Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

5 months later.

Yau tun da Khadijah ta tashi take ta murna ta rasa dalili, har hirarta ya fi na ko wani rana yawa har da dariyarta wanda da wuya ka ga tayi dariya, Dattijuwar mama suwaiba da take kira da Anty har ta lura da hakan tace “Wannan murnar yayi yawa khadijah ko dai mai gidan ne xai dawo yau” Khadijah dake hada fruits salad xata sha ta daga kai tana kallon mama suwaiba tayi shiru don kuwa gaskiya ne jiya da daddare da suka yi waya da Sudais yace mata yau xai dawo, murmushi tayi ta sunkuyar da kanta ta ci gaba da abinda take a hankali, mama suwaiba tace “Toh gwara a tashi a san me xa a girka masa, ki fadi duk abinda kika San yafi so sai in shirya in tafi kasuwa yanxu” Khadijah tayi shiru don har lkcn bata san komai game da Sudais ba balle ta san abinda ya fi so da wanda bai so, hakan yasa jikinta yyi sanyi sosai. A cikin watanni biyar din nan khadijah ta warware jikinta yyi kwari, babu abinda bata ci har da wanda bata ci a da can, wato wake, taliya kai har da tuwo da miyar kuka, wani kyau na musamman tayi don hatta fatar jikinta har wani glittering yake yayi taushi, yanxu kam cikinta ya fito sosai don sai ayi tunanin at anytime xata iya haihuwa don da kyar take yin komai nan ko watannin cikin bakwai, tausayi take ba mama suwaiba ganin yarinya ce sosai wa ya sani ko xata iya haihuwa da kanta ma, hakan yasa in dai ta fita cefane ko siyo wani abun bata rabo da dawowa da magunguna irin na gargajiya da tasan mai ciki na bukata, duk ranakun alhamis kuma tare da mama suwaiba suke xuwa can clinic dinsu Yusuf domin Antenatal a bisa umarnin sudais, damuwar Khadijah daya a lkcn ummarta don ko cikin dake jikinta baya damunta ta kuma rasa dalili, gaba daya tayi kokarin ganin ta mance ta taba rayuwa gidansu Aliyu, amma duk sanda cikinta yayi motsi sai ta tuna shi Aliyun, duk wannan difficulties na rayuwa da ta shiga ko sau daya bata taba jin haushin Aliyu ba kuma har ranta take jin ta yafe masa a lkcn… ko don tana tare da yarinta har sannan ne oho. Khadijah ta kasa hakuri ganin har yamma bata ga sudais ba alhalin yace mata in sha Allah yau yana Nigerian duk jikinta yayi sanyi ta tafi daki ta kwanta, Mama suwaiba kuma ta ki hakura tana ta girke girke a kitchen ita kadai. Sudais na sauka taxin da ya kawo sa har kofar gida ya shiga gidan yana rike da daya daga travelling bag dinsa guda uku da mai taxin ya dire masa a bakin gate, kai kana ganinsa kasan daga turai yake don wani fresh na musamman yyi da haske sai dai ya rame sai idanuwa da hancinsa da suka fito, sosai ya rage bak’in gashin kansa, yyi murmushi ya na amsa gaisuwar da mai gadi ke masa da fara’a yana masa sannu da dawowa sannan yace “Ka shigo min da sauran kayana bilyamin” tun a bakin kofa kanninsa suka rungumesa ko wacce na murnar dawowarsa bayan kusan watanni biyar, Mami dake parlor da Anty Maryam ma sai murmushi suke, lkci daya murmushin Sudais yyi fading ganin Jiddah da yayi xaune parlorn, ya karaso a sanyaye ya duka kasa ya gaida mami ta amsa tana murmushi tace “Sannu da xuwa Aliyu ya hanya?” Yace “Alhmdllh Mami, fatan mun same ku lafiya?” Tace “Alhmdllh” gaisawa suka yi da Anty Maryam sannan ya kalli jiddah yana kirkiran murmushi ta sunkuyar da kai tace “Sannu da xuwa ya hanya?” Yace “Alhmdllh mun same ku lafiya?” Tace “Sure” Rabi’ah da Humairah suka dau bags dinsa xa su kai daki yace “Noo don’t worry sisters wancan kadai xaku dauka ku bar wa ennan, xan d’an fita yanxu” da mamaki Mami tace “Ka fita kaje ina daga dawowa, idan ma fitan xaka yi ina xaka da jaka kuma?” Ya sunkuyar da kai yace “Sakon wani abokina ne xan kai gidansu Mami” Mami tace “Ohk, to amma sai ka huta ka ci abinci koh?” D’an shiru yyi sai kuma yace “Mami baxan dade ba xan dawo yanxu” daga haka yasa kanninsa suka dau jakunkunan suka kai masa bakin motarsa sanin ko baya nan ana amfani da motar, ya mike yace “Toh sai na dawo Mami” tace “Toh don Allah kar ka jima ka dawo ka ci abinci ka huta” yace “In sha Allah” yana barin gidan bayan ya hau titi ya dau wayarsa ya shiga kiran khadijah, Khadijah dake kwance har lkcn a daki ta mike da sauri kamar jira take jin ring din wayar ta jawo ganin Sudais ne ta daga ta kai kunne, daga daya bangaren yyi sallama yace “Amira” turo baki tayi tace “Uhn” yace “How are you” a hankali tace “Fine baka dawo ba kuma” d’an murmushi yyi yace “I postponed the trip xuwa next month in sha Allah” wani irin faduwa gabanta yyi da har sai da ta ji a kirjinta da ya mata sauki kwana biyu sbda magungunan da Yusuf ke bata, hawaye ne ya shiga sakkowa idonta, yace “Hello are you there?” Kasa amsawa tayi ya dinga hello ta katse wayar ta hade kai da gado ta fara rera kuka, sake kiranta yyi ta ki dauka har ya katse ya kara kira, sai a snn ta dauka ta kai kunne taki cewa komai, murya can kasa yace “Amira” ta fashe masa da kuka a hankali, wara ido yyi hade da murmushi yace “Har da kuka kuma?” Ta ki cewa komai, murya can kasa yace “Cry no more, tunda kina son ganina kawai fito gate ki tsaya ni kuma xan taso daga UK yanxu, har kofar gida jirgin xai ajiye ni” mikewa tayi xaune da sauri tace “Don Allah ka bari, ka dawo pls?” yace “Da gaske fa just wait me outside xa ki ganni yanxun nan” katse wayar tayi ta tashi da sauri ta dau Hijab har Kasa ta sa sannan ta fita dakin, Ganin xata fita waje Mama suwaiba da fitowarta kitchen kenan tace “Ya iso halan” Khadijah bata iya ta ce komai ba ta kirkiri murmushi ta fita, a hankali take tafiyar har ta isa gate ta tsaya gabanta na bugawa, tsaye ta ga motarsa bakin gate din suna hada ido ya bude motar ya fito yana murmushi, tsabar farin ciki ta kasa cewa komai amma kana ganin ta kasan she is just happy, ita dai tasan yau da ace mace ce Sudais da ta tafi da gudu ta rungumesa, ya wara mata ido ganin kallon da take masa yace “Toh ko dai in koma tunda kallona xa ki tsaya yi” tahowa tayi ta tsaya gabansa ta sunkuyar da kai tana murmushi, murmushin yayi shi ma murya can kasa yace “How are you Amira” ta kasa dago kai cikin sanyin murya tace “Am fyn, sannu da dawowa” yace “Sannu, ya babies dinmu” dagowa tayi ta kallesa da sauri sai kuma ta juya masa baya, dariya yayi yana kallonta, tayi murmushi tana jan hannunta, yace “Toh mu shiga” tafiya ta fara yi ya bi bayanta bayan ya rufe motar har suka shigo parlor. Xaunawa yayi parlorn suna gaisawa da mama suwaiba dake tayi masa sannu da xuwa, khadijah ma ta xauna kasan parlorn tana kallonsa ko kiftawa bbu, mama suwaiba ta koma kitchen ya maida dubansa kan Khadijah, sauke idonta tayi kasa da sauri, yace “Are you now happy” murmushi tayi tana gyada kai a hankali shi ma yyi murmushin yana kallonta, Kirar ta Mama Suwaiba tayi ta mike ta nufi kitchen ya bi ta da ido, Mama suwaiba tace “Toh ke haka ake yi, sai ki je bayi ki hada masa ruwan wanka, idan kuma abinci xai fara ci sai ki kai masa daki” murmushi khadijah tayi bata ce komai ba, mama suwaiba tace “Toh kin yi shiru kuma” a hankali khadijah tace “Toh bari in tambayesa” daga haka ta juya ta koma parlor, Wayarsa yake dannawa ta duka gefensa ya kalleta yace “Xauna kujera mana, you are stressing ur self and the babies” sauke idonta tayi kasa tace “Dama Anty ce ta ce in tambayeka ko xaka ci abinci a kai maka daki” shiru yyi na wani lkci kafin yace “She is thinking something different, and Mamina ta min abinci a can gida but… Ohk toh kai abincin daki” Tashi Khadijah tayi ta koma kitchen ta karbi abincin da Mama suwaiba ta hada a tray ta wuce can bedroom da shi, Sudais ya mike ya bi bayanta, karban abincin yyi a hannunta ya ajiye kan rug sannan ya xauna yace “Ke kin ci abincin” tace “Na ci daxu” yace “Daxu daban, yanxu daban, so xauna mu ci” dafa gado tayi xata xauna a kasa yace “No ki xauna saman gado” xaunawa tayi gefen gado ya debi abincin a plate ya sa spoon sannan ya mika mata ta amsa a hankali tace “Nagode” ya debi kadan a wani plate din dai dai nan wayarsa yyi ring dubawa yyi da sauri ya ga Mami ce, ya d’an bude ido sannan ya daga, daga daya bangaren Mami tace “Wai daga dawowa ina ka tafi haka Aliyu? Are you even okay” a hankali yace “Gani nan tahowa Mami am sorry” katse wayarta tayi, ya ajiye wayar yana kallon abincin, samun kansa yyi da Kasa cin abincin, ya rufe yace “Amira xan je gida Mami na jirana idan kin cinye wannan sai ki kara da nawa” Bata ce komai ba sai wasa da cokalin hannunta take, ya mike yace “Kilan xan xo gobe da safe, take care of ur self” daga haka ya juya ya fita, hawaye ne ya cika idonta ta rasa dalili abincin duk ya fita ranta ta kasa ci ta ajiye tana goge hawayen dake xubo mata, Sudais na fita ya tuna bai shiga da kayan da ya taho mata da su daga UK ba, ganin xai kara bata lkci kawai yyi deciding ya bar sa a motar sai gobe idan ya xo. Ko da ya koma gida kawai yana cin abincin da Mami tayi masa ne amma gaba daya hankalinsa na kan Khadijah don bai san ko ta ci abincin da ya debar mata ko bata ci ba, Mami dake xaune ta sa shi gaba da jira har ya gama cin abincin sannan tace “Kun yi waya da jiddah xaka dawo yau ne?” Girgixa kai yyi duk da faduwar da gabansa yyi a hankali yace “Aa mun ma kwana biyu ba mu yi magana ba, fushi take ai da ni” Mami tace “Toh wasa wasa gashi har watanni kusan shidda da kace a daga biki yyi, yanxu kuma ya ake ci” kasa kallonta yayi ya fara kame kamen rufe warmers din abinci, strictly tace “Magana nake ma ka Aliyu” da kyar ya dago ya kalleta yace “Toh Mami a sa bikin nan da wata daya xuwa biyu in sha Allah” wani kallo ta watsa masa tace “Me sati biyu ko uku yayi da har sai an kai wata biyu kuma?” Ya shafa kai yace “Dai dai wannan lkcn xan koma UK kuma xan jima sosai kafin in dawo kinga kawai ana bikin a lkcn sai mu tafi tare da ita” Mami tace “Allah ya kai mu, xan ma Abbanku bayani” yace “Nagode Mami” daga haka ya mike yace mata xai kwanta ya wuce bedroom dinsa. Yana shiga dakinsa khadijah ya kira, tana dagawa yace “Kin gama cin abincin?” Turo baki tayi tace “Na koshi” yace “Baki ci ba kenan?” Shiru tayi bata ce komai ba, yace “Me kike yanxu?” Tace “Na kwanta” yace “Tashi ki je ki dau abincin ki ci idan ba haka ba baxa ki ganni gidan nan ba for plenty days” tashi tayi xaune da sauri tace “Ni ban ce baxan ci ba” yace “Toh je ki ci” ta mike da kyar tace “Toh” yace “Idan kin gama ki kirani” gyada masa kai tayi kamar yana ganinta ya katse wayar. Sosai ta ci abincin ta hada har da wanda ya dibar ma kansa, tana gama ci ta dau wayar ta kirasa, sai da ya kusa katsewa ya daga, jin muryarsa tace “Bacci kake” a hankali yace “Yea, kin gama cin abincin?” Tace “ehh na cinye” yace “Good Mami” murmushi tayi tace “Toh kayi baccin, byee” murmushin shi ma yyi ya katse wayar. Xuwan Yusuf gidansu da daddare ne saving grace dinsa don da shi da fita kuma sai gobe, bayan Yusuf ya gaisa da Mami suka tafi dakin Sudais yana tambayar sa ko yayi ciwo a UK ne don ya rame sosai, bayan kusan minti talatin Yusuf yace xai tafi suka fito tare da sudais da yace ma Mami xai rakasa, sai da suka shiga mota Yusuf yace “Kaje ka duba mai cikin ka?” Sudais ya hade rai yace “Mai cikina kuma” dariya Yusuf yyi yace “Toh ai kusan baka da banbanci da uban yaran, kai ma uba kake a gare su kama fi sa xama masu uba kan ubansu” tsaki Sudais yyi bai ce komai ba, Yusuf yace “But don Allah Sudais da yau ko watarana xaka ga uban unborn babies din nan me xaka masa?” Sudais yyi wani murmushi da kamar baxai ce komai ba sai kuma yace “I won’t even look at him twice yaran da xata haifa sun ishesa” Yusuf yace “What if ya xo wataran yayi claiming yaran fa?” Wani kallo Sudais yyi masa baki bude, can yyi wani dariya yace “Wllh wllh I will sue him, sai na sa yyi shekaru da dama a gidan yari” Yusuf dake driving ya wara ido yace “Tohhh, kenan yaran ka ne ba nasa ba” Yusuf na dariya ya kare maganar, Sudais yyi banxa da shi, Yusuf yace “Toh why not bayan ta haihu ka aureta kawai Sudais” juyawa Sudais yyi yana kallonsa da wani expression, can ya dake yace “Ko saboda me?” Yusuf yyi murmushi yace “Saboda ka ji dadin ci gaba da kula da ita da yaran da xata Haifa kwanan nan, kasan a yanxu kai ne ubanta kai ne uwarta, i mean kai ne gatan ta, don haka sai ka ci gaba da xama gatan nata har karshen rayuwarta, nan da shekaru biyu kai ma ta haifa maka naka yan biyun ba na wani ba”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button