Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Aliyu ya mike xaune yana kallonta yace “Did you come to check on me?” Ta tsuke fuska tace “Saboda kai Shureim ne?” Ya shafa kansa bai ce komai ba, ta juya da sauri ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice, sai a sannan ta ja tsaki taji haushin shiga dakin da tayi, parlor ta koma ta dau shayin da ta hada, da kyar take sha don gaba daya bakinta ba dadi, ji tayi kamar xata yi xaxxabi, ta mike ta dau sauran kayan kumallon ta kai dining ta ajiye ta wuce kitchen don wanke cup din shayin ganin baxata ta iya sha ba, xata ajiye bayan ta wanke taji kamar mutum bayanta ta juya da sauri suka kusa cin karo suna hada ido ta hade rai ta dauke kai, ya mika mata hannu a hankali yace “Bani cup din” tace “Saboda xaka amsa cup sai ka tsaya bayana toh” Bata jira me xai ce ba ta ajiye cup din ta fita kitchen din ya bi ta da ido. Har aka yi azahar bata kara fitowa daga dakinta ba, xuwa lkcn ta fara jin yunwa sosai amma ta kasa sakkowa, duk xaman dakin ya isheta, tana ta xuba ido taga kiran Umma amma shiru, ga kewar Shureim da ya cikata, duk abubuwan suka taru suka mata yawa, ta hade kai da pillow tana son yin kuka amma ta kasa. Aliyu na xaune parlor yana duba wasu articles bayan sun yi waya da Sudais yace masa suna hanya, saboda su ma ya dawo parlorn ya xauna, ajiye takardar hannunsa yyi ya dau pain reliever a center table for the second time in 2hrs ya balla biyu ya dau table water dake ajiye ya sha maganin ya mayar da ruwan ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, ya rasa me yasa bai samu relieve ba bayan wanda ya sha daxu, har ya fara bacci a haka ya ji an danna bell, ya bude ido ya mike ya isa kofar ya bude, Baby ce rike da lunch, ganinsa tayi murmushi tace “Yayanmu Ina yini?” Ya shafa kai a hankali yace “Lafiya lau” da damuwa tace “Are you sick?” Ya d’an bude ido yace “Me kika gani?” Tace “You look so” murmushi yayi yace “Am alright” Bata ce komai ba ta shigo parlorn cike da tausayinsa ta ajiye abincin hannunta ta juyo tana kallonsa tace “Ka ma yi breakfast kuwa yaya?” Yace “Nayi mana, ya su Mumy” Xaunawa tayi tace “Suna gaishe ku” ya xauna shi ma yace “Ki kai mata abincin sama” xaro ido baby tayi tace “Uhn ba ruwana, I don’t want to imagine me going to her now” Aliyu bai ce komai, tana kallonsa a hankali tace “You just have to be patient ya Aliyu, soon nasan xata hakura… Kar ka damu kaji yayana, I know it’s just for few days” Murmushi yayi yace “Toh Allah ya sa” cike da tausayin sa tace “Ameen” yace “Plss ki taho da Shureim idan xa ki xo anjima….” Tace “Ae yana can gidansu” yace “Ehh ki dauko sa can din, I am lonely…” Tace “Toh Yaya xan kawo sa” Wayarsa ne yayi ring ya dauka yaga Sudais ke kiransa, yyi pick din call din Sudais yace “Muna waje” Aliyu yace “Alryt ku shigo” Baby na kallonsa bayan ya katse wayar tace “waye yaya?” Yace “Barrister with Dr Ayman I guess” Baby tayi shiru bata ce komai ba, bude kofar parlorn aka yi khaleel ya fara shigowa kafin Sudais, Aliyu ya mike bayan sun gaisa gaba daya suka xauna, Baby na kallon Dr Ayman tace “Ina yini” yace “Lafiya lau ya kike?” Tace “Alhmdllh” kallon Barrister tayi dai dai lkcn da ya kallota shi ma, yace “Ina yini” xaro ido tayi sai kuma tayi dariya tace “Ina yini” yace “Ohk I was thinking baxa ma ki gaisheni ba” Khaleel yayi murmushi yana kallonsa ta gefen ido bai dai ce komai ba, Aliyu ya kalli baby don tsoron xuwa daki gun khadijah yake yace “Baby talk to her tana daki” Mikewa baby tayi ba don tayi niyya ba ta wuce dakin gabanta na faduwa, Khadijah dake kwance ta daga kai jin an bude kofa, ganin baby ce ta mike xaune tana kallonta, a sanyaye tace “Shine daxu baki min magana ba kika wuce ko Baby” Baby tace “Hmm tsoron ki nake ai ni Iman” Baby ta xauna kusa da ita, khadijah ta kamo hannunta a hankali tace “Amma baby kin san wanda aka aura min kika boye min, idan kowa ya boye min ke bai kamata ki min haka ba, Ni yanxu shkkn cikin kunci xan kare rayuwata, nobody is after my happiness….” Hawaye cike idonta ta kare maganar, a sanyaye Baby tace “Nan gaba xa ki gane ma’anar hakan da aka yi Iman, just give my brother a chance… Iman ki manta abinda ya faru a baya, ki kwantar da hankalin ki da Yaya Aliyu you won’t regret it am giving you my words….” khadijah ta dinga share hawayen dake sakko mata bata ce komai ba, tasan ita dai baxata taba kwantar da hankalin ta da wanda yyi disfiguring dinta heartlessly ba, cikin kwantar da murya Baby “Kiyi hakuri Iman, nima wllh ban san da yayanmu aka daura auren ba sai da muka tashi barin gida jiya da yamma kin dai ji na rantse maki” Har sannan khadijah bata iya ta ce komai ba sai goge idonta take, Baby tace “Ki sakko ki xo gu gaisa da su Barrister suna parlor” Kallonta khadijah tayi da sauri ta tsuke fuska tana girgixa kai tace “Am not going anywhere, they are nothing but group of deceivers…” duk yanda baby ta dinga lallabata Khadijah kin yarda ta fito tayi har da kukan ta, baby ta rasa yanda xata yi, mikewa tayi daga karshe ta dawo parlor, Aliyu na ganinta yasan kwanan xancen, Baby ta kirkiri murmushi tace “Tana fa bacci ne, Kuma bana son tada ta….” Murmushi Sudais yyi yana shafa beard dinsa a hankali yace “That’s nyc, thanks for covering up for her, but we are not strangers, kuma baxa mu ji haushi ba idan kin ce tace baxata fito ba, wataran xata fito mu ganta ai” Dariya khaleel yyi yana kallon baby da ta rikice sai rawar baki take, Aliyu yyi murmushi bai dai ce komai ba, Sudais na kallonta duk da dariyar da ta basa shi ma yace “Sorry, just relax Mami ni ban yi haka don ki rikice ba” Baby bata san lkcn da ta balla masa harara ba ta juya da sauri xata wuce tana murmushi, Aliyu yace “Kawo masu drink” kitchen ta wuce ta dauko masu drink din ta ajiye, Aliyu yace “Abinci fa?” Sudais yace “Nop Alhmdllh” mikewa baby tayi ta dau abincin ta wuce sama, Dakin khadijah ta shiga tana harararta ta ajiye abincin hannunta tace “thanks for making me look stupid downstairs, Kuma abincin ma na daina kawowa sai dai ku fita eatry da mijin naki” daga haka ta wuce, tana shiga parlor tace “Yaya ni xan koma, Mumy tace kar in dade” Yace “Alryt then, da driver ku ka xo?” Ta girgixa kai yace “Toh je sama ki dau transport” Khaleel yace “Xa mu wuce yanxu sai Barrister yyi dropping dinta tunda hanyar daya” Har bakin mota Aliyu ya raka su bayan sun wuce ya dawo cikin gidan, sama ya wuce ya bude dakinsa ya shiga ya kwanta. Har aka yi la’asar khadijah na daki, duk da ta ji gidan shiru ta kasa fitowa ta dau plate ta debi abinci, Tana tunanin yanda xata fita aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo, sau daya ya kalleta ya mayar da dubansa kan abincin da Baby ta ajiye dakin, ya isa gun abincin yace “Ain’t you eating the food?” Banxa tayi masa, ya duka ya bude warmer din yana kallon abincin, dauka yayi ya juya ya nufi kofa ta bi sa da wani kallo, ganin ya fita ta tashi da sauri ta bi bayansa har ya shiga dakinsa ta shiga ya juyo yana kallonta, tace “Nace maka na ci abincin ne ni?” Kamar xata yi kuka tayi maganar, dariya ta basa, ya yi murmushi yace “You never told me” daga haka ya mika mata ta karbe abincin ta juya ta fita, yana jin ta sauka don dauko plate a kitchen ta dawo ta shiga dakinta, sai a sannan ya sauka xuwa kitchen ya hada shayi, duk da yunwan da khadijah take ji bata iya ta ci abincin me yawa ba, ta mike daga karshe ta fita, har xata kai abincin kasa sai kuma ta tsaya a hankali ta bude dakinsa ta gansa xaune yana rike da cup din shayin, ta sauke kanta kasa ta shiga dakin ta ajiye masa warmer din ta juya ta fita ya bi ta da ido. Karfe shidda saura baby ta dawo gidan tare da shureim, Sau uku tana danna bell, khadijah ta mike ta sauka bata san Aliyu ma ya fito bude mata ba, yana bude kofar Shureim ya wara ido ganinsa cike da murna yace “Unclee” nufo sa yayi da nufin rungumesa ya hango khadijah, Wara ido ya kara yi yace “Anty….” Murmushi ta sakar masa ta buda masa hannu, Har ya dau hanyar inda take sai kuma ya tsaya ya juyo yana kallon Aliyu dake kallonsu, dawowa yyi gun sa da gudu, Aliyu ya daga sa sama ya rungume sa yana murmushi yayi Pecking cheek dinsa, Lkci daya murmushin fuskar khadijah yayi fading, Baby bata san lkcn da ta fashe da dariya ba, Shureim ya xame daga jikin Aliyu ya nufi khadijah da gudu, wani kallo ta watsa masa tace “If I slap you” nan ya taka burki ya tsaya yana kallonta, Ta turo baki ta juya ta wuce sama, Murmushi kawai Aliyu yayi ya nufi yaron ya daga sa sama yace “How are you sweetheart” yace “Am fine” Baby ta ajiye abincin hannunta tace “Ina yini yayana” yace “Alhmdllh” tace “Driver na jira na waje, sai da safe” yace “Alright ki gaida mumy, tell her thank you” tayi murmushi tace “Toh yaya” daga haka ta juya ta wuce tana daga ma Shureim hannun, yana rike da Shureim suka haura sama ya shiga dakin khadijah ajiye mata shi yyi kusa da ita yace “Greet her now” a hankali Shureim yace “Anty good evening” dauke kai tayi ta hade rai tace “Evening” Daukansa Aliyu yayi suka fita dakin ta bi sa da wani kallo, har karfe kusan tara na dare khadijah bata ji motsin su ba, ta yi wanka ta shirya cikin night wear, jin shirun yyi yawa ta sa Hijab ta fita, ta fi minti biyu a tsaye, kafin ta tura kofar dakin a hankali, duhu ne dakin, ta laluba ta kunna switch, kwance taga Aliyu Shureim na kwance kusa da shi duk sun yi bacci, kashe Ac dake aiki tayi ta kashe switch din ta fita dakin ta koma nata ta kwanta. Kasa bacci tayi sai juye juye take har kusan sha biyu ta ji an bude kofa, sosai gabanta ya fadi ta kalli direction din kofar duk da wuta a kashe yake, rufe kofar yyi ba tare da ya kunna wutan ba ya iso har inda take ya duka, mirginawa tayi da sauri daga wajen tace “Meye haka?” Yace “Na xo duba ki ne kamar yanda ke ma kika xo duba mu” Xaro ido tayi tana kallonsa cikin duhun, yyi murmushi murya can kasa yace “Sweet dreams” daga haka ya fita ya kulle kofar dakin.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button