Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Anty khadijah na kallon Aliyu da kyau tace “Ko baxa kayi bayanin ba in taya ka ne dakta?” Bude ido Aliyu yyi da kyar yana kallonta, lkci daya idanuwan Mumy suka kawo ruwa kana ganinta kasan ba karamin shock ta shiga ba, Aliyu ya isa gabanta ya duka kan gwiwowinsa cikin sanyin murya yace “Mumy…” Dakatar da shi tayi hawayen idonta na sakkowa tace “Irin tarbiyar da nayi maka kenan Aliyu…. Yanxu yar mutanen kayi ma haka?” Ya rufe fuskarsa jikin kafarta cikin rawar murya yace “That’s the greatest mistake of my life mum, shine abinda na kasa gaya maki shekaru shiddah kenan, mumy ba halina bane kema kin sani, ban san ya aka yi ba ranan, it look as if I was possessed, I ruin the little girl… Mumy I….” Kasa ci gaba yyi hawaye na sakko masa, Anty khadijah ta tabe baki tace “Lallai Abuturrab baka jin kunyar karya? abu ya faru ba sau daya ba ba sau biyu ba ka kirasa mistake? Tunda abun ba arxiki har ya kai ga ka fara yi ma ‘ya ta sharri to wllh nima baxan duba abinda ke tsakanina da mahaifiyar ka ba, gwara in tona maka asiri, idan ni baka ji kunyar toxarta ni da iklima ba to nima baxan ji kunyar ramawa ba a matsayin ka na d’an yayata” daga haka ta bar wajen ta shige daki… Aliyu ya bi ta da kallo, duk abun nan da take fada fa ba ji yake ba mamakinsa shine ya aka yi tasan abinda ya faru tsakaninsa da Khadijah bayan bata gida ranan, how is that? Fitowa Anty khadijah tayi daga dakin rike da iklima da ta sa ma Hijab suka sauka downstairs kamar xata tashi sama tana matsar kwalla tace “Da raina kayi ma yar cikina irin wnn sharrin koh Aliyu, duk matsayina gun uwarka baka gani ba saboda na rufa maka asiri da yawace yawacen da kake nace a aura maka ‘ya ta shine xaka mana wannan cin mutuncin ka saka min da sharri” gidan ta bari gaba daya tare da yar ta, Mumy ta juya ta koma dakinta a sanyaye, Aliyu ya kasa daga kai ya kalli kanninsa da sauran relatives dake wajen. Anty khadijah na fita da kafa suka karasa bakin titi da iklima, hankali tashe take tambayarta yaushe rabon da ta ga al’adarta, iklima ta turo baki tace “Oho nima ban sani ba” dundu ta kai mata tace “Kaji min shegiya wai baki sani ba, ni nake maki al’adar? To wllh sai dai ki daura ma ubanki hawan jini ba ni ba, mu je asibitin ai xa su mana bayani a can, in ma ya kama in kashe ni Wllh sai in kashe Ki a can din, tunda duk abinda nake maki bakya gani ni xaki ja ma abun kunya ni xaki kunyata a idon duniya” Ganin sun shiga Napep yasa Anty Khadijah tayi shiru sai girgixa kafa take tana Allah Allah ta ganta a asibiti har suka isa asibitin dai, iklima kam ko dar sai ma gyangyadi da take ta yi a napep din, suna shiga asibitin likita ya tabbatar ciki gare iklima, Anty khadijah ta daura hannu a ka tana xaro ido tace “Na shiga uku na lalace ni Khadijah, iklima yanxu ni xa ki ma haka, a ina kika je aka maki ciki, don na sake maki sai ki tona min asiri iklima? Ni xa ki kunyata?” Shi dai likitan kallonsu kawai yake, Anty khadijah ta share xufar dake keto mata ta hadiye yawu da kyar tace “Likita ko nawa kake bukata ka fada xan baka ka raba ta da wannan bala’in dake tare da ita ka rufa mana asiri” likitan yace “A’a ba ma haka a nan Hajiya ku yi hakuri, ku je wani asibitin…” Anty khadijah ta fashe da kuka a karo na farko tace “Haba bawan Allah, kai baka taimako ne, wllh dariya xa a mana ka rufa min asiri ina da makiya da yawa duniyar nan, ka ji tausayina ka taimaka mani” Likitan yace “Wato kin fi so kiji kunyar lahira a kan ta duniya kenan Hajiya?” Da sauri Anty khadijah tace “Eh wllh” sake baki yyi yana kallonta, can ya gyada kai yace “Gaskiya ne, toh Allah ya shirye ku, kuyi hakuri ku fita akwai patients da xan yi attending ma yanxu, mu ba ma aborting ciki a nan” tashi Anty khadijah tayi tana masa matsiyacin kallo tace “Yanda ka ki taimakona kai ma haka yar ka xata jajibo maka abun kunya ka rasa madafa in sha Allah, mara imani kawai…” daga haka ta ja Iklima kamar xata tashi sama suka fita, haka Anty khadijah suka dinga yawo hospitals tana neman inda xa a cire ma iklima ciki har dai ta samu wani da kyar, kudi ba na wasa ba ta bada aka yi aikin, unconsciously ta tafi da iklima gidan wata da suka hadu a kauyen da take yawan xuwa suka kulla abota suke kawance kamar xa su hadiye juna, kwanan matar uku gidansu Aliyu lkcn biki, jiya ta baro gidan bayan an gama komai ba rabon xa ayi komai a gabanta, Hajiya Laure sai kallon iklima dake kwance take da mamaki bayan Anty khadijah ta mata bayanin komai tana matsar kwalla, can Hajiya Laure ta sauke ajiyar xuciya tace “Toh ai baki ga ta kuka ba Hajiya Khadijah neman mafita xa ayi, yanxu dai a takaice bbu auren kenan?” Anty khadijah ta tsayar da kukan da take da sauri tace “Aure kai, aure na nan daram dam ba inda ya je, ai ko hauka nake baxan ce masu cikin ne ba har an cire, nunawa xan yi kawai gidan ki na kawota da xuciya ta debeni” Hajiya Laure tace “Gaskiya ne, toh wai kin ma yi yanda aka ce maki wajen nan da muka je ranan kuwa?” Anty khadijah tace “Ba gashi nan ta sa nayi asara ba yanxu don nasan ba sha xai yi ba, ni wllh da tun kafin bikin nasan da shegen cikin nan da na je an cire, sai ma kin ga ko gama xama halitta cikin bai yi ba, a can wani gutter na jefar kafin mu shigo nan don likitan cewa yyi mu tafi da shi kar mu ja masa matsala” Hajiya Laure tace “Alhmdllh da abun ya xo a haka ba sai da aka kai ta gidansa ba, amma shi ma dai ya aka yi har yasan tana dauke da cikin?” Anty khadijah tace “Toh ai likita ne shi din” Hajiya Laure ta xaro ido tace “Kai haba, to yanxu baxai gane cirewa aka yi ba?” Anty khadijah tace “Yo ya gane mana ai wllh sai yyi xaman aure da ‘ya ta ko ya ki ko ya so, sai ya xauna da ita don ubansa” Hajiya Laure tace “Toh kuma har yanxu uwar ta sa ba ta kira ki ba?” Anty khadijah tace “Tana can na tara mata xafi, ina labarin da na taba baki a kan wata yarinya da ta taba dauka da dadewa??” Hajiya Laure tace “Eh, eh na tuna, wannan dai da kika ce a sunan me aiki ta dauketa, da kika sa Aliyu ya lalata ta” Anty khadijah tace “Yauwa er gari ita, Toh yau dai na tona abinda Aliyun yyi mata, tunda nima tonan asirin ya min, suna can na bar su ban san ya ake ciki ba” Hajiya Laure ta kyalkyale da dariya tace “Amma baki da kirki Khadijah, Toh amma baki tunanin uwar na iya neman yarinyar yanxu ko ta sa ya nemo ta? kin fa ce min sonta take kamar ita ta haifeta” shiru Anty khadijah tayi da wani irin shock baki bude tana kallonta, salati ta sake daga karshe tace “you have a point, wllh Anty fati xata aikata, wannan shine anyi ba ayi ba, xama bai gan ni ba laure bari in koma gidan ayi komai a gabana, xan bar iklima nan ki sa mata ido don Allah” daga haka ta mike ta suri jakarta har tana tuntube ta fice dakin Laure na cewa tayi a hankali. Aliyu ya kusa awa daya tsaye bayan ya koma dakinsa, gaba daya a sanyaye yake bai san ta ina xai fara ba, bai san me xai ce ma Mumy ba, hakan yasa hawaye ya kawo idonsa tunda yake bai taba jin tsanar Anty khadijah ba sai ranan a ransa, dama tasan abinda ya faru tsakaninsa da Iman, then how? Bayan bata gidan abun ya faru, ranan daga shi sai Iman ne a gidan, kofa ya nufa daga karshe gwiwowinsa a sake ya shiga dakin Mumy, ita da aminiyarta Hajiya Balaraba ne a dakin, Mumy tayi tagumi kana ganinta kasan ta yi kuka ne sosai, tun da ya shigo Hajiya balaraba ke kallonsa, ya kasa kallon su ya isa gaban mumy a sanyaye ya duka cikin raunin murya yace “Mumy don girman Allah kiyi hakuri ki gafarce ni, i knw you Neva expect such, but… Mumy ban san ya aka yi ba ni ba halina bane, har yau ban san ya aka yi hakan ba kuma na kasa samun natsuwa, for the past 5 years neman Iman nake….” Katse sa Mumy tayi tace “Kake neman ta tayi maka me, dama kai ka sa yarinyar ta bar gidan nan Aliyu?” Ya kasa dago kansa a hankali yace “Mumy I was confused, I was thinking that’s the only way out for me… I was restless staying under the same roof with her, mumy nasan na cuceta, amma ni nasan ba yin kai na bane don ba halina bane…” kasa ci gaba yyi sbda cracking da muryarsa ya shiga yi ya hade kansa da gado, Bude kofar dakin aka yi Anty khadijah ta shigo, Mumy ta goge hawayen idonta ta daga kai tana kallonta, Anty balaraba ta tabe baki ta dauke kai, karasowa Anty khadijah tayi ta xauna gefen gado ta fashe da kuka cikin rawar murya tace “Yanxu Anty fati ki ji kaxafin da Aliyu yyi ma iklima amma ke abinda ya dame ki daban? Did i and my daughter deserve this” Mumy tace “Ki rabu da ni Khadijah, ki fita ki ban waje, ba don ba don ba wllh yau sai in ce ke din makiyiya ta ce, bakya so na, baki daukeni yar uwar da muka fito ciki daya ba” Mumy na magana ne tana kuka, Aliyu ya mike ya nufi kofa, Sai da ya isa bakin kofa ya juya yana kallon Mumy cikin sanyin murya yace “Na maki alkawarin xan nemo Iman in sha Allah mum, I will repair the damage I made in sha Allah” Mumy ta masa wani mugun kallo tace “And how are you to repair the damage?” Kamar baxai ce komai ba, sai kuma a hankali yace “By marrying her in sha Allah” Girgixa kai mumy tayi tana wani murmushi tace “Noo, babu aure tsakaninka da ita, xaka iya aikata komai domin ta yafe maka idan ta ga xata iya amma banda aure, babu aure tsakaninku, and I told you that long ago, I have my reasons, leave kar ka ci gaba da bata min rai, get out Aliyu” shiru Aliyu yyi yana kallon Mumy a sanyaye, Anty khadijah ta sauke wani ajiyar xuciya tana hamdala a ranta. Tun Khadijah na daurewa ganin twins dinta shiru har dauriyar ya fara karewa, da farko Umma na ta tambayarta inda suka je ita ma ta hakura ta daina ganin ta ki fada sai cewa take yanxu xa su dawo, khadijah ta shiga daki daga karshe ganin har anyi magrib ta dau wayarta ta shiga kiran khaleel da layin da ya kirata daxu, har ya katse bai daga ba, sai da ta kira kusan sau uku ya dauka yace “Uhn me yara to, ki ma cire ran ganinsu yau” xaro ido tayi tace “This is after seven plss…” Ya katse ta yace “Toh ki taho ki daukesu, I can give you the address” daga haka ya kashe wayar, ji tayi hankalinta ya tashi lkci daya hawaye ya kawo idonta, ta sake kiransa bai dauka ba, ta kira yyi sau hudu kafin ya daga, cikin rawar murya tace “Don Allah ka dawo da su dare yyi, Umma ce fa ke ta tambayarsu” Yace “Hmm toh naji” kashe wayar yyi ta xauna bakin gado a sanyaye.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button