Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Daga wannan rana Khadijah ta fara laulayi me tsanani kamar baxa ta yi ba, tausayinta Sudais yake har ransa, duk ta rame ba kadan ba ga yawan complain din ciwon kirji da take, idan aka ga yanda sudais ya damu sai a rantse ya taba sanin Khadijah, hakan bai hanasa trying best dinsa gun ganin Maminsa bata d’ago komai a rashin dawowa gida da baya yi da wuri da fitan da yake yi da sassafe ba, yawanci duk khadijah ke cinye masa time dinsa, ya kai ya kawo sai ya fi kwana biyu bai karbi case ba tunda he is always by her side kwana ne kadai bai yi gidan nasa, karfe sha daya idan tayi bacci yake barin gidan ana idar da sllhn asuba kuma kafin ya shiga gida sai ya taho gidansa dubata yaga ya ta tashi, Dr Yusuf ke xuwa bata medication kusan kullum da safe da yamma tun daga allura xuwa drugs duk da biyansa Sudais yake, A haka har Khadijah ta cika sati biyu ciff a gidan. Da safe misalin karfe sha daya Sudais yaje can clinic gun Yusuf, bayan sun gaisa Yusuf ya tambayesa jikin khadijah, ya shafa kai yace “Toh ga ta can dai, am just tired Yusuf, wai why not baxa ka taimaka ka cire mata cikin nan ba frnd, am talking to you about this for the 3rd time don Allah ka cire mata ko nawa ka bukata xan baka, plss Yusuf” Yusuf ya girgixa kai yace “My reply will always be the same, I don’t abort pregnancies and I will not, nace ka kai ta wani asibitin ni dai baxan yi ba ka ki ganewa” Sudais ya marairaice yace “Nasan baka cire ciki amma ita wannan case dinta daban ne, she was raped… beside she is too young da ciki dubi fa yarinya ce karama, gashi sai wahala take sha ko don haka ka tausaya mata mana Yusuf” Yusuf dake rubuce rubucensa yace “Ae sai kuma ka yi Barrister” Sudais ya d’an hade rai yace “Haba Dr, ya kke son marainiyar tayi da yaron da xata haifa yanxu, ta ina xata fara rainonsa don ni dai ba dauwama xata yi tare da ni ba na har abada, har ynxu ina tunanin taimakon da xan bata ta tafi ta inganta rayuwarta but nt when she is this sick everyday, dubi fa jiddah gani take kamar na yaudareta ne, but ba hka bane idan aka yi auren ina xan sa ta, kasan it won’t make sense ina da gida in kama haya, dole Mami xata so sanin dalili, infact she will be suspicious, Yusuf don girman Allah ka rufa min asiri ka cire mata jaraban nn ta kama gabanta plsss” Yusuf ya tabe baki yace “xa ma ka gama dadin bakin ka” jin Sudais yyi shiru yana kallonsa ya ajiye pen din hannunsa yace “Sae in har in rubuta maka kaje can pharmacy ka siya nasan baxa ka rasa iya allura ba, duk sai kayi mata da kanka” ban da hararansa babu abinda Sudais yake, Yusuf yace “yes, or you buy her just drugs shkkn amma ni dai ba da hannu na ba” Sudais ya dake trying hard to hide his anger yace “Rubuta min” Takarda Yusuf ya jawo yyi rubuce rubucensa ya mika masa Sudais ya fixge ya nufi kofa Yusuf ya bi sa da kallo yana murmushi, Gida ya nufa bayan ya je garage din mota amso sakon Mami da ta aikesa tun safe, Xaune ya same Mami parlor, tun da ya shigo take kallonsa ganin ramar da yyi har ya karaso ya xauna kasa kusa da ita yace “Ina yini Mami” tace “Lafiya lau, sannu da xuwa” ajiye mata ledan hannunsa yyi yace “Ga sakon Mami” Bata ce komai ba ganin haka ya daga kai yana kallonta, tace “Aliyu ni ban fa gane nufin ka ba kayan akwatunan da kasa nayi jere da shi a daki ka hana a kai, toh Abbanku ya sa in xaunar da kai ka sanar da ni ko fasa auren kayi, wannan ai iskanci ne da kokarin mayar da mu kananun mutane da kake, idan ma da matsala ne ai sai ka yi mana bayani, babu mai maka dole tun da kai ka kawo yarinyar nan kana so ba wani ya kawo maka ita ba, yanxu ni ka gaya min ma’anar cewa da kayi kar a kai kayan a dakata” Sudais da har xufa ya fara keto masa ya shafa kai da kyar yace “Mami ba wai na fasa bane, kawai dai akwai matsala… ina son a min alfarmar ce masu su d’aga ko xuwa sabon shekara da xa mu shiga, idan kuma sun ga baxa su iya dagawa ba to gaskiya na hakura, Allah bata wanda ya fi alkhairi a kai na” Mami dake masa wani kallo tace “A daga a kan wani dalili?” Ya kasa dago kai yace “Kiyi hakuri Mami ayi min yanda nace pls, I just want to figure out the problem, Mami kin fa san aure ba don kwana daya ko ‘yan watanni ake yin sa ba na har abada ne, Mami I don’t want to make marriage mistake in my life don ni bani da burin xama da mace fiye da daya so I want to have the best marriage, ku taimaka ku ce masu a daga har lkcn, idan sun ga yyi masu tsayi to na hakura gaskiya I don’t want to cheat my self” Mami tace “Toh shi kenan, Allah sa mu dace, xan yi ma Abban naku bayani” Sudais ya dan yi murmushi a hankali yace “Nagode Mamina, xan je in dawo yanxu” Mami na kallonsa da kyau tace “Wllh ban gane fitar nan da kake kamar me talla ba kwanan nan sudais, da sassafe ka fice baka dawowa sai kusan sha daya, what’s wrong with you?” Ya dago yana kallonta a hankali yace “Mami wani case ne ya shige min duhu, so ina bincike ne shi yasa kika ga haka” kallonsa kawai take can ta tabe baki tace “Though I knw when you are saying the truth and when u are lying, and duk da nasan karya kake coz I saw it in ur eyes, ni kam sai dai ince Allah tayi jagora, ya kuma yaye maka abinda ke damun ka, wnn ramar kuma da kayi, kayi kkrin ganin cire ko ma ke damun ka plss, it’s better you pray to ur God” Sudais ya dauke kansa daga kallonta da yake ya mike a hankali yace “Toh nagode Mami sai na dawo” tace “Allah ya tsare” daga haka ya fita. Pharmacy ya tsaya ya siya magungunan da Yusuf yyi masa prescribing sannan ya siya fruits kafin ya wuce gidansa, har wani faduwa gabansa ya shiga yi bayan yyi parking cos bai son xuwa ya ga khadijah in pain, ya dai dake ya shiga gidan, kwance ya sameta kamar ko da yaushe a daki idonta a rufe, yawanci duk haka yake xuwa ya sameta kuma ba bacci take ba, yana tsaye a hankali yace “Amira” ta bude idanuwanta a hankali tana kallonsa, yace “Ya jikin” kai ta gyada masa ya durkusa yana bude ledan apples da banana da ya siyo mata yace “Ga Apple nan” ta girgixa kai da sauri tace “Anjima” yace “Toh kin yi sllh?” Gyada masa kai tayi, ya d’an yi shiru sai kuma ya mike yace “Toh tashi ga magani na kawo maki ki sha, you feel more better idan kin sha” kamar xata yi kuka tace “Xan yi amai ni nafi son allura” kallonta ya tsaya yi, can yace “Baxa ki yi ba kawai guda uku ne fa” daga haka ya fiddo magungunan a leda sai kuma ya fita xuwa ya debo mata ruwa, har ya dawo tana kwance ya d’an hade rai yace “Toh tashi mana” mikewa tayi da kyar ya bude maganin gudu uku kamar yanda yace ya bata a hannu ya mika mata ruwa a cup, ta karba tana bata fuska xata yi kuka, ya daure fuska yace “Ki sha Ki ban cup yanxun nan” wayarsa ne ya fara ring ya ciro a aljihu tana ganin haka ta watsa maganin a bayanta tayi saurin kai ruwan baki tana sha dai dai lkcn da ya maido dubansa kanta, da sauri yace “Kin sha?” Ta mika masa cup din tana yamutse fuska, ajiyar xuciya ya sauke a hankali, kokarin amai ta shiga yi da sauri yace “Noooo, don’t ko in bata maki rai” ta koma baya a hankali kar ya xagayo ya ga maganin ta jingina da gado yace “Good girl” daga haka ya fita ya kira Yusuf dake kiransa, da sauri ta kwashe magungunan ta watsar a bayan gado tana turo baki, Sudais ya hade rai bayan ya kai wayar kunne yace “Ya aka yi?” Yusuf yace “Ya ta sha?” Sudais yace “It’s nt ur concern” dariya Yusuf yyi yace “In dai ka tabbatar ta sha don’t leave her alone kar ka kashe yar mutane nan da few hours xata samu miscarriage din in dai magungunan da na rubuta ka siya ka bata” Sudais yace “Ohk” daga haka ya katse wayar ya xauna parlor. Haka Sudais yyi ta xama gidan har magrib amma shiru kke ji, ya duba ta yyi sau ashirin kafin magrib amma banda bacci bbu abinda take hankli kwance, yana fitowa masallaci ya kira Yusuf yace “Kai ni da ina ta xaune gidan har yanxu shiru” Yusuf yace “Bata sha ba toh” Sudais yace “Ya xaka ce haka, a gabana fa ta sha ni ma na bata maganin da ruwa” Yusuf yyi shiru jin haka, sudais yyi tsaki ya katse wayar. har washegari shiru kake ji bbu alamar miscarriage gashi Yusuf yace kar ya kara bata wani, duk ran sudais ya baci, da yammacin washegari Yusuf ya xo gidan, Magungunan ya dauka yana ta kallonsu kamar yanda Sudais ke hararansa shi kuma, can ya balli wasu ya mika ma sudais yace “Bata ta sha” Khadijah dake kwance tana kallonsu kamar xata yi kuka tace “Ni maganin wani iri yake min bana so plss” Sudais ya daure fuska yace “Karba my friend” mikewa tayi hawaye ya cika idonta ta amshi maganin ya mika mata ruwa, daga shi har Yusuf suka kafeta da ido, ta daga gefen Hijab din jikinta tana share hawayen idonta hakan ya bata daman sakin maganin gaba daya a Hijab din cikin dubara sai kuma tayi saurin dage kafarta kamar xata daura kanta bisa kneel dinta, har lkcn kuma hannunta na dunkule kamar tana rike da drugs din, Yusuf yace “Baxa ki sha ba?” Bude baki tayi ta yi kamar ta watsa su ciki sannan tayi saurin xuba ruwa bakin ta tana yamutse fuska har da kokarin amai, da sauri Sudais yace “Don’t try that” ta hade kai da gwiwa suna ta tsaye suna kallonta har ta dago a hankali, Yusuf ya juya ya fita sudais ya bi bayansa, Yusuf yace “Toh sai kayi xaman gadi” daga haka ya bar gidan, Sudais na ta xaune har dare amma shiru, mamaki ya dinga yi anya ba yaudararsa Yusuf yyi ba, a fusace yaje har gida ya samesa don jin me yasa yyi masa haka, Yusuf dake dakinsa kwance yace “Toh ka kai ma wani likitan takardar maganin ka tambayesa na menene, I think that’s all I can tell you” Bayan kwana biyu sudais ya sake komawa Yusuf office da rana, da damuwa yace “Dr ko xaka canxa wani method din ne, wllh I don’t have rest of mind, am afraid kar Mami ta san abinda nake yi, gashi in few weeks time xan je UK, to ya xan yi da yar mutane?” Yusuf yayi dariya yace “Tunda taimakonta kake son yi ka tafi da ita mana” Yusuf ya watsa masa kallo yace “Ko matata ce ke wannan laulayin ina xa ni da ita balle wannan” Yusuf yace “In baka shawara Barrister?” Sudais yyi shiru yana kallonsa, Yusuf ya mike tsaye yace “Wllh ka kyale mata cikinta tunda ka ga haka, Allah kadai yasan me xata haifa, there is power in the baby, banda haka ban ga dalilin da xai sa ta sha drugs din nan har sau biyu ba amma shiru ake ji, just let her pls and idan son samu ne ka taho da ita clinic ko gobe da safe ayi mata scan cos this is almost a miracle” kasa cewa komai Sudais yyi can ya juya ya fita. Washegari kamar yarda Yusuf yace haka Sudais ya sa khadijah ta shirya suka je asibiti don a mata scan, gaba daya jikinsa yyi mugun sanyi bayan result ya fito, shi kadai da Yusuf ne a office din Yusuf din, ita kuma tana reception, Yusuf yace “You see, da haka xaka sa ayi wasting bayin Allahn da basu san komai ba, 2 souls barrister” Sudais bai iya yace komai ba. A hakan dai Sudais ya ci gaba da ba Khadijah kulawa yanda ya kamata, bai rage ta da komai ba a gidan sa, damuwarsa daya yanda ta ki kwantar da hankali har lkcn ga yawan koke koke, idan ya sa ta gaba ta fadi me ke sa ta kuka sai ta ce masa ita bata da kowa yanxu, hakan nasa jikinsa yyi sanyi, sannan hakan ke kara masa kwarin gwiwan ci gaba da taimaka mata, ganin saura yan kwanaki ya fita kasar ya sa ya shiga tunanin wanda xai bar ta da a gidan, idea ne ya xo masa yasa aka nema masa wata dattijuwar da xa su xauna tare da Khadijah a gidan nasa, hakan aka yi bayan matar da baxata haura shekaru hamsin ba ta amince duk wata xai dinga bata dubu arba’in. A yau Khadijah na daki xaune kasan carpet tana shan kunun da dattijuwar da ta dama mata, dattijuwar matar da a ranan tayi kwana uku a gidan duk tunaninta Khadijah matar Sudais ce, su biyu ne dakin Sudais yayi sallama bakin kofa, ta mike da sauri ta iso kofa ta bude tana cewa “Sannu da xuwa yallabai” Gaisheta yyi ta amsa cike da jin dadin yanda yake girmamata sannan ta fita, Sudais ya karasa cikin dakin yana kallon khadijah, wani mugun haske tayi da kyau sai kyalli take, lips dinta yyi pink colour, dauke kai yyi ya isa gefen gado ya xauna, a hankali tace “Ina yini?” Yace “Lafiya lau, ya jiki?” Tace “Da sauki” shiru yyi na wasu yan mintuna kafin yace “Am traveling Amira” ta dago tana kallonsa, ya gyada kai yace “Yeah, gobe xan tafi” sauke idonta kasa tayi, lkci daya hawaye ya kawo idonta cikin sanyin murya tace “Tafiya xaka yi ba bar ni” ya tsura mata ido kafin yyi murmushi yace “Aiki xan tafi yi can, in sha Allah xan dawo when am done” ta kallesa hawayen idonta ya sakko tace “Toh yaushe ne xaka gama” ya wara Manyan idonsa yace “Nima ban sani ba, but da na gama xan dawo ai” kai kawai ta gyada masa amma kana ganinta kasan jikinta yyi sanyi, murmushi ya sake yi yace “Ba ga mama ba xata dinga kula da ke xan bar mata kudi ta dinga siya maki duk abinda kike so, just promise me baxa ki dinga damuwa ba that’s all” murya can kasa tace “I promise, amma yaushe xaka dawo?” Dariya ta basa ganin ta yi tambayar daxu yace “Duk sanda kika samu lafiya kika fara cin abinci sosai sannan bakya damuwa xan dawo” xaro ido tayi tana kallonsa, yace “Yes” murmushi tayi ta sunkuyar da kanta, sae ranan ya fara ganin murmushinta ya dinga kallonta ganin xata dago kanta yyi saurin dauke kai, tana wasa da dogayen yatsun ta tace “Toh naji” yace “Yauwa ko ke fa” wayarsa daya ya Ciro ya mika mata yace “Xan dinga kiran ki in sha Allah” karba tayi a hankali tace “Toh” yace “to tashi ki raka ni” Ba musu ta mike shi ma ya tashi ya nufi kofa sannan ta bi bayansa, a parlor ya tsaya yyi sallama da Dattijuwar ya kuma sanar da ita xai yi tafiya ta dinga masa addu’ar Allah ya tsare yace “Ameen Ngd mama, don Allah ki dinga sa mata ido bata son cin abinci” tace “In sha Allah kar ka samu damuwa” Dubu hamsin ya ba matar ta dinga siya ma khadijah duk abinda ta bukata, ya kuma sanar da ita komai babu gidan Dr Yusuf xai kawo masu, daga haka ya juya yana kallon khadijah dake ta kokarin ganin bata yi kuka ba yace “Toh mu je” har bakin mota ta rakasa kanta a kasa ya kara mata sallama ta kasa daurewa ta fara kuka, duk jikinsa yyi sanyi, a hankali yace “Look Amira ba dadewa xan yi xan dawo ba, ki daina kuka pls” kai ta gyada masa cikin sanyin murya tace “Toh Allah ya tsare hanya” daga haka ta juya ta koma cikin gida ya bi ta da ido. Kamar kar Sudais ya bar kasar Khadijah ta fara samun lafiya sosai dattijuwar me kirki komai take so shi take mata kafin wani lkci duk babu ramar da tayi sai cikinta da ya fara fitowa, kullum a rana sudais xai kirata kusan sau biyar just to check if she is fine, idan bai kirata ba kuwa ta dinga damuwa kenan, a haka har watanni suka shude.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button