiya dake ta kallon khadijah tace “Alright, what’s ur name!” Khadijah ta kalleta tace “My name is khadijah Muhd” Hajiyar tace “From where” khadijah tace “I am from kano, I lost my mum and dad… My step mum brought me to Kaduna 4 days ago and she left me….” Tana magana ne har hawaye ya kawo idonta, Hajiya dake kallonta keenly tace “And… Who is this woman that left to ease her self now?” Khadijah tace “My stepmum told me she is her senior sister..” Shigowar yakumbo yasa khadijah tayi shiru, Yakumbo ta shiga kalle kalle kamar munafuka ta xauna amma kuma ta kasa cewa komai tana jiran jin hukuncin Hajiya, ta ma san kawai Hajiya fasa daukar khadijah xata yi don ita tunda take bata taba jin an dauki mai aiki yar boko ba, sai ayi tunanin wani mission ya kawo ta gidan, Hajiyar na kallon Yakumbo tace “Nawa ne kudin aikin?” Xuciyar Yakumbo yyi mugun sanyi ta gyara zama tace “Wallahi ko nawa Hajiya, ko nawa Allah ya hore maki babu damuwa barin yanxu da kudi yyi wahala” Hajiya tace “Dubu uku xan bayar, yanxu kuma xan ba da na wata uku kamar yanda nake ma duk mai aiki idan na dauka” Yakumbo dake ta godiya kamar marokiya tace “Wallahi ba damuwa Allah ya bi ya maki bukatunki na alkhairi, nagode nagode nagode” Kanwar Hajiya mai sunan Khadijah dake gefenta ce tace “Why House maid again bayan kyauta Mumy? Beside I don’t think this little girl will be capable, you just look at how engross she is with the TV….” Ko kadan khadijah bata ma san abinda ake cewa ba don gaskiya ne gaba daya hankalinta ta mayar kan kallo, yakumbo da babu abinda taji baya ga kyauta a xancen da Anty khadijah tayi ta marairaice tace “Kiyi hakuri baiwar Allah bbu abinda yarinyar nan ba ta iya ba wllh” Hajiya tace “Toh idan naga bbu abun kirki in sha Allah nan da kwana uku xa ku dawo ku dauki yarinyar, idan ya so sai ki mayar min da dubu shidda nah, ki rike dubu uku” Yakumbo tace “In sha Allah Hajiya, nagode nagode nagode” Hajiya ta katse ta daga godiyar da take yi tace “Toh ta wani number xa a same ki?” Yakumbo tace “ni ki ban naki idan na koma gida sai in kira ki Hajiya, na bar wayar a gida kuma ban san number ba” Hajiya ta sa kyauta ta kawo takarda da Biro tana cikin rubuta number aka bude kofar, duk suka juya kallon bakin kofar banda ita dake rubuta number, dogo ne tamkar dai khaleel din wasu can Lol… Irinsa shi ma ake kira da gentlemen, sanye yake da farar T-shirt da bakin wando, shigar ya kara haska farin fatarsa, iyakar kyau dai kam Alhmdllh Allah ya masa, tuni turarensa ya gauraye ko ina na gidan, har ya iso cikin parlorn idanuwansa na kan mahaifiyarsa dake rubuta sunanta kan number da ta rubuta a takardan hannunta, ya xauna gefenta yana murmushi ya mata side hug a hankali yace “Good morning mum” Sai a sannan ta kallesa hade da turasa tace “Morning…tashi kusa da ni sai warin asibiti kake dalla” Xaro ido yayi yana shinshina kayansa yace “Kai mum warin asibiti kuma duk kamshin nan da nake” tace “Ae kamshin daban warin asibitin daban” ya d’an yi murmushi yace “Ba dai warin asibiti ba sai dai kice kamshin magunguna mum…” Ya kalli Small mum dinsa yana shafa kai yace “Good morning small mum” tabe baki tayi tace “Allah ya kara…. ina ce nan ka tsallakeni ka tafi can gashi an gwaleka” rike kansa yyi yana d’an murmushi can ya dago a hankali yace “Mum kin ji koh” Sai a sannan ya kalli su Yakumbo, tayi saurin cewa “Ina kwana Alhaji” yace “Lafiya Alhmdllh” Hajiya da har ta bata paper din tace “Toh shkkn, yanxu saura in baku kudin ina sauraren kiran ku” kallon D’an ta dake xaune har lkcn a gefenta tayi tace “Aliyu akwai cash tare da kai yanxu?” Ya sa hannu aljihun sa, tace “10k xaka ban” dubu goman ya fiddo ya mika mata ta karba ta ba Yakumbo, Hannu bibbiyu ta karba tana jero godiya, Aliyu yyi saurin dauke kai yana kallon small mum dinsa da wani expression yace “Who are they?” Anty khadijah ta tabe baki tace “Wai house help” yace “House help kuma, did mum dismissed the one available?” Anty khadijah tace “Ina fa, duk biyun xata hada ina ga” ya yatsine fuska yace “Which means ta ba ma su Siyama daman su kara relaxing kenan” Anty khadijah ta tabe baki bata ce komai ba, yace “Which among them is the house help” Anty khadijah ta nuna masa khadijah dake rakube gu daya ana ta kallo happily, lekata ya dinga yi baki bude, can ya dago da sauri yace “Which help will this little girl render?” Anty khadijah tace “Kai ma dai ka gani” bai sake cewa komai ba ya fiddo wayarsa dake vibrate a aljihu, Su Yakumbo suka tashi xa su tafi har lkcn tana ma Hajiya godiya ko bin ta kan Khadijah bata yi ba ta fita tana kara dunkule kudin hannunta Abuu na biye da ita, Hajiya ta kalli Khadijah tace “Tashi ki dau cups din nan ga kitchen can ki kai su” ko kadan khadijah bata ji mai Hajiya ke cewa ba, har sai da Anty khadijah ta mata tsawa, ta dawo daga kallon da take a firgice, Hajiya ta nuna mata cups din tace “Ga kitchen a can ki kai su” tashi khadijah tayi tana neman cups din ta gansu can kusa da Anty khadijah, tana kallon Tvn da wayo ta nufi gun cups din, xaro ido Aliyu yyi jin yanda ta take kafarsa ya fixgota a mugun fusace yace “Baki da hankali ne” Hajiya tace “Bata sani ba fa ina ji Aliyu….” Khadijah dake ta kallonsa tayi kasa da kai a hankali tace “I am sorry, I didn’t notice ur leg”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button