Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Daga sama har kasa Aliyu ke kallon Khaleel da ya ki sake sa, Aliyu ya dake yace “Who are you?” khadijah na ganin haka a rikice ta ajiye jakar hannunta tace “Noo plss Dr ka kyale shi…” Khaleel na kallon kwayar idon Aliyu strictly yace “Stay away from her or else you regret it….” Yana fadin haka ya sakesa, Aliyu yyi wani murmushi yace “And who are you to tell me that? Her boyfriend? Husband or??” Juyowa khaleel yyi a mugun fusace ya sake cakumosa Aliyu ma ya cakumesa yana mayar masa da irin kallon da yake masa, khaleel yace “Both! Husband and boyfriend” dariya Aliyu yyi yace “You are very very stupid, idan ma mijinta ne kai ka shirya rabuwa da ita domin kuwa she is not meant for you” Khadijah na ganin abun ya kai haka ta shiga tsakaninsu da sauri cikin kuka tace “Wayyo na shiga uku, don Allah don annabi ku rufa min asiri ku yi hakuri” tayi facing din khaleel dake hade fist dinsa yana ma Aliyu wani irin kallo ta rikesa hawaye na sakko mata tace “Plss am begging you ka kyale sa don Allah Dr” lkci daya khaleel ya sake Aliyu ya kama hannunta ya dau jakarta, Aliyu ya fiddo complimentary card dinsa a aljihu ya saka a na Khaleel yana kallon kwayar idonsa yace “I will be waiting for ur call young man” still khaleel yyi kamar xai cire ya jefar sai kuma ya bari ya juya kamar xai tashi sama ya bar wajen Khadijah ta dinga bin sa xuciyarta na bugawa, Aliyu ya bi su da kallo yana murmushi a hankali yace “I will surely get you soon Iman, not when I have set my eyes on you” ta waigo ta kallesa tayi saurin dauke kai, har suka shiga cab Khadijah waigawa take taga ko ya biyo su, sai dai ta kasa ganewa don mutane ne da yawa ko ganinsa bata sake yi ba, duk ta kasa samun nutsuwa, tana kallon Khaleel da har sannan fuskarsa ke a daure kamar xata yi kuka tace “Plss Dr kar ka sake kulasa” Kallonta khaleel yyi a fusace xuciyarsa na heaving yace “That’s idan bai shiga rayuwar ki ba, Billah xan iya yi masa komai, I don’t care… Ina da wanda ya tsaya min a kasar nan, look… my father….” Sai kuma yyi shiru, lkci daya idanuwansa suka canxa kamanni, Khadijah jikinta yyi sanyi sosai, muryar khaleel ne ya dawo da ita tunanin da ta tafi, cikin sanyayyan muryarsa yace “Don’t forget this is Abuja, ina xa mu? Thinking Kaduna kika ce min Umma take” A hankali tace “Dole sai mun bi train xuwa Kaduna” yace “Why not flight” ta hararesa tace “Bayan mun baro airport din, kawai kaje xaka tara mana crowd a airport ko meye na kulasa” bai ce komai ba sai kallon tagar taxin yake, khadijah ta sanar ma mai taxin train station xai kai su, Tsaki taji khaleel ya ja yace “Seriously It’s being long aka ba ta min rai haka… Da ba don airport bane we ought have teach each other a lesson da guy din nan, I don’t even care about d securities there…” Khadijah dai sai kallonsa take ganin how serious he was, Juyowa yyi ya kalleta tayi saurin dauke kanta, murya can kasa yace “It’s because of you khadijah, don ke na kyalesa da mun yi karamin exercise a wajen nan” ta tabe baki tace “Ni dai babu ruwana” yayi murmushi da ya bayyana dimples dinsa yace “Billah ke kuwa ke da ruwa baby” kallonsa tayi da sauri, ya tsuke fuska kamar ba shi ya fada ba ya fiddo wayarsa yana dannawa, tayi murmushi tana ci gaba da kallon waje, suna isa station suka samu jirgin kasa mai xuwa Kaduna, Khaleel ya yankar masu ticket, sai da jirgin ya tashi khadijah ta kallesa tace “Are you a Nigerian” kallonta yyi, ta sauke idonta, yyi murmushi yace “Sure, A Nigerian… From Kaduna also, why do you ask, ko ban yi kama da ku ba ne” bata ce komai ba, shima bai ce komai ba, bayan few hours suka isa station din train dake kaduna, Napep suka dauka da xai kai su har gida, Yace “Do I have to accompany you har kofar gida” Khadijah ta kallesa sannan ta sa mai Napep ya tsaya tace “Sauka toh ka hau wani adai daitan ka tafi gidan ku” wara ido yyi yace “Like serious??” Ta langwabar da kai tace “Sure” murmushi yyi ya sauka yace “Ohk then” tace “Yeah, thanks” daga haka ta sa mai Napep din ya wuce khaleel ya bi su da kallo. Khadijah na isa gida ta sauka ta bude Jakarta, tunawa tayi ba kudi wajenta ta basa hakuri tace bari ta amso a ciki sannan ta shiga gida, sudais da shureim ne parlor suna kallon cartoon, suna ganinta suka mike a guje suka yi kanta suna mata oyoyo ta rungumesu gaba daya cike da murnan ganin yan biyunta, Umma dake kitchen ta fito da mamaki tana kallonta, da kyar ta yakice yaran a jikinta ta nufi Umma ta rungumeta tace “Ummata na dawo” Umma na kallonta tace “What happened Khadijah??” Ta marairaice tace “Umma ina missing din ku ne na taho fa” Umma ta hade rai tace “Kina da hankali kuwa, kamar warce xata taho daga kano, yaushe kika koma da har xaki taho yanxu” shiru ta yi bata ce komai ba, Umma ta saki baki tana kallonta a mamaki, juyawa khadijah tayi ta nufi jakar Umma dake ajiye parlorn ta bude ta fiddo kudi tace “Umma bari in kai ma mai adai daita” daga haka ta fita ta kai ma sa kudin sa twins dinta na rike da ita, suna dawowa parlor duk suka haye kanta Shureim yace “Anty ina wannan uncle din nan dake UK, did he tell you to greet us?” Khadijah tayi murmushi tace “Sure sweetheart” Sudais yace “Anty is he also from Nigeria, I like him” Umma dake kallonsu tace “Wani uncle suke fadi?” Khadijah ta saci kallonta tace “Neighbor dina ne fa Umma” Umma tace “Ba mace bace kwanaki da muka je?” Khadijah tace “Ayya, Nancy ai ta tashi” Shiru Umma tayi kafin tace “Toh dai a kula, Allah ya ci gaba da tsare ku” A hankali khadijah tace “Ameen” Umma tace “Toh don me wai baxa ku xauna tare da Vanessa ba?” Khadijah tace “Umma am nt comfortable a gidanta ne” Umma tace “You have no choice, bana son xaman ki gida daya da namiji” da sauri khadijah ta kalleta, murmushi tayi tace “Umma he is a Nigerian, kuma I think bahaushe” Umma tace “So?” Shiru Khadijah tayi, Dai dai nan wayar dake jakarta ya fara ring ta bude jaka da sauri ta fiddo tunawa da tayi wayar khaleel ne, shiru ta yi tana kallon number kafin ta daga, muryarsa taji yace “Are you home?” Ta saci kallon Umma Kafin ta mike tace “Uhn” daga haka ta wuce daki yaranta suka bi bayanta Umma ta bi su da kallo.

Flight Aliyu ya bi ya taho kaduna, Ji yayi gaba daya ba wani sauran damuwa a tare da shi, lkci lkci sai yyi murmushi, har ya isa gida a taxi tunanin Khadijah yake, he is just happy seeing her today, bayan ya sauka taxi mamakin me ake yi a gidan ya dinga yi ganin mutane da manyan motoci har su Usman da Sanusi shadda ce sabuwa jikinsu, suna ganinsa suka washe baki suna masa sannu da dawowa, ya amsa gaisuwarsu ya entrance din gidan, ganin takalma da yawa alamar mutane ne sosai parlorn ya xaga ta baya, iklima ce bakin tap a durkushe tana kwarara amai, ya karasa yana kallonta ganin uban kunshin da aka mata ga kitso an yaryara mata a kai, yace “Baki da lafiya ne?” Jin muryarsa ta dago da sauri, lkci daya ta mayar da kanta ta sunkuyar, tana maida numfashi da kyar tace “Sannu da dawowa yaya Aliyu” bai damu da ya amsa ba yace “Me ake yi a gidan nan?” Shiru tayi da farko kafin tace “Aurenmu” Few seconds yyi amfani da wajen apprehending abinda ta fada, cike da confusion yace “Aurenmu? Aurenmu da wa?” Still bata kallesa ba tace “Ni da kai” bude baki yyi yana kallonta dai dai fitowar Anty khadijah tayi wani shegen haske ta xama katuwar gaske, tana ganinsa ta saki guda tace “Saukar yaushe ango?” Aliyu na xaro ido yace “Anty ban gane ba, ango kuma?” Anty khadijah na taunar cingam da ya cika waje da kara tace “Tafi Anty fati na daki xata maka bayani yanda xaka gane my son” daga haka ta nufi ‘yar ta tace “Ki taso mu je, mai make up din ta gaji da jira” janta tayi suka Wuce ciki suka bar Aliyu tsaye baki bude, har lkcn shi dai bai fahimci komai ba. Wucewa ciki yyi direct ya tafi sama Dakin Mumy ba tare da ya kula da mutanen dake parlor ba, ita da frnds dinta sai mahaifiyar Abbansa da suke kira da yaya ne xaune dakin, yyi hankalin gaishesu kafin yace “Mumy I don’t get what’s happening in this house” Yaya tace “Bikin ku ake yi da ‘yar uwar ka” Aliyu ya yo waje da ido yace “Wace yar uwar tawa?” Yaya tace “Iklima, Allah bai yi da Hanan ba” Wani kallo Aliyu ya dinga yi mata kafin yace “Allah ya kiyaye, wace iklimar? Iklima da ta gagari kowa gidan nan xa a makala min, No Mumy I have never failed you but… No mum me yasa xaki min xabin da xai cutar da ni, mumy kema kinsan iklima ta fi karfina, Mumy ki rufa min asiri…” Tsawa Mumy tayi masa ta mike tana masa wani mugun kallo tace “Get out Abuturrab, idan an kai ma iklima gidan ka kayi gunduwa gunduwa da namanta ko kuma ka koro mana ita, fita nace” Juyawa Aliyu yyi ya fice daga dakin, Yaya tace “Fatima, da gaske yarinyar ta gagari kowa? Ni dai an san ba saninta nayi ba, kar ku cutar min jika” Mumy ta hade rai tace “Yaya yar yar uwata ce uwa daya uba daya fa” tana fadin haka ta fita dakin, kawayenta suka bi ta da kallo.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button