Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Sorry if I disappoint anybody
Aliyu ya lumshe ido ya bude a hankali yace “Toh kar ki masa butulci Iman, baki san xai baki shi ba ya baki, prayer is all what ur little boy wants from you, kiyi masa addu’a ba kuka ba Iman, if you continue like this what will be the fate of his twin, kin ga shi ma xai shiga damuwa sosai na rashin halve dinsa and this might affect him badly…. Or did you want anything bad to happen to him also, For his sake plss ki kwantar da hankalin ki so you won’t loose him too, am telling you damuwar da shi xai shiga sai ma ya fi naki” khadijah ta kamo hannunsa cikin rawar murya tace “Na shiga uku don girman Allah kar ya bar ni shi ma” yace “Then ki kwantar da hankalin ki and accept this fate” hawaye na xuba idonta tace “Toh” yace “Promise me baxa ki sake kuka ba Iman” k’in cewa komai tayi, ya kira sunanta a hankali ta daga kai tana kallonsa, sosai gabanta ya fadi, ta kuma rushewa da kuka tace “Yanxu Sudais ya tafi ya bar ni…. Shi fa yace min in je in kira masa Shureim he wants to tell him he is sorry, dama mutuwa xai yi baya son ya mutu a kusa da ni” Ta hade kai da gwiwa tana kuka kamar ranta xai fita maganar Sudais na karshe na dawo mata “Anty ki ce Shureim ya xo, I want to tell him am sorry” kuka ta ke kamar ana dada tunxurata, Aliyu ya kasa ce mata komai duk jikinsa yyi sanyi, Ta rikosa tana girgixa kai cikin tashin hankali tace “Yanxu shkkn baxan sake ganin sa ba, me yasa ya tafi ya bar ni da Shureim” Aliyu ya kasa cewa komai wani mugun tausayinta na shigarsa, cikin sanyayyen muryarsa yace “Pls ki daina kukan nan Iman, da duk biyun Allah ya raba ki da ya xa ki yi kenan, you neva knew why he took him so soon, be a good Muslimat plss” shiru khadijah tayi jin yace Dukka biyun, ta goge idonta gabanta na mugun faduwa cos she can’t just imagine that, Murya can kasa yace “You make the promise now, that baxa ki sake masa kuka ba sai dai addu’a….” Ta gyada kai da kyar trying not to cry tace “I promise” yace “Add in sha Allah to the promise” a hankali tace “In sha Allah” Ya d’an yi murmushi yace “Good” mikewa yyi ya dago ta ta mike ita ma tana goge idonta yace “Ki wuce ciki and remember the promise you make” tace “Toh” daga haka ta fara tafiya ya bi ta da kallo, da sauri ta juyo sai kuma ta dawo tace “Ina shureim plss” da kamar baxai ce komai ba, sai kuma a hankali yace “Yana nan tare da mu” ta hadiye abu da kyar tace “Ka dauko min shi plss” yace “They are people everywhere, later xa a kai maki shi” shiru tayi sai kuma ta juya a sanyaye ta fara tafiya, Juyowa tayi ta kara dawowa idonta har ya fara kawo kwalla tace “Toh me yake yi?” Yace “Kukan xa ki fara kuma” da sauri ta girgixa kai tana goge idonta, yace “He is just sitting down” bata ce komai ba ta fara tafiya kamar iska xai kadeta ta fadi har ta bar wajen, Aliyu ya koma a sanyaye ya xauna ya jinginar da kansa jikin bango yana jin mutuwar yaron har cikin ransa, Tun da khadijah ta dawo compound din khaleel ke bin ta da kallo har ta shiga parlor, sai a sannan barrister Sudais ma ya dauke idanuwansa daga kallonta, Bedroom ta wuce duk mutanen parlon suka bi ta da kallo cike da tausayinta, Umma na xaune har lkcn duk jikinta yyi la”asar, da ido ta bi khadijah har ta dauko Hijab dinta ta sa ta xauna kan darduman dake shimfide ta jingina da bango, hawaye ya cika Idon Umma don bata yi xaton hakan ba, tashin hankalinta ta Inda xata fara lallashin Khadijah sai ga shi taga ta ma daina kukan, Wata frnd din umma ta dawo kusa da ita a sanyaye tace “Kiyi hakuri kinji Khadijah, Allah yayi masa rahama…” A hankali khadijah tace “Ameen” Umma taji hankalinta ya kwanta sosai, tashi tayi ta fita da kanta taje kitchen ta hado mata shayi ta dawo, kasa sha Khadijah tayi har lkcn ta kasa yarda Her lovely Sudais is gone forever, tana son kuka amma sai ta tuna promise din da tayi, hakan yasa xuciyarta ya dinga mata xafi sosai, kowa ya ganta sai yaji tausayinta, Umma har lkcn mamakin karfin halin nata ta dinga yi, a haka har aka yi la’asar, tana xaune kan darduma bayan ta idar da sllh umma ta xubo mata abinci ta xauna kusa da ita cike da lallami tace “Don Allah ko kadan ne ki ci Khadijah, tun jiya fa baki ci komai ba” Khadijah tayi shiru bata ce komai ba, can ta dago da kyar tana kallon Umma tace “Umma yanxu shikenan Sudais ya tafi” Rungume ta umma tayi tana kokarin ganin bata xubda hawayen dake baraxanar xubo mata ba, cikin sanyin murya tace “Pray for him daughter, Allah yasa can ya fi masa nan, Allah ya sa mai ceton mu ne” cikin rawar murya Khadijah tace “Ameen” umma tace “Toh ki ci abincin kadan don Allah” ta girgixa kai tace “Umma baxan iya ci ba” Umma tace “Ko cokali biyu ne ki yi” Nanny ce ta shigo dakin da kumburarrun idonta ta duka kusa da su tace “Umma akwai baki parlor sun xo mata gaisuwa ta daure ta fito” Umma tace “Kice su shigo nan” mikewa Nanny tayi ta fita ba a dau lkci ba ta dawo tare da su Mumy, Baby da su seeyama da wata daban, Mikewa Umma ta yi ganin su ta shimfida masu babban darduma tana masu sannu da xuwa, Khadijah ta dinga kallon Mumy har ta xauna, A hankali tace “Sannu da xuwa Mumy” mumy da kana ganin idanuwanta kasan ta yi kuka sosai tace “Sannu Khadijah, ya hakuri” Khadijah ta kasa amsawa ta dakar da kanta, Su siyama ma suka mata gaisuwar a sanyaye, sai a sannan khadijah ta kara dago kanta tana kokarin ganin bata bar hawayen idonta suka xubo ba, Kallon warce ke xaune kusa da baby ta dinga yi, ita ma yarinyar kallonta take da mamaki, Khadijah tayi karfin halin cewa “Maryam sannu da xuwa” Maryam tace “Ashe yaron ki ne ya rasu Khadijah, Allah ya ji kansa” Khadijah tayi karfin halin cewa “Ameen” sai dai xuciyarta cike yake da mamaki, Maryam dama yar uwar su Aliyu ce kenan, makarantar su daya a UK amma Hi kadai ne mutuncin da ke tsakaninsu kawai ta rasa me yasa bata son yarinyar, kawarsu Vanessa ce dai. Mumy sun kusa minti sha biyar a dakin, duk tausayin khadijah ya cika don tasan rashin yaro da ciwo sosai ga uwarsa barin yaro mai shiga rai irin sudais, bata ma samu courage din tambayar ina Shureim ba, Karfe biyar da yan mintuna tace ma umma xa su tafi, Umma tace “Toh mun gode kwarai Hajiya, Allah ya bar xumunci” Mumy tace “Ameen, kuyi hakuri bamu xo tun safe ba kanwata ce ba lafiya tana asibiti sun yi hatsari tun shekaranjiya” Umma tace “Subhanallah, toh Allah ya bata lafiya, ya yaye mata” Mumy tace “Ameen mun gode” hakuri ta kara ba khadijah Umma ta rakasu suka fita parlor, Sai a sannan Mumy tace “Kanin Aliyun yana waje ya xo mata gaisuwa amma ko xuwa anjima sai ya dawo” Umma tace “A’a bari ta fito” mumy tayi convincing dinta kan ta bari sai anjima ya dawo daga haka suka wuce Umma ta koma ciki. A hankali khadijah ta tako har cikin parlor tana sanye da Hijab dinta har kasa ta xauna kujera a sanyaye tana kallonsa, rasa abinda xai ce mata yyi, ta sunkuyar da kai a raunane tunawa da lkcn da suka dinga dragging sunan da ta xabar ma sudais dinta da shi, A hankali yace “Amira…” Ta daga kai tana kallonsa lkci daya idanuwanta suka kada, cikin sanyi yace “Keep on praying for him, Allah ya sa mai ceton mu ne, life moves on plss, ai da baki san Allah xai baki shi ba, so kiyi hakuri ki cire sa ranki, tsakanin ki da shi yanxu addu’a, baxai ji dadi kiyi ta masa kuka ba” Tana gyada masa kai da kyar tace “Ai na daina, Allah ya ji kansa, ya hada ni da shi a aljanna” Barrister sudais yace “Ameen, Allah ya kara maki hakuri” Murya can kasa tace “Ameen” yace “Toh yi ma Umma magana xan mata gaisuwa” Ta mike tace “Toh” daga haka ta wuce ciki, ba a dau lkci ba Umma ta fito, da ta amshi gaisuwar sudais tana sa masa albarka, Bai dade parlorn ba yace mata xai koma gida, tayi masa Allah ya kiyaye hanya ya fita parlorn, ita dai har ranta taji Sudais ya kwanta mata, ta kuma san har abada baxa ta mance hallacin da yayi mata ba, don ko ita yayi ma, bata kuma san da me xata saka masa ba. Karfe tara da yan mintuna, Aliyu ya shigo parlorn, har sannan Umma na ciki bayan ta sallami wasu bakin, suka gaisa ya kara mata gaisuwa tace “Allah ya ba mu hakuri gaba daya, daxu su hajiya ma suka xo, mun gode kwarai” shi dai bai ce komai ba, Umma sai ta ga kamar sudais ne xaune gabanta ya girma, hakan yasa duk jikinta ya kara sanyi, Aliyu da ya rasa abinda xai ce yyi karfin hali daga karshe yace “Mama tana Ciki ne?” Umma tace “Ehh tana ciki bari in mata magana” Daga haka ta mike ta wuce ciki, bayan wani lkci ta dawo tana kallonsa tace “Aliyu tayi bacci kuwa” yace “Toh shkkn Mama, sai na dawo gobe Allah kara hakuri” tace “Ameen, Allah bada lada” tana son tambayarsa Shureim amma bata san ta ya ba, ta kasa daurewa daga karshe kafin ya fita tace “Aliyu ina shureim din fa?” Juyowa yyi yace “An tafi da shi mama” tace “Can gidan ku?” Ya girgixa mata kai, Umma tace “Toh shikenan Allah ya kiyaye hanya” daga haka ya fita, umma ta san khaleel ne ya tafi da shi can gidan nasu. Ta koma cikin dakin Khadijah ta rufa mata bargo, Nanny dake dakin tace “Umma da ki kwana nan, tunda akwai baki dakin ki” Umma tace “A’a ke ki tsaya tare da ita babu komai duk daya ne” daga haka ta fita dakin.