Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Sudais na dawowa dakin ya dinga kallonta har ya iso kusa da ita yace “Me yaran suka maki da kike cewa baki son su Amira” kin cewa komai tayi, ya ja kujera ya xauna yyi shiru, bayan kusan minti goma wayarsa ya fara ring dauka yyi ya duba yaga Mami ce, yau ta kirasa yyi sau hudu duk bai dauka ba, ya mike yana kallon khadijah da ta lumshe idonta yace “Mama xata dawo yanxu, ni xan je gida Mami na ta kirana, gobe da safe xan xo kin ji?” Bude ido tayi tana kallonsa yace “Be strong, kuma kar ki sake kuka plss” gyada masa kai kawai tayi ya juya ya fita. Bayan fitarsa da yan mintuna mama suwaiba ta shigo, sannu ta dinga yi mata, ta xauna kusa da ita tace “Kin ma ga yaran naki kuwa Amira” Khadijah ta hade rai tace “Ehh” daga haka ta rufe idonta, ana yin isha mama suwaiba tayi sallah a nan ward din da bayan ta shimfida dankwalinta a kasa, bude kofar ward din aka yi nurses biyu suka shigo da babies din Khadijah ta rufe ido da sauri, kan gadon jariran dake kusa da na khadijah suka kwantar da su, daya daga nurse din na kallon Mama suwaiba da ta mike ganin yaran tace “Xa a iya ba su nono yanxu idan suka bukaci haka” daya nurse din na nuna mata babyn kusa da ita tace “Wannan shine Hasan, na kusa da shi kuma Hussain” Mama suwaiba tace “Maa sha Allah, Allah ya raya mana su” nurses din suka amsa da amin sannan suka fita, mama suwaiba sai kallon kyawawan fararen yaran take tana murmushi sai dai abinda ke daure mata kai daga Sudais har Khadijah babu wanda taga yaran suka biyo, a ranta tace “Ikon Allah, to ko wa suka biyo su kuma maa sha Allah” kallon khadijah tayi da ta ki bude ido har lkcn, tausayinta ta dinga ji don idan akwai abinda ta tsana shine ayi ma mace operation. Karfe sha daya da wani abu mama suwaiba ta kwanta a spare bed dake Dakin, har ta fara bacci taji kukan jariri, ta bude ido da sauri taga daya ne ke motsi, ta Mike ta daukesa tana kallon khadijah, Bata san Khadijah na jin yaron ba sai dai idonta a rufe yake har sannan, Mama suwaiba da a tunaninta bacci take ta rungume yaron ta xauna, haka mama suwaiba ta dinga lallaba su tana basu ruwa a feeder ganin yunwa suke ji har Washegari da safe. Karfe tara saura sudais ya shigo ward din,sanye yake da farar shirt da black jean yayi kyau ba kadan ba, direct gun babies dake cikin cot dinsu bayan an masu wanka ya nufa, ya dau daya ya lumshe ido ya daura lips dinsa a soft cheek din babyn, juyawa yayi ya kalli khadijah dake bacci, jikinsa yyi sanyi don da alama mama suwaiba ta je gida dauko abu, daga ita sai yaran ne a ward din, nobody to stay with them, banda tsotson baki bbu abinda yaron dake hannunsa yake alamar yunwa ya kalli d’an uwansa shi ma yaga haka yake da bakin, yana ta tsaye dakin bai tashi Khadijah ba mama suwaiba ta shigo bayan sun gaisa yake tambayarta ko Khadijah ta fara basu abinci ne, Mama suwaiba tace “Aa bata basu ba da nayi mata magana daxu ce min tayi cikin ta na ciwo har na fita na kira wata nurse, tun jiya ruwa kawai nake ba su” Sudais bai ce komai ba ya xauna saman kujera, bayan wani lkci yace “Toh ita ta fara cin abinci ne?” Mama suwaiba tace “A’a ga shi nan dai kunu ma na je gida na dama mata, cewa likitan yyi shi kadai xata iya sha anjima, toh kafin ta tashi shine naje nayo” yace “Toh sannu mama” ya d’an jima a dakin kafin ya bar asibitin kuma har lkcn khadijah bata tashi ba. Wasa wasa yau kwanansu uku a asibiti amma khadijah taki ba yaran nono, da farko cewa take cikinta na mata ciwo baxata iya ba sudais ya siyo masu madara na jarirai mama suwaiba na basu, har abun ya fara daure ma mama suwaiba kai don har sannan khadijah taki daukan yaran ta, tunda tayi kokarin bata su sau daya ta ki amsan su ta kuma ga kamar ranta ya bace bata sake bata su ba. Satinsu daya da kwana daya aka sallamesu asibitin bayan Sudais ya biya bill din, duk yaran na hannun mama suwaiba don khadijah bata amshi ko daya ba, ya bude motar bayan sun isa gida ya amshi dayan yaron hannun Mama suwaiba, ta fito rike da dayan ta nufi cikin gida, kallon khadijah yyi da ta fito ita ma ya mika mata yaron, dauke kai tayi ta bar wajen da sauri tace “Ni dai baxan iya ba” Wani kallo ya mata da mamaki yace “Kee” ta juyo tana kallonsa, mika mata yaron yyi fuskarsa daure yace “Karbesa” kamar xata yi kuka tace “Xai iya faduwa pa” yace “Ya fadi” ganin yanda ya tsare ta da ido ta karbi yaron hawaye har ya kawo idonta ya yi gaba ya bar ta gun tsaye, a hankali ta bi bayansa ba tare da ta bari ta kalli yaron hannunta ba, sudais ya karbi yaron hannun mama suwaiba ya wuce bedroom da shi khadijah ta bi bayansa, gefen gado ta xauna ta ajiye yaron kan gadon, yana kallonta yace “Basu abinci yanxu” da sauri tace “Ai naga sun sha madara fa, ni…..” Katse ta yayi yace “Baki son yaran nan koh Amira?” Ta kallesa ta gyada kai a hankali kamar xata yi kuka, yana mata wani kallo yace “Dama kin san baxa ki so su ba kika yarda kika haifo su duniya, me yasa baki amince an raba ki da su tun a ciki ba?” Cikin rawar murya tace “Toh ai babu kyau” yace “Ohk…. abinda kike masu yanxu da kyau kenan” shiru ta yi hawaye na sakko mata, yace “Kin san Allah idan baki basu abincin su ba am leaving here now, kuma wallahi babu ruwana da ke, are you this wicked?” da sauri tace “Kayi hakuri xan basu” tana magana hawaye na xuba idonta don ita har ranta da gaske bata son yaran, Sudais yace “Toh ba su yanxu” tana share hawayen idonta ta fara bude zip din rigarta xata sauke rigar yayi saurin dakatar da ita “Kee haka aka ce maki ake yi?” Kamar xata yi kuka tace “Toh ai ban iya ba” juyawa yyi ya fita sai gashi tare da mama suwaiba, yana tsaye ta gwada mata yanda xata yi tana dariya sudais ya juya ya bar masu dakin, har da kukanta ita wai xafi take ji, Mama suwaiba ta dinga lallaba ta don ita ma tausayin yaran take ganin basu samu gatan shan nonon uwarsu ba tun da suka fito duniya, da kyar ta amince ta ba dayan ma, a ranta kuwa tasan shine farkon shan su kuma shine karshe don ita dai baxata iya ba. Kwanansu biyu da dawowa daga asibiti Sudais ya shigo dakin da Khadijah take da safe, xuwan sa kenan gidan, farar Gezna ce jikinsa dake ta kyalli, waya ne kare kunnensa ya shigo dakin yana magana amma can kasa kasa, ya nufi gun babies dake kwance yana kallonsu kamar yanda Khadijah da ke tsaye gaban madubi ke ta kallonsa tun shigowar sa, Sudais is just the real definition of handsome, duk da wayar da yake gaba daya hankalinsa na kan yaran dake ta tsotson baki yana murmushi, xuwa jikin khadijah yyi kwari sosai don har aikin ya gama warkewa, sosai kirjinta suka ciko har ciwo suke mata amma taki ba ma yara abinci, yanxun ma mama suwaiba ce ta shigo da su ta kwantar ko xata tausaya masu ta basu nono, Sudais ya mayar da wayarsa aljihunsa ya juya ya kalleta tayi saurin dauke kanta, ya xauna gefen gadon yace “I know baki abinci ba yau” ba tare da ta kallesa ba tace “Na basu ka tambayi Anty” bai ce komai ba, bayan wasu mintuna yace “Wani sunan za a sa ma babies din?” Still taki kallon inda yake tace “Nima ban sani ba” yace “Baki sani ba kuma?” Tace “Ko wanne ma ka sa masu” yace “A’a ke xaki xaba da kanki ba yaran ki bane” kin cewa komai tayi, yace “Am talking to you Amira, kuma akwai inda xa ni” ta langwabar da kai a hankali tace “Toh Muhammad da….” Sai kuma tayi shiru, yace “Da wa?” A hankali ta saci kallonsa tace “Kai” ya buda ido sosai yace “Ni kuma?” Tace “Ehh, ur name” murmushin sa mai kyau yyi yace “Aa ki xabi wani sunan dai Amira” hawaye ya kawo idonta tace “Ni kai nake so a sa” Yace “Aliyu kike nufi?” Ta gyada masa kai, wani murnushin ya sake yi yace “Sunan mahaifinsa dai kenan” da sauri khadijah da gabanta yyi mugun faduwa tace “Noo, Brr Aliyu Sudais nake nufi not Dr Aliyu Turab” Shiru Sudais yyi yana kallonta, mikewa yayi bai sake cewa komai ba ya fita yana murmushi. Raguna biyu sudais ya yanka ma ‘yan biyun, Hasan aka sa ma Muhammad, Hussain kuma Aliyu, kusan duk sadaka yyi da daya ragon ya bar ma khadijah daya mama suwaiba ta gyara mata, ita dai mama suwaiba kanta ya gama daurewa taga babu me xuwa barka tun dawowarsu, shiru kuma ba xancen taron suna gashi har an gyara rago, Yusuf kadai ya xo gidan a ranan, nan xuciyarta ya fara wani tunanin anya wa en nan ma’aurata ne ma kuwa, don ga dukkan alama wnn dai ba aure bane domin kuwa tun xuwanta bata taba ganin Sudais ya kwana gidan ba, amma meye tsakaninsu? Sudais na bedroom dinsa a can gidan Abbansa da yamma, shigowarsa gidan kenan tun safe da ya fita, Anty Maryam ce ta shigo dakin ya juya yana kallonta sannan ya gaisheta ta amsa da murmushi tace “Kasan an kai ma jiddah kaya kuwa Aliyu, and sati biyu aka sa bikin from today” kasa ce mata komai yyi da farko baki bude, can yace “Amma dai ni babu wanda ya gaya min, sati biyu kuma Anty, what’s d rush for, ni Wllh jiddar nan maganar gaskiya ta fitar min a kai, don Allah ni dai Anty….” Dafe kansa yyi yace “Ohh God, sati biyu fa ku ka ce?” Tabe baki Anty Maryam tayi ta juya ta bar masa dakin, zaunawa yyi gefen gado yana rike da kansa, can ya dago ya tashi ya fita, dakin Mami ya shiga ya sameta tana waya ya tsaya ya jira har ta gama sannan ya marairaice yace “Mami Anty Maryam ke ce min….” “Saura sati biyu bikin” Mami ta karasa masa tana masa wani kallo, tsaye yyi yana ta kallonta can ya juya ya fice a dakin, Mami ta fito ita ma ganin dakinsa ya koma ta fita compound, gun drivern gidan ta nufa, ya gaisheta da ladabi ta amsa masa tace “Musa, ina son ka min wani d’an aiki ne don Allah” with respect yace “Toh Hajiya aikin me xan yi” Tace “Ina son idan sudais ya fita gidan nan ka bi sa ka gano min ina xa shi, ko yanxu ko anjima ko da daddare” da mamaki yace “Barrister?” Tace “Shi” yace “Toh in sha Allah Hajiya” Har ta fara tafiya ta juya tace “And be very very careful you knw who you are dealing with”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button