Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Ta fi 10 seconds a tsaye ganin babu haske a dakin, bata kunna wutan ba saboda akwai d’an hasken na corridor kuma a bude ta bar door din, ta nufi gaban mirror a hankali don ajiye wayar hannunta, lkci daya ta juya jin an rufe kofar dakin duhu ya gauraye ko ina, saurin ajiye wayar tayi ta nufi kofar tana cewa “Why is that….” Xaro ido tayi ganin kamar nufota yake yi ta dinga komawa baya kamar xata yi kuka tace “Meye haka Aliyu, ka bude min kofa in fita, I only brought you ur mobile phone” murya can kasa yace “Why did you pretend you were sleeping” jingina tayi da banga xuciyarta na bugawa ta marairaice tace “Laifi ne don na kawo maka wayarka? to ka bani in mayar I thought you need it ne dama” Yana d’an murmushi yace “Better… dauka ki mayar” tace “Toh ka matsa” a hankali ya koma gefe idonsa a kanta, ta taho xata wuce gabanta na faduwa kawai ta ji ya fixgota xuwa jikinsa ya rungumeta gam, jikinta ya dau bari tace “Wayyo na shiga uku, meye…” Bai bata damar karashe abinda xata ce ba ta xaro ido tana kallon kwayar idonsa, passionately yake kissing dinta, tun tana kokarin kwace kanta har tayi give up, lkci daya jikinta ya mutu gaba daya ta ji ta kasa tsayuwa, bata ankara ba bayan lokaci me tsawo sai ganin su ta tayi saman gado, jikinta ya dau rawa a tsorace tana girgixa masa kai hawaye na sakko mata tace “Noo Aliyu, I still haven’t forget the experience, it’s always fresh, don Allah kayi hakuri, and….” kasa ci gaba tayi tana kuka a hankali, Aliyu da lokaci daya ya bar abinda yake jikinsa yayi sanyi, ya kai bakinsa kunnenta cikin sanyin murya yace “And… what?” Cikin shessheka tace “You didn’t follow the teachings of our prophet” komawa yayi a hankali ya kwanta ya lumshe ido yana maida numfashi, ta rufe kanta duvet har sannan hawaye ya ki tsaya mata gabanta na faduwa, a tunaninta yayi bacci don an dau lkci me tsawo bai motsa daga yanda yake kwance ba, a hankali ta mike ta maids wears dinta, xata fita ya mike ya jawota ya rungume cikin sanyin murya yace “I am… sorry Iman” ita dai bata ce komai ba, ita dai bata ce komai ba tayi lamo jikinsa, yana jin yanda xuciyarta ke bugawa, bayan wani lkci ganin ta nutsu ya kwantar da ita a hankali ya sauka daga kan gadon ya shiga bathroom, har bacci ya dauketa bai fito ba. Da asuba ta ji ana shafa fuskarta a hankali ta bude ido, murmushi ya sakar mata yana kallonta yace “It’s time for prayer” Rufe ido tayi da sauri don ya kunna fitilan dakin, yana murmushi yace “In kashe wutan?” Cikin sanyin murya tace “Yes plss” mikewa yayi ya kashe, sai a sannan ta mike xaune a hankali, ya dinga kallonta cikin duhun, Bata yarda ta tashi kan gadon ba ta kallesa tace “Toh baxa ka je masallaci ba?” Yace “We just finished now” Turo baki tayi ta mike tace “Toh ni ba nan xan yi alwalan ba” yace “Saboda me?” Bata ce komai ba ta nufi kofa, ya mike da sauri ya rufe yace “Cinye ki xan yi a nan din?” Kamar xata yi kuka tace “Ka bude min plss” yace “Sai kin yi a nan” tace “Baxan yi ba” yace “Why?” Tace “I have my reasons, kuma ba dole bane ai” murmushi yayi yace “Baki son in ga kin yi wanka?” Xaro ido tayi tace “Kamar ya?” Yace “kamar yanda nayi jiya” ta hade rai tace “Ka bude min Aliyu” yace “Toh tafi bathroom kiyi wankan ki a can” ya fadi hakan yana nuna mata bayin sa, a fusace tace “Ce maka nayi wanka xan yi, a kan wani dalili xan yi wanka” Murmushi yayi ya koma kan gado ya kwanta yana kallo ta cikin duhun, ta fi minti goma tsaye tana masa magiya amma ya ki budewa, ta fashe da kuka daga karshe ta durkushe wajen, ya mike yana dariya ya bude kofar yace “Toh tafi kiyi wankan ki” sai da ta fita tace “Ba wanka xan yi ba sai dai swim” daga haka ta shige dakinta ta rufe tasa makulli, turo baki tayi ta shiga bathroom dinta tayi wanka ta dauro alwala ta fito. Tana ta xaune kan darduma har gari ya waye ta mike a hankali ta shiga gyara dakinta ta wanke har bathroom sannan ta fito parlor don gyaran gidan, sai kusan karfe takwas da rabi ta gama ta shiga kitchen, Irish ta deba tana fere wa, Jin kamshin da ya ziyarci kitchen din ta juya a hankali tana kallon bakin kofa, tsaye ta gansa ya jingina da kofar ya rungume hannunsa yana kallonta, sauke idonta tayi ta ci gaba da abinda take, ya karasa cikin kitchen din ya tsaya bayanta, murya can kasa yace “Good morning Iman” kasa cewa komai tayi, kuma bata juyo ba ta ci gaba da peeling din Irish da take, har ta gama yana tsaye bayanta, a hankali ta juyo suka hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta, jawota jikinsa yayi yana kallonta cikin sanyi yace “Forgive me once more for what happened seven years back Iman, I made you a mother with kids out of wedlock at a very tender age, I know this will always remain in ur memory till the end, nasan kuma da kin gan ni sai kin tuna da hakan, kamar yanda nima in dai na ganki I do felt guilt deep inside me, I want us to get rid of that Iman, I want to have peace with you as my wife, nasan baxan iya biyan ki irin wahalan da kika yi ta dalilina ba, but forget the past plss let build our new home Iman, i promise to love you till the end, I promise to be by ur side till the end, nayi alkawarin xame maki haske a rayuwar ki till the end, I never bargained for this Iman, Allah ya gani na so haskaka maki rayuwar ki xuwan ki gidanmu, na so maki duk abinda xan yi da baxa ki yi maraicin iyayen ki ba, sai dai muna namu Allah kuma na nasa, kaddara kuma ta riga fata, kuma a matsayin mu na musulmai we have to accept it either good or otherwise, all we have to say now is Alhamdulillah” Bata iya ta dago ba hawaye ya dinga xuba idonta, a hankali ta xame kanta daga jikinsa ta juya masa baya trying her best bata fashe da kuka ba, Juyawa yayi a sanyaye ya fita kitchen din, Bata da wani kuxari ta karasa duk abinda take ta juye ruwan shayi a flask sannan ta fita da breakfast din gaba daya dining ta ajiye, kwance ta gansa kan 3 seater idonsa lumshe, ta karasa cikin parlorn tana kallon sa, Bata taba yarda cewar yara na kama da mahaifinsu hundred percent sai a kan kids dinta, the resemblance is just too obvious, har ta isa kusa da shi bata sani ba, ta durkusa gefensa tana ci gaba da kallonsa a sanyaye ta kamo hannunsa, lkci daya ya bude manyan idanuwansa ya mike xaune yana kallonta shi ma, wasu sabbin hawayen suka cika idonta ta sauke kanta kasa a hankli tace “Toh ni me yasa basu yi kama da ni ba?” Da mamaki ya dinga kallonta, ta mike xata bar wajen ya jawota jikinsa yana murmushi murya can kasa yace “The kids?” Ta gyada masa kai hawayen idonta suka xubo, ya rungume ta sosai ya lumshe ido yana shakar kamshinta yace “Next one’s xa su yi kama da ke in sha Allah” kwace kanta tayi ta hade rai tace “Next what?” Bude ido yayi, yyi dariya yace “Next kids mana” wani kallo tayi masa ta turo baki ta mike ta nufi dining ya bi ta da kallo yana dariya kasa kasa, sai da ta isa nan ta juyo tana kallonsa taga kallonta yake shi ma, a hankali tace “Breakfast…” ya mike yana murmushi ya iso dinning din, kanta a kasa tace “Do you still take coffee?” Yana kallonta yace “Sure…” kitchen ta wuce ya bi ta da ido ta dawo da coffee powder ta hada masa ta ajiye gabansa a hankali, sannan ta debar masa Irish da kwai ta ajiye masa tare da bread, ya wara ido yace “Duk ni kadai wife?” Bata ce komai ba ta hada nata shayin ta xauna tana sha, a hankali ta dago kai suka hada ido, kasa daina kallonsa tayi kamar yanda shi ma ya ke kallonta babu kiftawa, tasowa yayi ya dawo kusa da ita cikin sanyin murya yace “Billah Ina son ki Iman” ta sauke idonta bata ce komai ba. Karfe sha daya tana dakinta Aliyu ya shigo yace ta shirya xa su fita, lkci daya mood dinta ya canxa, dariya yayi don ya ma san dalilin hakan, ya karasa kusa da ita ya xauna gefenta yace “Baxan kai ki inda xa kiyi kuka yau ba, sai dai kiyi na farin ciki wife” ta turo baki kamar xata yi kuka tace “Ni ko daya bana so, am going no where…” ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace “xa ki so wannan in sha Allah ummu Shureim, I am giving you 100% assurance” a hankli tace “To xa mu dauko Shureim daga nan?” Kamar jiran tambayar yake ya girgixa kai da sauri yace “Nooo” da mamaki tace “Why?” Murmushi yayi yana kallon kwayar idonta yana shafa sajensa a hankali yace “Baxai bari in gwada maki yanda nake son ki ba anjima, he will be a barrier…” Wani kallo ta dinga masa tace “Ni dai yau yarona xai dawo, ba ruwana” Yar dariya yayi yace “Inaa sai na gama tabbatar maki da soyayyata anjima..” daga haka ya mike ya nufi kofa yace “Am waiting for you downstairs Iman, don nasan baxa ki shirya gabana ba” yana fadin haka ya juyo ya kalleta ya kashe mata ido ta bi sa da ido har ya fita, Aliyu yana ta xaune parlor yana jiran ta, message ya shigo wayarsa, dauka yayi ya bude yana duba address din da Dr Ayman ya turo masa, ajiye wayar yayi ya jinginar da kansa jikin kujera, shi kam har sannan ya kasa daina mamakin khadijah, he couldn’t believe it, bai taba xaton xata hakura ta sauko da wuri ba haka har ta kulasa duk da maganganun Anty khadijah, he never expect that from her, murmushi kawai yyi tunawa da yayi kilan yana cin albarkacin yaransu ne that she is seeing in him, but he will surely teach her to love him not because of the kids, sakkowa tayi stairs sanye da hijab har kasa babu abinda ta shafa fuskarta banda powder sai chappete a lips dinta amma har wani glowing take, she is just the definition of true beauty, ya mike yana murmushi a hankali yace “Kin yi kyau wife” sauke idonta tayi har ta iso parlorn, ya isa har gabanta ya duka yayi pecking lips dinta a hankali, ta hade rai tana goge bakin tace “Bana so” yana murmushi yace “Toh yi hakuri na bari” daga haka ya kama hannunta suka fita, sai da suka bar gidan a motarsa suka hau saman titi tana kallonsa a hankali tace “Ina xa mu je plss Aliyu?” Kallonta yayi na few seconds sannan ya dauke kai, murya can kasa yace “Yanxu baki jin kunyan kiran sunana Iman?” Ta hade rai tace “Toh me xan kira ka?” Ya langwabar da kai yace “Sai ki sakaya even because of Shureim, though nasan I don’t deserve that” jikinta ne yyi sanyi ta tuna yanda take kiransa seven years back, a hankali ta kallesa taga driving dinsa kawai yake ta sauke idonta tace “Toh xan ce maka Yayan Baby” murmushi kawai yayi bai ce mata komai ba kuma bai kalleta ba, bayan wani lkci yace “Ohk then” sun fi 10 mins babu wanda yace komai tayi breaking silence din, ba don shirun dake motar ba da ba lallai ma yaji abinda tace ba coz it’s very low, “Or Abu Shureim” abinda ta fada kenan sai kuma ta dauke kai kamar ba ita ta fada ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button