Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Umma na dawowa cikin gidan ta tafi daki gun Khadijah a daki, xaune ta sameta kasa ta hade kai da gwiwa tana kukan takaici, Umma ta sauke ajiyar xuciya tace “Amma Khadijah ban taba xaton haka daga gare ki ba, da ilimin ki bai kamata kiyi abinda kika yi ba, ina ce ko ba komai xai ci albarkacin mahaifiyarsa, ke da kanki kin bani labarin irin abubuwan da tayi maki while with them, me yasa xa ki mance hakan da wuri, don me laifin d’an ta xai shafeta, me yasa ko don ita baxa ki raga masa ba, ni ban ce lallai sai kin kulasa ba, Amma for the sake of his mum….” Cikin kuka tace “Umma kiyi hakuri, but I have nothing to do with Aliyu and his family again, I will pretend ban taba rayuwa tare da su ba, don Allah su rabu da ni su bar min yarana su je na yafe masu, ina jin kunyar mahaifiyar sa shi yasa nake raga masa, only me knew wat I passed through in life, ni kadai nasan abubuwan da na fuskanta a rayuwa shekarun baya, Umma na sha wahala, na ji na tsani rayuwar, ban taba sanin xan yi surviving ba ummata, da ba don sudais ba da ban san me xai sameni ba, me yasa rana tsaka Aliyu xai dawo rayuwata yana min gadara a kan yaran da bai ma san da su ba, why Umma??” Umma ta xauna duk jikinta yyi sanyi tace “Ni ba nace ki yarda da Aliyu bane Khadijah, amma kiyi hakuri ko domin mahaifiyarsa ki yafe masa, ki mance past din ki” tana kallon umma da jajayen idanuwanta tace “Na yafe masa amma kar ya sake cewa shi ne uban yarana, kuma da kai na xan shirya in tafi in dauko yarona gidansu gobe, it’s better Barrister sudais ya raba ni da su then ace Aliyu, saboda shi ne ya sha wahalar su kuma shi ya koya min sonsu ba don shi ba kilan da sun mutu yanxu” shiru Umma tayi ta kasa cewa komai tana kallonta, mikewa khadijah tayi ta hau saman gado ta kwanta, Umma ta mike a sanyaye ta kama hannun Shureim dake ta kallon uwar tasa ta fita da shi. Mikewa xaune khadijah tayi jin wayarta na ring ta dau wayar, ganin khaleel ne ta daga ta kai kunne tayi masa sallama cikin sanyin murya, Daga daya bangaren ya amsa a hankali yace “Sun kawo maki yaran Khadijah?” Ta fashe da kukan takaici tace “they brought just one, Shureim kawai suka kawo, ya tafi da sudais” Khaleel yace “Saboda me?” Cikin kuka tace “Wai xai kai sa asibiti, I don’t knw ko meye damuwarsa da ciwonsa, ni dai ya rabu da yarana, ya kyale min su” Khaleel yyi shiru na wani lkci kafin yace “Kar ki damu xa su dawo maki shi, bana son ki kara sa ma kanki damuwa Khadijah, and plss because of his mother let take everything easy, kar ma ki sake kulasa, sure baxata bari ya dauke maki kids ba, kin san ana barin halak ko don kunya, am sure soon xa a dawo maki da little Sudais kin ji” kai kawai ta gyada masa hawaye na sauka idonta, yace “Sleep without worries plss Khadijah” a hankali tace “Toh nagode” daga haka ya katse wayar, ta koma ta kwanta ta lumshe ido, cikin dare misalin karfe biyu Khadijah na xaune kan darduma bayan ta idar da slh taga wayarta yyi haske alamar shigowar text, ta mike a hankali ta isa gun wayar, message din barrister Sudais ta gani ta dauka ta bude tana kallon content din, “Dear am sorry I didn’t call, na shiga gida ne da wuri jiya, but mun yi communicating da Dr Ayman, he told me everything, you don’t worry xa a dawo maki da little sudais soon, gobe da safe xan xo in sha Allah, sleep without thought plss” tabe baki tayi ta ajiye wayar ta koma kan darduma ta xauna, har kusan asuba Khadijah bata runtsa ba, damuwa yayi mata yawa sosai ga yawan faduwar gaba da take ta ji, karfe hudu saura umma ta shigo dakin da Shureim ganin khadijah kan darduma ta isa kusa da ita da yaron tace “Gashi ya ki bacci, his temperature is high but na basa paracetamol, wai xai xo wajen ki” xaunawa Shureim yyi kusa da ita yana kallonta yace “Anty yaushe sudais xai dawo, I want to see him” Umma tace “Au abinda ke damun ka kenan” murmushii tayi ta juya ta fita tace “ka gamu da aiki kam” Khadijah ta jawo sa jikinta a hankali, taji jikin nasa ya dau xafi sosai, dago kansa tayi tace “Are you feeling pain anywhere?” Ya girgixa mata kai yace “I want to go to my brother” ta rungume sa sosai tace “Gobe xai dawo ka ji” ba a dau lkci ba yaron yayi bacci a jikinta ta mike ta daukesa ta kwantar kan gado, ta koma ta xauna tana jiran lkcn sllhn asuba. Washegari da safe Mumy na xaune kusa da Sudais da Aliyu ke sa ma drip da damuwa tace “Abuturrab ko xa ku je asibiti dai a kara duba sa, he is suffering slowly…” Aliyu ya kalleta yace “He will be okay mum, na dubasa babu wani matsala, a hankali xai dinga recovering, and it looks as if he is missing his twin, tun jiya yake ta tambayar sa” Tace “Toh ko xa a mayar da shi gidan ne?” Da kamar baxai ce komai ba, sai kuma yace “Mumy bari ya kara samun lafiya” Baby ce ta shigo da wayar Mumy dake ring ta mika mata ta fita, Mumy ta karba ta daga kiran, shiru ta d’an fara yi kafin tace “Ehh ni ce, who is on the line” ganin Mumy bata sake cewa komai ba sai shock da ya bayyana a fusakarta, a hankali afterward ta sauke wayar daga kunnenta tana kallon screen din, Aliyu dake kallonta yace “Waye mumy? Me ya faru?” Kallonsa tayi a sanyaye tace “Ka sake kiransu kilan ban ji da kyau ba ne” Aliyu ya amshi wayar ya kira number, bayan wani lkci aka dauka, abinda aka fadi ma Mumy aka sake maimaita masa, ya d’an bude ido shi ma lkci daya yace “Subhanallah, to ga mu nan xuwa, mun gode” daga haka ya katse wayar yace “Mumy wai Anty khadijah na asibiti…” A hankali mumy tace “Toh sai ku je, ni kam baxan je ba” ya bata fuska yace “No plss mumy kar ki ce haka, tunda har aka kira ki mu je kawai, baxa a biye ta halinta ba, kuma ai ba a canxa ma tuwo suna she still remain ur sister” da kyar Aliyu yyi convincing Mumy ta yarda xa ta je. Umma tayi pecking din goshin Shureim har sannan jikinsa da dumi tana shafa kansa tace “You behave your self kaji my boy, kuma ban da fada a gidan” Kai ya gyada mata, Khadijah ta kama hannunsa suka fita parlorn, khaleel na jingine jikin motarsa har suka iso inda yake, ya duka yana kallon kyakkyawan yaran a hankali yace “How are you Darling” murmushi Shureim yyi yace “Am fine uncle” mikewa khaleel yyi ya kama hannunsa yana kallon khadijah yace “Toh sai mun yi waya…” murmushi tayi tana bin sa da kallo tace “Nagode, byee” daga haka ya bude front seat ya saka Shureim ya xaga ya shiga maxaunin driver ya tada motar ya bar layin, Khadijah ta juya to koma ciki feeling relieved. Shureim na wasa da wayar khaleel yace “Uncle baxan sake ganin Sudais ba?” Khaleel ya d’an buda ido ya kalllesa yace “In ji wa ya gaya maka haka?” Ya langwabar da kai bai ce komai ba, duk sai ya basa tausayi, a hankali Khaleel ya shafa kansa yace “Xai dawo soon ka ji my boy” har khaleel ya isa gida Shureim bai sake cewa komai ba, gida ne mai girman gaske, Shureim ya wara ido yana bin makeken compound din da kallo yace “Uncle is this ur home” khaleel yyi murmushi ya gyada masa kai bai dai ce komai ba, yaron yace “It’s big” parking khaleel yyi a parking space ya fito ya xaga ya sakko da yaron sannan ya nufi entrance na babban parlorn gidan yana rike da hannunsa, yara ne da baxa su wuce Shureim din ba su uku duk maxa kusan duk kamanninsu na larabawa suna wasa parlorn da puzzles, suna ganin khaleel suka yo kansa da gudu suka rungume sa suna gaishesa da larabci, ko wannensu cike da murnan ganinsa, Dukawa yyi duk ya shafa kansa yana murmushi yace “I brought you a new friend, Shureim by name” Murmushi Shureim yyi yana kallonsu yace “Hey” sallama suka yi masa gaba daya, khaleel yyi dariya sosai, ya mike ya kama hannun Shureim suka wuce sama yana waigo yaran, bedroom din Ummun sa ya tafi da shi, Wata balarabiya ce da baxata haura sittin ba xaune dakin tana waya da halshan larabci, ya xauna gefen makeken gadon ta, ya dau Shureim ma ya ajiye sa gefensa, tana gama wayar ta juya tana kallon khaleel tace “Sai yanxu” gaisheta yayi ta amsa da murmushi ta na kallon shureim tace “Ina ka samo mana yaro” Ya shafa kai a hankali yace “Ummu… Khadijah da nake baki labari, he is her son Shureim” Umma tace “Maa sha Allah, xo in ganka sweetheart” Shureim ya sauka kan gadon ya tafi gunta ta jawo sa ta rungume sa tace “Ya ummun ka fa?” Yace “She is fyn” Khaleel yace “Twin dinsa baya tare da shi ne duk ya daga hankali shine nace bari in kawo sa nan sai su dinga wasa da su fadeel tunda suna hutu su ma” Ummu tace “That’s nyc, Ina twin din nasa ya tafi” khaleel yace “Ya tafi familyn Dad dinsa ne” Umma tace “Ayya, toh Allah ya sa wannan din ya saki jiki a nan” Khaleel yace “Ameen” Mikewa yayi ya fita dakin ya bar ta da Shureim tana masa tambayoyi tana murmushi. Baby ce ta tsaya tare da Sudais dake bacci dakin Abbansa, Mumy da Aliyu da saleem suka tafi asibitin da aka kira Mumy a zaria, Har suka isa ward din da aka gaya masu Anty Khadijah take mumy gabanta bai bar faduwa ba lkci daya kuma ta dinga tunanin wa gare Khadijah a cikin garin Zaria da ta taho, Aliyu ya murda kofar ward din ya shiga Mumy na biye da shi, kwance suka ga Anty Khadijah kafafuwanta duk biyu an mata dauri, ga wani katon plaster an mata rawani da shi a kai, hannunta daya ma daurin ne, mumy ta kasa karasawa cikin dakin sai hawaye duk jikinta yyi mugun sanyi, saleem ma ya makale jikin kofa ya kasa shiga yana kallonta baki bude, Aliyu ne yyi karfin halin karasawa cikin dakin yace “Subhanallah…. Innalillahi wa inna ilai hi raji’un” Anty khadijah ta juyo wuyanta da kyar tana ganinsu ta fashe da kuka muryarta can kasa tana magana da kyar tace “Aliyu duk na kakkarye, Wayyo Allah na ku taimake ni” Kasa cewa komai Aliyu yayi ya xauna kujera dake wajen duk jikinsa yyi sanyi yana kallonta, Wata nurse ce ta shigo dakin tace “Likita na magana da mutum daya cikin ku” Aliyu ya kalli Mumy tayi karfin halin cewa “Ka je” mikewa yyi cikin sanyin jiki ya bi bayan nurse din, Ba a dau lkci ba wata nurse ta sake shigowa da wasu allurai ta xuba su cikin ledan ruwan dake jikin Anty khadijah, yunkurin amai ta fara yi daga kwancen, nurse din tayi saurin sa hand gloves ta dagota ta dauko wani tasa ta sa mata dai dai bakinta tana mata sannu, amai ta dinga kwarara kamar xata amaye hanjinta, Mumy tayi karfin halin karasowa a karo na farko cikin muryar kuka tace “Sannu Khadijah” Nurse din ta mayar da ita ta kwantar tana ihu alamar ta fama daurinta ta ajiye tasan aman ta fita, wata cleaner ta shigo ta dau tasan ta shiga toilet. Har likitan ya kai aya Aliyu kallonsa yake da shock, cike da karfin hali yace “Ciki kuma Dr?” Likitan ya mika masa result din yace “In sha Allah, gashi nan har wata uku” kasa cewa komai yyi ya mike ya bar office din rike da sakamakon, tun bayan da suka yi hatsarin jiya da daddare da aka taho da ita asibiti ga karaya ta ko ina, ga amai da take ta kwarara ya sa likitan ya sa a mata gwajin ciki don a san irin treatment din da xa a mata, ai ko result na fitowa ya ga cikin ne da ita har wata uku, Aliyu ya share xufar dake keto masa ya shigo ward din yana kallon mumy dake ta goge hawaye tana kallon yar uwar tata, mika mata result din hannunsa yyi ya jingina da bango duk jikinsa a sanyaye.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button