Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Haske writers association????

Noor-Al-Hayat

By khaleesat Haiydar????✍????

6……

Nigeria

Ajiye fork da knife din hannunsa yyi ya tura abincin gabansa lkci daya ya fuzar da iska ya dau tissue yana goge bakinsa ya mike ya bar dinning din, mum dinsa dake xaune parlor ta bi sa da wani kallo tace “Barin abincin kayi sbda xancen da nake maka Aliyu?” Kallonta yyi da sauri yace “Noo, not at all Mum, xan je sallama da Granny ne coz am leaving as early as possible tomorrow” daga haka ya dau makullin motarsa da ya ajiye kan Center table ya nufi kofa yace “Sae na dawo mum” tagumi mahaifiyar tasa tayi ta bi sa da kallo cike da damuwa har ya fita, ya fuzar da iska bayan ya shiga motarsa ya jinginar da kai jikin kujera hade da lumshe ido yace “Ba ta taba barin in ci abinci in koshi Mum, always with a particular complain” ya bude ido a hankali snn ya tada motar yyi horn mai gadi ya bude gate ya fita rai ba dadi, bai yi minti goma yana tafiya a Independent way ba wata 206 dake gabansa ya taka wani burki da har sai da ya kusa bugesa ba dan shi ma yyi saurin preventing hakan ba, wanda hakan kuma ya janyo motar dake bayan tasa motar ta buge sa, Kilan rudewa ya sa me 206 din ya juye kan steering wanda hakan yasa ya buge motar gefensa shi ma da karfi, everything just happened all of a sudden, lumshe ido Aliyu yyi ya bude yana kiran Allah a xuciyarsa bayan komai yyi still kamar ba ayi ba, sai a sannan ya lura da wani bike ne ya shigo ma mai 206 din yyi kkrin avoiding da ya janyo faruwan slight accident din, Aliyu ne ya fara fitowa daga motarsa daga nn kuma kowa ma ya fara fitowa, ya nufi 206 din da har driver din ya fito da sauri ya bude back seat, kukan yara ke tashi a motar, jin hakan Aliyu ya karasa da sauri gun motar, identical twins ne bayan motar da baxa su wuce shekaru biyar ba, Aliyu ya fiddo su duk biyun daga motar yana kallon yaran dake sanye da uniform din makaranta ya durkusa a hankali yace “Hey boys are you okay??” Dayan kadai ne ya gyada masa kai a tsorace, dayan kuwa banda kuka babu abinda yake yana kiran Anty, kallon yaran kawai Aliyu yake ko kiftawa bbu, muryar mutanen da ke tsaye gun kowa na fadin albarkacin bakinsa yasa shi mikewa a hankali yana shafa kansu yace “Sorry Boys, Allah ya tsare gaba” Wani mutumi ne ya dinga tambayarsu inda ke masu ciwo duk suka girgixa kai, Aliyu ya daga kai jin abinda mutumin da ke gefensa ke ce masa yana kallonsa, “Allah dai ya kiyaye gaba ka tafi da yaranka gida kawai, Allah kyauta na gaba” cewar mutumin kenan, wani mutumi ma ya sake fadin makamancin hkn, murmushi yyi yace “No, ni ban san su ba” mutumin karshe da yyi magana ya kalli yaran sannan Aliyu, kada kai yyi yace “Ikon Allah….” bude bayan motar Aliyu yyi ya shigar da yaran yana kallon Drivern yace “Ka ajiye su gida, Allah ya kiyaye gaba” godiya Drivern yyi ma mutanen wajen ya shiga motar ya tada ya hau kan titi ya bar wajen. Aliyu ya koma gun motarsa ya shiga har lkcn cute twins din na ransa, bai kuma damu da kallon da wasu suka bi sa da shi ba. A waje yyi parking ya shiga gidan grandmum dinsa da sallama bayan sun gaisa da masu gadi, wata budurwa ce da baxata wuce shekaru ashirin da daya ba kwance kan kujera dake parlon tana danna waya, sau daya ya kalleta bai sake kallon inda take ba ya wuce dakin grannynsu da suke kira da yaya, sllh ya sameta tana yi ya kalli agogo sanin Magrib bai yi ba, ya tabe baki ya dawo parlon ya xauna ko sallan me take, ba a dau lkci ba ta biyosa tace “Mijin ka xo kenan” ya gaisheta ta amsa da fara’a tana tambayarsa ya hanya, yace “Alhmdllh” ta kalli budurwar dake kan kujera tace “Ke koh Salmah kun gaisa da yayan naki” yarinyar ta gyada mata kai idonta a kan waya, ya kalleta fuskarsa daure yace “Uban wa kika gaida?” Ba ta ko kallesa ba tace “Yaya ni ki ce ya daina xagi na plss” Mikewa grandmum din tasu tayi tace “A’a ni dai gaskiya ba a gidana ba yau, ku je can gidan iyayen ku ba ruwana, kai kuma naga ai ba dole bane sai an gaisheka, ke kuma sa’an ki ne shi din da baxa ki gaishesa ba” mikewa yyi ya nufi kofa, kakar ta bi bayan sa da sauri tana cewa “Ina kuma xaka Aliyu” bai juyo ba yace “Sallama dama na xo maki gobe xan wuce Uk….” da sauri take bin sa ganin yaki tsayawa tace “Toh baxa ka tsaya ba ina ma magana” yace “Mu yi waya” bata fasa bin sa ba tana cewa “Da kai fa nake Aliyu…” juyowa yyi yace “Don Allah yayah ki rabu da ni dama sallama na xo maki kuma gashi na maki dai ko” rike ha6a tayi tace “Yo ni me ya sha min kai da sallamar ka da rashin sa, magana ce dai baxan fasa maka ba tunda ba tsoronka nake ba, baka kuma isa inji tsoron ka ba, kum maganar dai da baka so ce xan maka wato maganar aure, Aliyu sa’annin ka daga me d’an shekara biyar sai mai d’an shekara shidda kai har bakwai akwai, yanxu kai baxa kayi ma kanka fada ba kasan inda ke maka ciwo d’an nan, ga mahaifin ka ya xuba ma na mujiya ya kyaleka ya fita lamarin ka, me kake son mayar da rayuwar ka ne, idan ma lafiya ce baka da ba sai ka mana bayani ba ko ni in kai ka asibiti amma ka mayar da mu shashashai….” tsaye yake yana saurarenta sai dai bai juyo ba har ta kai karshe sannan ya juyo yana kallonta yace “Allah kawo lkci yayah” daga haka yyi ficewarsa daga gidan, ya jima xaune mota ya kasa barin anguwar, ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido a hankali ya bude cikin sanyin murya yace “Can I ever get her? Then Where?” Lkci daya idonsa ya kada ya hade kansa da steering, ya fi minti goma a haka kafin yyi karfin halin dagowa ya tada motar ya bar gun jikinsa a sanyaye, yana hawa independent way yaran daxu suka fado masa, ya d’an yi murmushi loving to see them once more and their parents. Bai yarda ya wuce gida ba a lkcn kawai ya wuce gidan abokinsa kuma amininsa Farouq, ganin Magrib tayi sai da ya fara shiga masallacin dake anguwar don gabatar da magrib bayan yayi alwala, ana idarwa kuma suka fito tare da Farouq, gaisawa suka yi Farouq yace “D’an rashin kirki kace min xaka dawo ranan kasa Madam tayi serving har da kai amma kaki dawowa, ina ta xuba ido, I called kuma you refused picking saboda kasan baka da gaskiya koh” Aliyu ya shafa kansa yana murmushi yace “Na ma mance me ya hanani dawowa wllh” har suka shiga gida mitan xancen Farouq yake, suka karasa har parlor, Boys din Farouq suka taho da gudu don gaida abokin dad din nasu, Aliyu ya rungumesu yana tambayar su ya school suka ce masa “Alhmdllh” Wara ido yayi yace “Toh ban ga “Baby Fiddausi ba” Ahmad yace “She’s upstairs with mum” yace “Alryt maxa ku je ku ce masu Ina gaishesu” Ahmad me shekara shidda da kaninsa takwaran Aliyu suka wuce daki da sauri. Farouq dake ta kallon Aliyu yyi kasa da murya yace “Doctor….” Kallonsa Aliyu yyi da sauri, Farouq yace “I don’t knw, may be am nt worth ur best…” Aliyu ya d’an bude ido yace “Ban gane ba Umar” Farouq ya girgixa kai yace “Kullum tambayata why did you prefer living as a bachelor ka ki bani answer, what’s ur problem Aliyu, am I not worth knowing ur problem, I would love seeing ur kids Frnd duk clique dinmu kai kadae ne Bachelor har ynxu, tell me why… I beg you…” Kallonsa kawai Aliyu yake can yyi murmushin karfin hali ya kauda kai yace “Xan yi Farouq, lkci ne kawai” a d’an fusace farouq yace “Na gaji da jin haka Ali.. For good six years this is always ur reply, kudin gashi kana da su Alhmdllh, yan matan gasu kawo maka hari suke ta ko ina…. Toh meye kuma yayi saura??” Aliyu dai bai ce komai ba sai danna wayarsa da ya fiddo yake, farouq na masa wani kallo yace “Ko Iman din dai kake jira har yanxu, I mean aljanar nan taka…” Aliyu ya dago da sauri hade da yin murmushin da ya fiddo da ainahin kyansa na fillo ya karyar da kai yace “Yeah” tsaki farouq ya ja yana girgixa kai cike da takaici, Aliyu ya dafe shoulder dinsa a hankali yace “Look frnd, wllh ba aljana bace mutum ce kamar ka, ka bar ce mata aljana” Farouq yace “Toh wai ni abinda ban gane ba a nan shine ita ta san ka?” Aliyu ya sauke manyan idanuwansa daga kallon abokin nasa a hankali yace “Yea may be tasan ni, may be kuma bata san ni ba” Wani dariya Farouq yyi har da kyakyatawa yace “Wllh baka da hankali Haiydar, wato bata ma san ka ba?” Murmushi kawai Aliyu yyi yana shafa cute beard dinsa bai dai ce komai ba, Farouq yace “To what if tayi aure? Ko kuma tana da aure?” Murmushin fuskar Aliyu ya bace lkci daya ya mike a fusace yace “Billah sai ya saketa ko ma waye shi… Na rantse da sarkin dake busa min numfashi xan iya kashe ko ma waye ya aureta” sakin baki Farouq yyi da mamaki yana kallonsa, yana kikkiffta ido yace “Aliyu are you alright kuwa, wani irin rantsuwa da threat ne haka, anya kana right sense din ka kuwa” Ko kallonsa Aliyu bai yi ba ya nufi kofa, Farouq ya mike da sauri ya rikosa yace “Habaa, Toh Allah baka hakuri, let eat plss, In sha Allah ma Iman bata yi aure ba duk da ni dai billahil azim ban yarda ba aljana bace” yana magana ne yana satan kallon Aliyu da har lkcn fuskarsa ke daure, da kyar dai ya samu ya lallabasa ya dawo ya xauna, Aliyu ya lumshe ido yace “In kaji wacece Iman din nan xa kayi mamaki Umar” Farouq yace “Toh don Allah ka gaya min wacece” A takaice Aliyu yace “Noo baka santa ba, bata sanka ba, kilan ni kadai na santa” dariya sosai Farouq yyi yace “Ko da yake gogan ma bai san ko ta san shi ba balle ni, wllh you look confused Aliyu, Allah ya yaye maka wannan bala’i” Aliyu ya kallesa yace “Plss xancen Iman da muke ya tsaya iya nan kar ko da wasa wataran kaje can gida kana cewa Iman” Farouq yace “Why, ko sun santa?” Aliyu ya girgixa kai yace “A’a kawai dai kar ka sa a daukeni mahaukaci ne” Farouq ya jingina kai yana murmushi yace “Hauka kam ka jima da fara sa ai frnd”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button